Sashe 80
Yar Garuwa Part 1 Complete Hausa Novel · about 7 min read
"Ni ce fa MA'U KHUBRA...Dana kawo ki aikatau,wanda tun bayan wanni biyar dana kawoki ban sake waiwayoki b..."
Ido KHUBRA ta zare tana kallonta da mamaki shimfid'e kan fuskarta na yadda ta kasa game kammaninta,ko tantama babu d'ayar kam LADIYO ce dan kamarsu d'aya su biyun fun can da.
Daga nan MA'U ta kwashe komai daya faru tun bayan data bar gidan,yadda tayi mata asiri kuma cikin hukuncin Allah kasancewar bata da hak'k'i Allah ya kareta,sannan ta d'ora da yadda asirin yayi tasiri akanta ita,maza suka dinga binta itama tana binsu kamar dai yadda igiyar ruwa ke kad'awa gefe zuwa gefe,kaf ta kwashe komai har ciwon da take d'auke da shi a halin yanzun,wanda tun bayyanar cutar a jikinta ta koma gidanta,kuma har lokacin bata bar halinta na biye-biyen maza ba,a haka ne wata rana suna tsaka da aikata masha'arsu a soron gidan nata kawai sai ga wata mak'ociyarsu nan ta shigo da niyyar tambayarta kasancewarta bak'uwa a unguwar,ganin da tayi musu mak'ale da juna yasa ta fasa k'ara dalili kenan daya sa mutanen unguwa taruwa kasancewar da yamma ne kuma ranar babu aiki,da yake an san ba aure gareta ba nan ko aka shiga jibgarsu babu ji bare gani ta k'arasa da fad'in
"Da kyar na samu na gudu,daga nan ban zame ko ina ba sai nayi tasha na tafi garin KASHIN DILA gurin YAYA,a lokacin dana je na sameta cikin mawuyacin hali wanda ko abincin da zata cima gagararta yake,babu gurin kwana babu suturar kirki har sai tayi bara take samun d'an abun da zata sawa cikinta,a k'ofar gida cikin rumfa na isketa gidan kuma a kulle,ko dana tambayeta sai take shaidamin cewa MALAM BUBA ya sake ta,kuma gidanma ya sallama shi ga mai gari tare da sauran kadarorin da iyayensa suka bar masa,yayi kuma sallama da mutanen garin da sunan bazai sake dawowaba.Sannan ta sanarmin da KHUBRA kin koma tare da wasu mutane da suka shaidawa MALAM BUBA a hannunsu kike kuma dai da alamun suna da alak'a tsakanin su da shi MALAM en Lamar yadda muka samu labari yanzun,to bayan nan kuma muka ci gaba da zama a garin wahalar da muke ciki tasa muka baro can muka dawo nan gidan dana zauna a nan kano,bayan mun dawo nan mun d'auki lokaci muna zuwa wannan unguwar muna neman gidan dana kawo ki aiki,sai dai Allah bai nufa zan gane gidanba sai yau da muka shigo muna neman taimakon abunda zamu ci saboda duk wata dukiya da nake da ita ta k'are yanzun,sai Allah yasa muka ga matar dana kawoki hannunta.Shi ne ta shaida mana kinyi aure tun shekaru biyu da aula wuce,min nemi son ganinki ne a gurinta shine race my jira zata kira mijinki ya kawo mata ke.
Kunji abunda ya faru tun daga rabuwarmu har kawo yanzun ...
Parlour'n kowa yayi shiru mamaki game da d'umbin al'ajabi na hali irin na wad'annan mutane da suke zaune duk ya d'aure musu kai,KHUBRA kam zuwa lokacin hawaye sun gama wanke mata fuska banda godiya ga Allah daya kareta ya kuma tsareta daga fad'awa tarko ba tare da an samu damar keta mata mutuncin taba take yi,mik'ewa BB yayi ya kamata suka bar gurin duk maganar da suke yi na ta yafe musu kan cutar da ita da suka yi,bai bari ta tsaya gurinba dan shima da kansa haushinsu yake ji,kuma yayi niyyar d'aukar mataki a kansu sai dai ya tuna wata magana da suka tab'ayi da yake ce mata sai ya d'auki mataki kansu,amsar data bashi a lokacin itace ta sake dawo masa,dalili kenan daya sashi janyeta a gurin coz yana son rarrashinta...
'Dakinsa na da ya shige da ita,d'akin ta kalla da hawaye har lokacin a cikin idonta,yana nan kamar yadda yake da,key ya murzawa k'ofan danma kada wani ya samu damar shigowa,janyota yayi ta shige cikin jikinsa,yana d'an jijjigata har ya samu tayi shiru sai ajiyar zuciya da take,bakin bed ya zauna ya d'orata akan cinyansa yana goge mata fuska,cikin kunnenta yake hura mata iska har sai da ta koma hayyacinta,mik'ar da ita ya sake yi tsaye tayi tunanin fita za suyi,da sauri ta rik'e shi tana sake sakin sabon kuka
"JAAN please kada ka mai dani gurinsu dan Allah baran iya zama guri d'aya da suba...kaji..?"
"Ok ok..! yi shiru babu inda zamu tunda baki so kinji ko..Zo nan na cire miki rigan kisha iska.."
Matsawa tayi jikinsa,sunkuyawa yayi a gabanta ya shiga bud'e mab'allan rigan jikinta,singlet ne a jikinta ta ciki sai nicker's,rungumeta yayi ya nufi saman bed da ita,kanta ya d'ora kan cinyansa ita kuma ta kwanta a gefenta na dama fuskarta na kallon fuskarsa,sai ajiyan zuciya take saukewa,gashinta ya shiga shafawa yana mata magan-ganu masu dad'i da kwantar da hankali,saboda kasancewarta mai d'auke da juna biyu daya tasamma tsufa ba'a son kasancewarta cikin b'acin rai,kafin wani lokaci sai gata ta ware har suna wasanni cike da nishad'i..
Can ko a parlour bayan barin su gurin MA'U da LADIYO sake b'arkewa suka yi da kuka ganin KHUBRA ta bar gurin ba tare da ta yafe musuba,kan irin cutarwar da suka mata,kuka suke suna k'arawa akan a kirata su nemi gafararta,shiru mutanen dake parlour en su kayi sai sauraren su suke sai da suka yi kukan son ransu wannan suka yi shiru, suna kuma dad's tonawa Kansu aspirin abubuwan da suka yita aikatawa Wanda aka sani dama Wanda ba a saniba,cike da tausyawa halin da suka jefa KHUBRA a ciki da mahaifiyarta data jima da rasuwa saboda girman kaidi da suka dinga shiryawa mutanen cikin parlour en ke kallonsu,da kyar UMMI ta bud'e baki tayi magana wanda yasa kowa ya maida kallonsa kanta,hatta kuwa da su masu koke-koken neman gafara,kiran KHUBRA da BB tasa ayi don kawo k'arshen komai,ko da d'an aike KHALEEL yaje ya tarar da k'ofa a kulle baiyi knocking ba ya dawo dan shima akan dole yaje saboda dai kawai bazai iya cewa UMMI a'a bane yasa yaje,sanar mata yayi da k'ofar a kulle take,sashi tayi ya koma yayi knocking ai ko kamar yadda ta umarta haka yayi,bud'ewa BB yayi sukayi ido hud'u da KHALEEL a nan ya coge ya kare k'ofar ba tare daya bawa KHALEEL damar gano cikin d'akinba ya furta
"Ya akayi ne...?"
"UMMI tana kiranku yanzun..."
Badon yaso ba ya koma ciki yana b'ata rai,shi kam babu yadda za ayima ya tasheta tana bacci,saboda haka ya fice had'e da kulle k'ofar,ganinsa shi kad'ai yasa suka kalle shi UMMI tana tambayan KHUBRA
"UMMI tayi bacci ne..."
Amsa daya bata kenan fuska a murtuke,aikuwa MA'U ta hau sheshshek'ar kuka,BB wani kallo ya jefeta dashi daya sata shiga nutsuwarta tana sunkuyar da kai k'asa,babu yadda basu yiba akan a tasota ta yafe musu,shi kuma ya kafe akan wallahi babu abunda zaisa ya tasheta,kawai suje an yafe musu saboda ubangiji yana son masu yafiya kuma itama zata yafe musu in sha Allah su tafi kawai,k'in tafiya suka yi ganin sun matsa kan sai sun nema yafiyarta su da ita kuwa yace musu idan suka takura to wallahi zai janye yafiyar da aka musu.
Babu b'ata lokaci suka fice suna kuka had'e da waiwayen gidan dan sun san shi kenan kuma suda sake ganin KHUBRA bare kuma MALAM BUBA daya koma AL-HAJI ABUBAKAR,wanda yake ji da dukiya a yanzun,ta inda cikin shekaru biyu da watanni ya bawa wasu miliyoyi baya.
*WAIWAYE....*
Tun bayan lokacin da MALAM BUBA ya kori LADIYO daga cikin gidansa,yayi sallama da mutanen garin,nan ya saida duka wata kadara daya mallaka ya tattaro kan dukiyarsa,wacce a k'arshe bayan dawowarsa ya damk'ata a hannun ALHAJI SAFWAN,inda shi kuma ya kawo shawara suka had'a kai su uku suka sake bud'e wani company da yanzun yake k'ark'ashin jagorancin KHALEED da KHALEEL.
_Wannan kenan....._
Bayan tafiyarsu aka koma maida labarin yadda al'amura suka faru a baya,kowa sai jimami yake kan yadda abubuwan suka faru.Bayan komai ya lafa su ABBA suka koma bakin aikinsu a d'ayan company ensu.
Su kuma sauran yaran aka barsu nan suna ci gaba da hiran haihuwan KHUBRA nan da wani watan suna kuma ci gaba da tsara irin shagulgulan da zasu yi idan ta haihun............
*ONE MONTH LEAP...*
Ido KHUBRA ta zare tana kallonta da mamaki shimfid'e kan fuskarta na yadda ta kasa game kammaninta,ko tantama babu d'ayar kam LADIYO ce dan kamarsu d'aya su biyun fun can da.
Daga nan MA'U ta kwashe komai daya faru tun bayan data bar gidan,yadda tayi mata asiri kuma cikin hukuncin Allah kasancewar bata da hak'k'i Allah ya kareta,sannan ta d'ora da yadda asirin yayi tasiri akanta ita,maza suka dinga binta itama tana binsu kamar dai yadda igiyar ruwa ke kad'awa gefe zuwa gefe,kaf ta kwashe komai har ciwon da take d'auke da shi a halin yanzun,wanda tun bayyanar cutar a jikinta ta koma gidanta,kuma har lokacin bata bar halinta na biye-biyen maza ba,a haka ne wata rana suna tsaka da aikata masha'arsu a soron gidan nata kawai sai ga wata mak'ociyarsu nan ta shigo da niyyar tambayarta kasancewarta bak'uwa a unguwar,ganin da tayi musu mak'ale da juna yasa ta fasa k'ara dalili kenan daya sa mutanen unguwa taruwa kasancewar da yamma ne kuma ranar babu aiki,da yake an san ba aure gareta ba nan ko aka shiga jibgarsu babu ji bare gani ta k'arasa da fad'in
"Da kyar na samu na gudu,daga nan ban zame ko ina ba sai nayi tasha na tafi garin KASHIN DILA gurin YAYA,a lokacin dana je na sameta cikin mawuyacin hali wanda ko abincin da zata cima gagararta yake,babu gurin kwana babu suturar kirki har sai tayi bara take samun d'an abun da zata sawa cikinta,a k'ofar gida cikin rumfa na isketa gidan kuma a kulle,ko dana tambayeta sai take shaidamin cewa MALAM BUBA ya sake ta,kuma gidanma ya sallama shi ga mai gari tare da sauran kadarorin da iyayensa suka bar masa,yayi kuma sallama da mutanen garin da sunan bazai sake dawowaba.Sannan ta sanarmin da KHUBRA kin koma tare da wasu mutane da suka shaidawa MALAM BUBA a hannunsu kike kuma dai da alamun suna da alak'a tsakanin su da shi MALAM en Lamar yadda muka samu labari yanzun,to bayan nan kuma muka ci gaba da zama a garin wahalar da muke ciki tasa muka baro can muka dawo nan gidan dana zauna a nan kano,bayan mun dawo nan mun d'auki lokaci muna zuwa wannan unguwar muna neman gidan dana kawo ki aiki,sai dai Allah bai nufa zan gane gidanba sai yau da muka shigo muna neman taimakon abunda zamu ci saboda duk wata dukiya da nake da ita ta k'are yanzun,sai Allah yasa muka ga matar dana kawoki hannunta.Shi ne ta shaida mana kinyi aure tun shekaru biyu da aula wuce,min nemi son ganinki ne a gurinta shine race my jira zata kira mijinki ya kawo mata ke.
Kunji abunda ya faru tun daga rabuwarmu har kawo yanzun ...
Parlour'n kowa yayi shiru mamaki game da d'umbin al'ajabi na hali irin na wad'annan mutane da suke zaune duk ya d'aure musu kai,KHUBRA kam zuwa lokacin hawaye sun gama wanke mata fuska banda godiya ga Allah daya kareta ya kuma tsareta daga fad'awa tarko ba tare da an samu damar keta mata mutuncin taba take yi,mik'ewa BB yayi ya kamata suka bar gurin duk maganar da suke yi na ta yafe musu kan cutar da ita da suka yi,bai bari ta tsaya gurinba dan shima da kansa haushinsu yake ji,kuma yayi niyyar d'aukar mataki a kansu sai dai ya tuna wata magana da suka tab'ayi da yake ce mata sai ya d'auki mataki kansu,amsar data bashi a lokacin itace ta sake dawo masa,dalili kenan daya sashi janyeta a gurin coz yana son rarrashinta...
'Dakinsa na da ya shige da ita,d'akin ta kalla da hawaye har lokacin a cikin idonta,yana nan kamar yadda yake da,key ya murzawa k'ofan danma kada wani ya samu damar shigowa,janyota yayi ta shige cikin jikinsa,yana d'an jijjigata har ya samu tayi shiru sai ajiyar zuciya da take,bakin bed ya zauna ya d'orata akan cinyansa yana goge mata fuska,cikin kunnenta yake hura mata iska har sai da ta koma hayyacinta,mik'ar da ita ya sake yi tsaye tayi tunanin fita za suyi,da sauri ta rik'e shi tana sake sakin sabon kuka
"JAAN please kada ka mai dani gurinsu dan Allah baran iya zama guri d'aya da suba...kaji..?"
"Ok ok..! yi shiru babu inda zamu tunda baki so kinji ko..Zo nan na cire miki rigan kisha iska.."
Matsawa tayi jikinsa,sunkuyawa yayi a gabanta ya shiga bud'e mab'allan rigan jikinta,singlet ne a jikinta ta ciki sai nicker's,rungumeta yayi ya nufi saman bed da ita,kanta ya d'ora kan cinyansa ita kuma ta kwanta a gefenta na dama fuskarta na kallon fuskarsa,sai ajiyan zuciya take saukewa,gashinta ya shiga shafawa yana mata magan-ganu masu dad'i da kwantar da hankali,saboda kasancewarta mai d'auke da juna biyu daya tasamma tsufa ba'a son kasancewarta cikin b'acin rai,kafin wani lokaci sai gata ta ware har suna wasanni cike da nishad'i..
Can ko a parlour bayan barin su gurin MA'U da LADIYO sake b'arkewa suka yi da kuka ganin KHUBRA ta bar gurin ba tare da ta yafe musuba,kan irin cutarwar da suka mata,kuka suke suna k'arawa akan a kirata su nemi gafararta,shiru mutanen dake parlour en su kayi sai sauraren su suke sai da suka yi kukan son ransu wannan suka yi shiru, suna kuma dad's tonawa Kansu aspirin abubuwan da suka yita aikatawa Wanda aka sani dama Wanda ba a saniba,cike da tausyawa halin da suka jefa KHUBRA a ciki da mahaifiyarta data jima da rasuwa saboda girman kaidi da suka dinga shiryawa mutanen cikin parlour en ke kallonsu,da kyar UMMI ta bud'e baki tayi magana wanda yasa kowa ya maida kallonsa kanta,hatta kuwa da su masu koke-koken neman gafara,kiran KHUBRA da BB tasa ayi don kawo k'arshen komai,ko da d'an aike KHALEEL yaje ya tarar da k'ofa a kulle baiyi knocking ba ya dawo dan shima akan dole yaje saboda dai kawai bazai iya cewa UMMI a'a bane yasa yaje,sanar mata yayi da k'ofar a kulle take,sashi tayi ya koma yayi knocking ai ko kamar yadda ta umarta haka yayi,bud'ewa BB yayi sukayi ido hud'u da KHALEEL a nan ya coge ya kare k'ofar ba tare daya bawa KHALEEL damar gano cikin d'akinba ya furta
"Ya akayi ne...?"
"UMMI tana kiranku yanzun..."
Badon yaso ba ya koma ciki yana b'ata rai,shi kam babu yadda za ayima ya tasheta tana bacci,saboda haka ya fice had'e da kulle k'ofar,ganinsa shi kad'ai yasa suka kalle shi UMMI tana tambayan KHUBRA
"UMMI tayi bacci ne..."
Amsa daya bata kenan fuska a murtuke,aikuwa MA'U ta hau sheshshek'ar kuka,BB wani kallo ya jefeta dashi daya sata shiga nutsuwarta tana sunkuyar da kai k'asa,babu yadda basu yiba akan a tasota ta yafe musu,shi kuma ya kafe akan wallahi babu abunda zaisa ya tasheta,kawai suje an yafe musu saboda ubangiji yana son masu yafiya kuma itama zata yafe musu in sha Allah su tafi kawai,k'in tafiya suka yi ganin sun matsa kan sai sun nema yafiyarta su da ita kuwa yace musu idan suka takura to wallahi zai janye yafiyar da aka musu.
Babu b'ata lokaci suka fice suna kuka had'e da waiwayen gidan dan sun san shi kenan kuma suda sake ganin KHUBRA bare kuma MALAM BUBA daya koma AL-HAJI ABUBAKAR,wanda yake ji da dukiya a yanzun,ta inda cikin shekaru biyu da watanni ya bawa wasu miliyoyi baya.
*WAIWAYE....*
Tun bayan lokacin da MALAM BUBA ya kori LADIYO daga cikin gidansa,yayi sallama da mutanen garin,nan ya saida duka wata kadara daya mallaka ya tattaro kan dukiyarsa,wacce a k'arshe bayan dawowarsa ya damk'ata a hannun ALHAJI SAFWAN,inda shi kuma ya kawo shawara suka had'a kai su uku suka sake bud'e wani company da yanzun yake k'ark'ashin jagorancin KHALEED da KHALEEL.
_Wannan kenan....._
Bayan tafiyarsu aka koma maida labarin yadda al'amura suka faru a baya,kowa sai jimami yake kan yadda abubuwan suka faru.Bayan komai ya lafa su ABBA suka koma bakin aikinsu a d'ayan company ensu.
Su kuma sauran yaran aka barsu nan suna ci gaba da hiran haihuwan KHUBRA nan da wani watan suna kuma ci gaba da tsara irin shagulgulan da zasu yi idan ta haihun............
*ONE MONTH LEAP...*