← Book details Yar Garuwa Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 73 OF 86

Sashe 73

Yar Garuwa Part 1 Complete Hausa Novel · about 7 min read

"Babu komaifa..."
Ta sake bashi amsa kuma har lokacin bata saki fuskar ba,juyo da ita yayi fuskarsu na kallon juna ta yanda suke iya jin numfashin junansu na sauka kan fuskokinsu
"JODI nine baza ki iya rakowa ba sai an ce ki rakani...?"
Kai ta girgiza idanunta a k'asa
"Me yasa to kika b'ata fuskanki dan ance ki rakoni...? ko dan bakya so ne shi yasa..?"
Nanma girgiza masa kai ta sakeyi
"To mene ne..?"
Shiru tayi shima shirun yayi ya jingina bayansa a jikin kujeran kallonta yaci gaba dayi,ba tare da ya mata maganaba,itama taci gaba da zama kanta a k'asa ta kasa magana.
Sun jima zaune babu wanda yayiwa wani magana,shi kuma BB zuba mata ido yayi yaga iya gudun ruwanta,gajiya yayi da shirun ya fara magana fuska babu wani wadataccen fara'a
"Wato baki san kinyi laifiba ko...?"

Idanunta ne sukayi rau-rau za tayi kuka,kansa ya d'auke daga kallon da yake mata cikin muryar kuka ta furta
"Kayi hak'uri YAYANAH dan Allah.."
Dai² lokacin hawayen suka sakko kan fuskarta,kasa jurewa yayi da sauri ya furta
"It's ok...!"
Yana janta jikinsa yana patting bayanta,ajiyan zuciya ta sauke tana dad'a kwanciya jikinsa,sai daya tabbatar ya sanyata dariya sannan ya mata sallama akan sai anjiman idan ya dawo zasu tafi,cike da farin ciki ta juya suna waving wa junansu.

Har dare tana gidan kowa sai nan-nan yake da ita musamman MAMA da FATAHIYYA,a nan su ABBA suka tarar da ita lokacin da suka dawo,sosai sunyi farin cikin ganinsu hankalinsu a kwance.
A wannan lokacin ba kowa ne zai kalli ABBA'N KHUBRA ya shaida shiba,ashe dama wahala da zaman k'auye sukasa ya fara tsofewa,cikin y'an watanni har ya soma yin shar da shi,da yake Allah yayi shi mai tsafta shi yasa cikin lokaci kad'an ya dad'a gogewa musamman kuma daya had'u dasu ABBA mutanen da suka yi gogayya da turawa,yadda suke tafiyar da harkokin kasuwancinsu yanzun idan ba wanda ya san suba ba zai tab'a tunanin ba jini d'aya bane su en,dan mutane da dama suna musu kallon y'an uwan juna.
Daf da zasu tafi KHUBRA ta matsa kusa da ABBA'NTA tana masa magana,cike da sha'awar ganin yadda y'ar tasa ta koma ya kalleta yana maida hankalinsa kanta dan ya fuskanci me zata fad'a,kamar abun arziki suka dad'a gaisawa yana tsokanarta,sai dariya take shi kuma hakan shi yasa shi yake sake jin dad'i sosai
"ABBA dama fa akwai maganar da nake ta son maka.."
Kallonta ya sake yi yana fad'in
"To y'ar albarka ina sauraronki"
Sai da tayi ajiyan zuciya sannan kuma kanta a k'asa tace
"ABBA dama ba kan komai bane sai wani al'amari da nake ganin idan hakan ya kasance kowa zaiyi farin ciki..."

Dad'a d'aure masa kai tayi saboda har lokacin bata fad'i abunda zata fad'a enba,muryarta ta katse shi daga sonyin magana
"ABBA damafa shawara ne nazo da shi,nace me zai hana ka yarda da BABA ZUWAIRA a matsayin mata,kaga itama dama bata da aure mijinta ya jima da rasuwa,kuma ABBA na baku labarin yadda ta rik'eni na tabbata bata da wata matsala...Kuma kaima yanzun ABBA baka da kowa sai ni kad'ai..."
Dakatar da ita yayi fuska a had'e yake fad'in
"Maganar dama da kika zo da ita kenan saboda futsara irintaku ta y'ay'an zamani har ni kikewa maganar nayi aure...?"
Yadda taga ya b'ata rai ya kuma zage yana ta mata fad'a yasa ta shiga bashi hak'uri,amma kam bata ji dad'iba daya k'i amincewa,haka sukayi sallama da mutanen gidan da suka rakosu har bakin mota kafin suyi musu sallama suka d'auki hanya.

Cikin motan shiru babu mai magana kanta a k'asa tana matse hawayen dake sauka kan fuskarta,maganar BB ya dakatar da kukan nata
"Me kika yiwa ABBA yayi miki fad'a....kin b'ata masa rai ko...?"

Sai da ta gama kukanta ba tare data kula shiba,shi kuma sai nasiha yake mata yana nusar sa ita hanyar da zatabi su zauna lafiya da ABBA,sai da ta bari sunje gida har sunyi wanka sun kwanta sannan ta bashi labarin abunda ya had'asu,ajiyar zuciya yayi kafin ya nuna mata illar abunda tayi,sai yanzun ta fahimci laifinta dan kam tabbas ba ita ya kamata tayi masa maganar ba.Tun daga lokacin ta k'udurce a ranta duk hanyan da zata bi sai ta bi na ganin hak'anta ya cimma ruwa kuma zata dage da addu'ah akan Allah ya tabbatar da alkhairinsa................
_Wannan kenan.._

*COMMENT FOR MORE PAGE'S..........* 💃💃💃💃💃

*~#TEAM KHUBRA-KHALEED.~*

*_®єαl $mαѕhєr._* 😉
💠💠💠💠💠

*Y'AR GARUWA......*
*(ɬɧɛ mơʂɬ ɧɛąrɬ ɬơųcɧıŋɠ ʂɬơrყ).*

🕊🕊🕊🕊
🌹🌹🌹

*fαcєвσσk grσup:* https://www.facebook.com/groups/369678263526212/
SMASHER,HUBBEEY,DIDEEYLOV & GENTLE NOVEL'S [email protected]

*©®2018*
*6/ɑմցմՏԵ,2018*

*ʂɬơrყ ąŋɖ wrıɬɛɛŋ*
*ცყ*
_HAWWA M.U {$мaѕнer}_
🕊🕊🕊🕊🕊
🌹🌹🌹🌹

_BISMILLAHIR-RAHMANIR-RAHEEM..._
*~___________________________~*
_cwєєt ѕíѕ *HALIMATUS-SADIYA MUHAMMAD (LEEMA)* ínα tαчαkí murnα dα fαrín cíkí nα gαmα wαnnαn nσvєl mαí cíkє dα d'umвín dαruѕѕα nα *IYA KU'DINKA* αllαh чα ѕα ѕαk'σnkí чα íѕα índα kíkє вuk'αtα αllαh чαѕα mutαnє ѕuчí αmfαní dα d'umвín вαѕírαrkí dα kíkα zuвє α cíkí dα ílímí dαkє cíkín lαвαrín..uвαngíjí чα k'αrα lαfíчα dα níѕαn kwαnα mαí αmfαní._ *#1 ♥ cwєєt lєєmαtєєч.* 😍
*~___________________________~*

*DEVOTED TO:*
_BILKISU M.ADAM (Y'AR ABBA)_

*BESTOWED TO:*
_MURJA SALIS (NA'IKKE)._

*AND*

_FATIMA ABUBAKAR (FATEEY AFIRST)._

6⃣0⃣

*K* imanin kwanaki biyu kenan da zuwansu gida,yauma yana zaune cikin parlour a lokacin KHUBRA na saman jikinsa kamar kowane lokaci da idan kaje zaka tarar dasu a hakan.Cike da so da kulawa ya kalleta yana fad'in
"JODI yanzun idan aka ce kizo a kaiki makaranta shin kina so ko kuwa...?"
Kallonsa tayi tana murmushi ba tare data ce komaiba,saima hannunta datake ci gaba da wasa da shi a jikinsa,ganin bata da niyyan magana yasa ya rik'e hannunta yana kuma kallon ta,a hankali ta d'aga kanta ta kalleshi tana murmushi
"Shi ne kina ji ina miki magana bara ki amsaba...? kin san dai bana son haka ko...?"
K'ure shi tayi da ido tana nazarin fuskarsa,ganin yanda yayi yasa ta d'an gyara kwanciyanta tana fad'in
"Ni kam YAYANAH wani karatu ne zanyi yanzun...? ina ganin bani da wannan daman dan kam lokacina ya riga da ya wuce,wanda nake da shima na addini ya isarmin,amma kam nayi girma da zuwa makaranta yanzun.."
Shiru yayi yana nazarin maganarta,lallaima yarinyar nan idan ba shirme irin nata ba,har wane girma ne za ace tayi yanzun da karatun,shi kam tabbas yana da burin ganinta tayi karatu,shirun da taji yayi babu magana yasa ta sake d'agowa tana fad'in
"YAYANAH waima me ya kawo wannan maganar ne kam yanzun...?"

Idanunsu sark'e cikin na juna yake fad'in
"Wato kefa a ganinki nan kinyi girma da zuwa makaranta ko...?"
Kai ta d'aga masa alamar eh,kuma har cikin zuciyarta take nufin hakan,d'an murmushi tayi kafin ta furta
"To waima YAYANAH kawai sai na wani tafi na zauna haka nan gemai-gemai dani nace naje koyan karatu ko me..?"
Da sauri ya katseta ta hanyar fad'in
"Haba hajiya bafa wani girman da kikayi da karatu kuma da kike wannan maganar ma SHEHU JAHA ma cewa yayi acikin labarinsa *"GEMU BAYA HANA ILIMI"* sannan kinga kuma yanzun baki san wane irin y'ay'a Allah zai azurtamu da suba,shin bakya sha'awar ace kin bada naki gudunmawar ta b'angaren ginuwar iliminsu...?"
Shiru ta sake yi tana nazarin maganarsa,ita kad'ai a zuciyarta take fad'in
"Gaskiya dai kuma da haka,ko ba komai zanyi alfahari da kasancewar hakan idan har ya faru,to amma abun tambayan shin zan iya kuwa....?"
Tambayan daya tsaya mata a rai kenan,ta kasa samun wani ya bata amsa,ganin jikinta yayi sanyi da maganar kuma da yiwuwar ya canja mata ra'ayi yasa baiyi k'asa a guiwa ba ya shiga kwad'aitar da ita amfanin karatun,wanda a k'arshe ya samu nasaran amincewarta,dan BB cewa yayi bazai mata doleba idan har ta nuna bata so zai bita a sannu har saita amince,saboda a nasa tunanin cewa yayi
_"Duk abunda wani yake so wani yayi,idan har wanda ake so yayin ba shida sha'awar hakan to tabbas baza a samu nasara ba amma idan yana so nan ne zaka ga ya dage dan ganin ya aikata wannan abun kuma burinsa zaka tarar bai wuce na ganin yayi nasara ba"_
Murmushin samun nasara yayi yana shafa lallausan gashinta dake kwance yasha gyara
"Uhmmm! JODI kenan wato kenan fa wai gani kike kin girma ko...?"

"Haba mana YAYA kaimafa kasan na girma ai yanzun ai wani abun da zanyi shi da a yanzun kam ko da kud'i banyinsa,bare kuma da hankalina ai baranma soma aikatawa ba"

"Gaskiya kam amma ni banga wani girman da kika yiba har yanzun"
Mik'ewa tayi a jikinsa ta tsaya tana juya jikinta cikin salo tace
"Haba YAYANAH kallenifa kaga yanda na koma hakama ai wani cewa zaiyi na zama uwar mata.."
Dariya kalamanta suka sashi,sai dai kawai ya gintse yana kallonta yana murmushi,janyota yayi yana maidata muhallinta data tashi
"Lallai kam babynah ta girma,amma wannan girman ai daban wanda nake nufi daban"

"To wanne kake nufi kai...? ni dai nasan na girma yanzun"
Chapter 73 · 0% Book details