Sashe 37
Yar Garuwa Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
"Haba KHUBRA me kuma ya kaiki kwanciya da wannan al'murun ke dama da ba lafiyaba ai sai ki jaa jikin naki ya dad'a yin zafi"
Shigowar BABA ZUWAIRA kenan gidan ta tarar da KHUBRA kwance tsakar gida saman tabarmar kaba....
'Dan d'ago da kanta tayi kad'an ta kalli BABA sannan ta sake maida kanta ta kwantar saman hannunta da tayi matashi da shi.
"Sannu da dawowa BABA"
"Yawwa y'ar nan,kinga na ce zan aiko miki da magani shiru gashi da gani jikin naki ke damunki...
Yau kam ISAH bai fito da wuriba shima sai yanzu da zan taho na biya naganshi...
Shi ne yake shaidamin gona yaje dubawa,Allah dai ya taimaka na samo miki maganin,yi maza ki tashi ki sha kinji idan aka jima an yi sallar ishaa sai ki kwanta kinji ko,Allah dai ya baki lafiya"
Duk maganar nan da BABA ZUWAIRA ke yi hankalin KHUBRA ba a kanta yake ba,tunani ne iri² duk zuciyarta ta cunkushe,jinta take a wannan lokacin tana so tayi kuka ko zata samu sauk'in rad'ad'in dake damunta a zuciyarta,a cikin kwanakin nan tana yawan yin mugayen mafarkai da wani mutum da har zuwa yanzun ta kasa tantance waye ne,sai dai duk lokacin da zata ganshi cikin muguwar damuwa take ganinsa wannan dalilin da yasa mafarkin ya tsaya mata a rai,yawan mafarkin da take da shi yasa ta shiga damuwa da ta haddasa mata ciwon jikin da take fama da shi cikin satin....
Sai da BABA ZUWAIRA ta tab'ata sannan ta tashi ta zauna had'e da karb'ar maganin tana juyashi a hannunta...
Da kyar ta samu tasha maganin sannan ta tashi da nufi yin sallah....
Tun misalin k'arfe 8:30pm tayiwa BABA ZUWAIRA salamma ta shige d'aki,ita ko BABA'N a lokacin tunaninta duk jikin ke damunta,ta dai bita da fatan samun sauk'i fuskarta duk alamun damuwa da halin da y'ar tata ke ciki...
Ko da ta shiga d'akin bayan ta kwanta nan ta shak'i kukanta har ta godewa Allah...
Sai bayan ta gama kukan ta tsaya tunanin menema wai yasata kuka haka?
Tana wannan tunanin bacci ya d'auketa cike da mafarkai iri-iri....
《《》》
Gari na wayewa suka hau shirin barin garin,misalin k'arfe 10:00am suka yiwa UMMI sallama suka mik'i hanya bayan d'umbin nasiha da suka sha a gurinta sannan ta musu fatan dawowa lafiya...
Sai da suka biya suka ga jikin MAMA,sai daifa har zuwa wannan lokacin MAMA bata sanma wanda yake kanta ba,bare ta samu damar yin magana.....
Daga nan suka d'auki hanya sai garin na JIGAWA DUTSE......
乛乛乛乛乛
Safe trip BB and KHALEEL.....
*~TEAM KHUBRA.~*
*_REAL SMASHER._*
💠
*Y'AR GARUWA......*
*(ɬɧɛ mơʂɬ ɧɛąrɬ ɬơųcɧıŋɠ ʂɬơrყ).*
🕊🕊🕊🕊
🌹🌹🌹
*©®2018*
*1/ʝųlყ,2018*
*ʂɬơrყ ąŋɖ wrıɬɛɛŋ*
*ცყ*
_HAWWA M.U {$мaѕнer}_
🕊🕊🕊🕊🕊
🌹🌹🌹🌹
_BISMILLAHIR-RAHMANIR-RAHEEM..._
*~________________________~*
_Matso maza kuji mutanen arziki,wollah a duk inda kuke ina k'aunarku irin wacce bazata fad'uba kuma ina alfahari daku_
*MISS ABATCHA,ZAINAB (ZEE MA'DAGWAS & KHADIJA (FRESH KHADEEY)*
_Kuyi komai ba komai mutanena Allah ya bar k'auna....*ME LUV U* ❤ irin tottaly ennan..._
*~__________________________~*
*DEVOTED TO:*
_BILKISU M.ADAM (Y'AR ABBA)_
*BESTOWED TO:*
_MURJA SALIS (NA'IKKE)._
*AND*
_FATIMA ABUBAKAR (FATEEY AFIRST)._
*3⃣8⃣*
*T* afiya ta mik'a a b'angarensu BB,inda babu wanda ke wata magana hakan ne yasa tafiyan nasu ya zama kamar na kurame...
K'arfe 1:15pm Motansu ya parker k'ofar wani madaidaicin gida,ginin gidan dai² na talaka dake cikin rufin asirin ubangiji,a cikin garin na DUTSE unguwan shiru babu hayaniya,fitowa BB yayi ya tsaya yana tunanin ko ina ne gidan daga cikin jerin gidajen?...
Sun shafe tsawon lokaci suna jira a gurin ba tare da ganin kowaba,sai zuwa can wani d'an dattijo ya fito daga zauren d'aya daga cikin gidajen,da alamun shima kamar gona zai tafi duk da wannan tsufan nashi...
Ganin mota tsaye bakin k'ofar gidan ya d'an kalli motan da mamaki a tare da shi...
Da sauri KHALEEL ya kalli BB
"MAN ya kamata fa mu tambayi wannan datijjon tun kafin mu rasa wanda kuma zamu tambaya"
Kallonsa BB yayi tare da murmushin k'arfin hali,sannan ya sake bud'e motan motan karo na biyu ya fita cikin sauri..
Matsowa yayi kusa da dattijon yayi masa sallama fuskarsa da fara'a,shima dattijon ya mayar masa da murmushin tare da amsa masa sallaman da yayi masa...
Bayan BB ya gaida shi ya amsa masa,sai kuma shiru ya ratsa tsakaninsu,tunanin BB ta ina zai fara masa bayanin abunda ya kawosu,shi kuma dattijon yana kallonsa ne irin na rashin sanin nan...
"Samari daga ina haka?sai dai kuma ban shaida kaba"
Sai da BB ya sake yin wani murmushin kafin ya fara magana
"BABA daga kano muke,to dama akwai wani gida da muke nema kuma dai gaskiya BABA gidan ne ya b'ace mana,saboda shekarun da yawa"
Murmushi dattijon yayi irin nasu na manya kafin ya tambayi BB
"'Dana wane gidane kuke nema haka?"
"Ehhh to BABA gidan MALAM ABDU MAI AL-MAJIRAI muke nema,ko nan ne unguwan da yake?"
Murmushi dattijon ya sake yi masa tare da gizgiza masa kai
"K'warai kuwa nan ne unguwan da yake gama gidan da kuke nema nan kusa da kai"
Ya fad'a tare da nuna k'ofar gidan da ya fito yanzun
"To amma wa kuke nema a gidan shi kuke nema ko wani daban kuke nema?"
Sosai BB yaji dad'in samun gidan da suka yi ba tare da sun sha wata wahalaba,fuskarsa d'auke da jin dad'in hakan ya furta
"BABA yana raye ne ko kuwa?"
"Sosaima kuwa d'an nan,sai dai ya jima yana jinya dan a halin da ake cikima yana kwance ne sai dai a tayar da shi saboda k'afafunsa da suka samu matsala"
"Eyyyahhh!Allah ya bashi lafiya....
Amma BABA idan da hali muna son ganinsa ne dan shi muka zo garin nan"
"To to kada ka damu yaro,bari na shiga na sanar masa da yana da bak'i tukuna"
Da sauri BB ya amsa da
‘’To BABA mun gode sosai‘’
Sai da ya ga shigan dattijon tukun ya juyo,ta saitin window en da KHALEEL yake ya tsaya tare da knocking..
Sauke glass en yayi yana kallonsa
"Yahh!ina fatan dai munyi nasara"
"Sosaima kuwa Allah ya taimakemu wollahi,ashema a k'ofar gidan muka tsaya"
"Kaiiii!ammafa naji dad'i sosai wollahi,to amma KAKA yana raye kuwa?"
Sai da yayi wani k'ayataccen murmushi kafin ya amsa
"K'warai kuwa,sai dai kuma ance bashi da lafiya yanzun hakama"
Yanayinsa ya d'an sauya lokacin da ya fad'i hakan,shima KHALEEL en yanayin da yake kan fuskarsa kenan lokacin da yaji hakan...
"Allah dai yasa ba wani seriuos ciwo ne da zaisa ya kasa fuskantar dalilin zuwanmu ba"
KHALEEL ya fad'a yana sauraron yaji me BB zai ce kan hakan..
"Ameen kam dan wallahi har murnan da nake ya soma b'acewa,gaskiya ina cikin damuwa yanzun haka da naji wannan maganar"
"Tohh!Allah yasa dai babu wani abu da zai mayar mana da farin cikinmu baya"
Suna cikin maganar dattijon ya fito yana waigawa yaga ina saurayin ya nufa kuma,bayan ya barshi tsaye a k'ofar gidan....
A jikin motan ya hango shi ya jingina,k'arasowa yayi da murmushi a fuskarsa
"To samari zaka iya shiga yana sauraren zuwanka"
Kallon KHALEEL yayi da yake k'ok'arin fitowa daga motan,sukama juna murmushin k'arfin hali sannan sukabi bayan dattijon zuwa cikin gidan....
Mata ne da k'ananan yara wad'anda bazasu iya aikin gonaba sunata aikace-aikace a tsakar gidan,gaisuwa kam su BB sun shata musamman da aka gansu da shiga data bambanta da yanayin y'an garin...
Haka sukaita wucewa har suka isa turakar mai gidan,shigansu suka tarar da wani DATTIJO da yafi wanda ya rakosu tsufa a kwance k'afafunsa sun kumbura sosai suna tsatstsafar da ruwa ta jikinsu...
Da tausayawa suke kallonsa wanda duk mai raunin zuciya idan ya kalli k'afafun sai yayi masa hawaye,inda tafin k'afar tasa yayi wani irin sai wata irin sab'a yake kamar jikin maciji.....
Kallon yanayin da yake ciki yasa jikinsu dad'a yin sanyi,dan har sun yanke tsammani da cewa wannan dattijo zai gane duk wani bayani da zasuyi masa a wannan lokacin,sai dai kuma maganarsa ta basu mamaki matuk'a...
"Marhaban lale"
Juyawa sukayi suka kalli juna da mamaki,sannan kuma suka kalli dattijon dake kwance...
Guri suka samu suka zauna,nan dattijon da ya rakosu shima ya samu guri ya zauna daga gefen wannan dattijo dake kwance...
"Samari daga ina haka?ban shaida fuskokinkuba"
Sai da suka sake kallon juna sukayi murmushi tukun BB ya juya ya kalli dattijon tare da fad'in
"BABA mu bak'i ne daga garin KANO,sai dai kuma ba lallaine dama ace ka ganemu ba"
K'ura masa ido dattijon yayi da alama akwai wani abu da yake son karanta akan fuskarsa da har yasa yake masa irin wannan kallon k'urilla,yanayin kallon da yake masa ne yasa shi yin shiru yana binsa shima da ido had'e da murmushi...
"Yaka nan zo maza,matso kusa dani kaji zo?...
Ina ji ajikina wannan yaron duk inda ya fito jini nane shi duk inda ya fito"
Da mamaki suka sake kallon juna shi da KHALEEL,inda KHALEEL en ya d'aga masa kai alamar yaje gurin dattijon...
Matsawa yayi kusa da dattijon,shi kuma sai k'ok'arin mik'ewa yake ya zauna,da sauri d'aya dattijon da ya rakosu ya mik'e ya kamashi ya zaunar...
Hannunsa ya mik'a ya rik'o BB yana dad'a kallonsa...
"Tabbas ko tantama babu wannan yaro duk inda ya fito jinin SAFWAN ne....
Allah sarkin hikima,yaro ina ka baro SAFWAN en?
Yana raye ko kuwa ya mutu ne?
Iya tsawon wannan lokaci SAFWAN ya watsar damu sam yak'i zuwa ya ganmu duk tsayin wad'annan shekaru,ina ya shiga haka?"
Ganin bai bashi amsaba yasa shi sake fad'in
"Yaro ka sanar dani ko dai da gaske SAFWAN en ya rasu kamar yadda nake mafarki?"
A lokacin da yayi wannan maganar idanunsa har sun kawo ruwa,wanda suke shirin zubowa,saboda rashin sanin amsar da za a bashi...
"A'a BABA yana raye"
BB ya fad'a wanda fad'ar hakan yasa KHALEEL ya kalleshi,zuciyarsa cike da tunanin
‘’Too kaji mutumin nan yana neman b'allo mana ruwa,idan har ABBA yana raye a wane bigere yake rayuwa,ko kuwa yasan inda ABBAN yake da har ya fad'i haka?‘’
Saurin katse tunaninsa yayi ya sake maida hankalinsa kan abunda BB zai fad'a...
"Too Alhamdulillah da har kuwa yana raye,amma me ya faru tsawon wannan shekaru ya kasa zuwa ya ganmu bayan yasan muna raye kuma muna cikin garin nan,idanma ace bana raye shin ba ga y'an uwansa nanba da suke ciki d'aya,ko kuwa shi kenan ya yanke zumunci da mu?"
Shigowar BABA ZUWAIRA kenan gidan ta tarar da KHUBRA kwance tsakar gida saman tabarmar kaba....
'Dan d'ago da kanta tayi kad'an ta kalli BABA sannan ta sake maida kanta ta kwantar saman hannunta da tayi matashi da shi.
"Sannu da dawowa BABA"
"Yawwa y'ar nan,kinga na ce zan aiko miki da magani shiru gashi da gani jikin naki ke damunki...
Yau kam ISAH bai fito da wuriba shima sai yanzu da zan taho na biya naganshi...
Shi ne yake shaidamin gona yaje dubawa,Allah dai ya taimaka na samo miki maganin,yi maza ki tashi ki sha kinji idan aka jima an yi sallar ishaa sai ki kwanta kinji ko,Allah dai ya baki lafiya"
Duk maganar nan da BABA ZUWAIRA ke yi hankalin KHUBRA ba a kanta yake ba,tunani ne iri² duk zuciyarta ta cunkushe,jinta take a wannan lokacin tana so tayi kuka ko zata samu sauk'in rad'ad'in dake damunta a zuciyarta,a cikin kwanakin nan tana yawan yin mugayen mafarkai da wani mutum da har zuwa yanzun ta kasa tantance waye ne,sai dai duk lokacin da zata ganshi cikin muguwar damuwa take ganinsa wannan dalilin da yasa mafarkin ya tsaya mata a rai,yawan mafarkin da take da shi yasa ta shiga damuwa da ta haddasa mata ciwon jikin da take fama da shi cikin satin....
Sai da BABA ZUWAIRA ta tab'ata sannan ta tashi ta zauna had'e da karb'ar maganin tana juyashi a hannunta...
Da kyar ta samu tasha maganin sannan ta tashi da nufi yin sallah....
Tun misalin k'arfe 8:30pm tayiwa BABA ZUWAIRA salamma ta shige d'aki,ita ko BABA'N a lokacin tunaninta duk jikin ke damunta,ta dai bita da fatan samun sauk'i fuskarta duk alamun damuwa da halin da y'ar tata ke ciki...
Ko da ta shiga d'akin bayan ta kwanta nan ta shak'i kukanta har ta godewa Allah...
Sai bayan ta gama kukan ta tsaya tunanin menema wai yasata kuka haka?
Tana wannan tunanin bacci ya d'auketa cike da mafarkai iri-iri....
《《》》
Gari na wayewa suka hau shirin barin garin,misalin k'arfe 10:00am suka yiwa UMMI sallama suka mik'i hanya bayan d'umbin nasiha da suka sha a gurinta sannan ta musu fatan dawowa lafiya...
Sai da suka biya suka ga jikin MAMA,sai daifa har zuwa wannan lokacin MAMA bata sanma wanda yake kanta ba,bare ta samu damar yin magana.....
Daga nan suka d'auki hanya sai garin na JIGAWA DUTSE......
乛乛乛乛乛
Safe trip BB and KHALEEL.....
*~TEAM KHUBRA.~*
*_REAL SMASHER._*
💠
*Y'AR GARUWA......*
*(ɬɧɛ mơʂɬ ɧɛąrɬ ɬơųcɧıŋɠ ʂɬơrყ).*
🕊🕊🕊🕊
🌹🌹🌹
*©®2018*
*1/ʝųlყ,2018*
*ʂɬơrყ ąŋɖ wrıɬɛɛŋ*
*ცყ*
_HAWWA M.U {$мaѕнer}_
🕊🕊🕊🕊🕊
🌹🌹🌹🌹
_BISMILLAHIR-RAHMANIR-RAHEEM..._
*~________________________~*
_Matso maza kuji mutanen arziki,wollah a duk inda kuke ina k'aunarku irin wacce bazata fad'uba kuma ina alfahari daku_
*MISS ABATCHA,ZAINAB (ZEE MA'DAGWAS & KHADIJA (FRESH KHADEEY)*
_Kuyi komai ba komai mutanena Allah ya bar k'auna....*ME LUV U* ❤ irin tottaly ennan..._
*~__________________________~*
*DEVOTED TO:*
_BILKISU M.ADAM (Y'AR ABBA)_
*BESTOWED TO:*
_MURJA SALIS (NA'IKKE)._
*AND*
_FATIMA ABUBAKAR (FATEEY AFIRST)._
*3⃣8⃣*
*T* afiya ta mik'a a b'angarensu BB,inda babu wanda ke wata magana hakan ne yasa tafiyan nasu ya zama kamar na kurame...
K'arfe 1:15pm Motansu ya parker k'ofar wani madaidaicin gida,ginin gidan dai² na talaka dake cikin rufin asirin ubangiji,a cikin garin na DUTSE unguwan shiru babu hayaniya,fitowa BB yayi ya tsaya yana tunanin ko ina ne gidan daga cikin jerin gidajen?...
Sun shafe tsawon lokaci suna jira a gurin ba tare da ganin kowaba,sai zuwa can wani d'an dattijo ya fito daga zauren d'aya daga cikin gidajen,da alamun shima kamar gona zai tafi duk da wannan tsufan nashi...
Ganin mota tsaye bakin k'ofar gidan ya d'an kalli motan da mamaki a tare da shi...
Da sauri KHALEEL ya kalli BB
"MAN ya kamata fa mu tambayi wannan datijjon tun kafin mu rasa wanda kuma zamu tambaya"
Kallonsa BB yayi tare da murmushin k'arfin hali,sannan ya sake bud'e motan motan karo na biyu ya fita cikin sauri..
Matsowa yayi kusa da dattijon yayi masa sallama fuskarsa da fara'a,shima dattijon ya mayar masa da murmushin tare da amsa masa sallaman da yayi masa...
Bayan BB ya gaida shi ya amsa masa,sai kuma shiru ya ratsa tsakaninsu,tunanin BB ta ina zai fara masa bayanin abunda ya kawosu,shi kuma dattijon yana kallonsa ne irin na rashin sanin nan...
"Samari daga ina haka?sai dai kuma ban shaida kaba"
Sai da BB ya sake yin wani murmushin kafin ya fara magana
"BABA daga kano muke,to dama akwai wani gida da muke nema kuma dai gaskiya BABA gidan ne ya b'ace mana,saboda shekarun da yawa"
Murmushi dattijon yayi irin nasu na manya kafin ya tambayi BB
"'Dana wane gidane kuke nema haka?"
"Ehhh to BABA gidan MALAM ABDU MAI AL-MAJIRAI muke nema,ko nan ne unguwan da yake?"
Murmushi dattijon ya sake yi masa tare da gizgiza masa kai
"K'warai kuwa nan ne unguwan da yake gama gidan da kuke nema nan kusa da kai"
Ya fad'a tare da nuna k'ofar gidan da ya fito yanzun
"To amma wa kuke nema a gidan shi kuke nema ko wani daban kuke nema?"
Sosai BB yaji dad'in samun gidan da suka yi ba tare da sun sha wata wahalaba,fuskarsa d'auke da jin dad'in hakan ya furta
"BABA yana raye ne ko kuwa?"
"Sosaima kuwa d'an nan,sai dai ya jima yana jinya dan a halin da ake cikima yana kwance ne sai dai a tayar da shi saboda k'afafunsa da suka samu matsala"
"Eyyyahhh!Allah ya bashi lafiya....
Amma BABA idan da hali muna son ganinsa ne dan shi muka zo garin nan"
"To to kada ka damu yaro,bari na shiga na sanar masa da yana da bak'i tukuna"
Da sauri BB ya amsa da
‘’To BABA mun gode sosai‘’
Sai da ya ga shigan dattijon tukun ya juyo,ta saitin window en da KHALEEL yake ya tsaya tare da knocking..
Sauke glass en yayi yana kallonsa
"Yahh!ina fatan dai munyi nasara"
"Sosaima kuwa Allah ya taimakemu wollahi,ashema a k'ofar gidan muka tsaya"
"Kaiiii!ammafa naji dad'i sosai wollahi,to amma KAKA yana raye kuwa?"
Sai da yayi wani k'ayataccen murmushi kafin ya amsa
"K'warai kuwa,sai dai kuma ance bashi da lafiya yanzun hakama"
Yanayinsa ya d'an sauya lokacin da ya fad'i hakan,shima KHALEEL en yanayin da yake kan fuskarsa kenan lokacin da yaji hakan...
"Allah dai yasa ba wani seriuos ciwo ne da zaisa ya kasa fuskantar dalilin zuwanmu ba"
KHALEEL ya fad'a yana sauraron yaji me BB zai ce kan hakan..
"Ameen kam dan wallahi har murnan da nake ya soma b'acewa,gaskiya ina cikin damuwa yanzun haka da naji wannan maganar"
"Tohh!Allah yasa dai babu wani abu da zai mayar mana da farin cikinmu baya"
Suna cikin maganar dattijon ya fito yana waigawa yaga ina saurayin ya nufa kuma,bayan ya barshi tsaye a k'ofar gidan....
A jikin motan ya hango shi ya jingina,k'arasowa yayi da murmushi a fuskarsa
"To samari zaka iya shiga yana sauraren zuwanka"
Kallon KHALEEL yayi da yake k'ok'arin fitowa daga motan,sukama juna murmushin k'arfin hali sannan sukabi bayan dattijon zuwa cikin gidan....
Mata ne da k'ananan yara wad'anda bazasu iya aikin gonaba sunata aikace-aikace a tsakar gidan,gaisuwa kam su BB sun shata musamman da aka gansu da shiga data bambanta da yanayin y'an garin...
Haka sukaita wucewa har suka isa turakar mai gidan,shigansu suka tarar da wani DATTIJO da yafi wanda ya rakosu tsufa a kwance k'afafunsa sun kumbura sosai suna tsatstsafar da ruwa ta jikinsu...
Da tausayawa suke kallonsa wanda duk mai raunin zuciya idan ya kalli k'afafun sai yayi masa hawaye,inda tafin k'afar tasa yayi wani irin sai wata irin sab'a yake kamar jikin maciji.....
Kallon yanayin da yake ciki yasa jikinsu dad'a yin sanyi,dan har sun yanke tsammani da cewa wannan dattijo zai gane duk wani bayani da zasuyi masa a wannan lokacin,sai dai kuma maganarsa ta basu mamaki matuk'a...
"Marhaban lale"
Juyawa sukayi suka kalli juna da mamaki,sannan kuma suka kalli dattijon dake kwance...
Guri suka samu suka zauna,nan dattijon da ya rakosu shima ya samu guri ya zauna daga gefen wannan dattijo dake kwance...
"Samari daga ina haka?ban shaida fuskokinkuba"
Sai da suka sake kallon juna sukayi murmushi tukun BB ya juya ya kalli dattijon tare da fad'in
"BABA mu bak'i ne daga garin KANO,sai dai kuma ba lallaine dama ace ka ganemu ba"
K'ura masa ido dattijon yayi da alama akwai wani abu da yake son karanta akan fuskarsa da har yasa yake masa irin wannan kallon k'urilla,yanayin kallon da yake masa ne yasa shi yin shiru yana binsa shima da ido had'e da murmushi...
"Yaka nan zo maza,matso kusa dani kaji zo?...
Ina ji ajikina wannan yaron duk inda ya fito jini nane shi duk inda ya fito"
Da mamaki suka sake kallon juna shi da KHALEEL,inda KHALEEL en ya d'aga masa kai alamar yaje gurin dattijon...
Matsawa yayi kusa da dattijon,shi kuma sai k'ok'arin mik'ewa yake ya zauna,da sauri d'aya dattijon da ya rakosu ya mik'e ya kamashi ya zaunar...
Hannunsa ya mik'a ya rik'o BB yana dad'a kallonsa...
"Tabbas ko tantama babu wannan yaro duk inda ya fito jinin SAFWAN ne....
Allah sarkin hikima,yaro ina ka baro SAFWAN en?
Yana raye ko kuwa ya mutu ne?
Iya tsawon wannan lokaci SAFWAN ya watsar damu sam yak'i zuwa ya ganmu duk tsayin wad'annan shekaru,ina ya shiga haka?"
Ganin bai bashi amsaba yasa shi sake fad'in
"Yaro ka sanar dani ko dai da gaske SAFWAN en ya rasu kamar yadda nake mafarki?"
A lokacin da yayi wannan maganar idanunsa har sun kawo ruwa,wanda suke shirin zubowa,saboda rashin sanin amsar da za a bashi...
"A'a BABA yana raye"
BB ya fad'a wanda fad'ar hakan yasa KHALEEL ya kalleshi,zuciyarsa cike da tunanin
‘’Too kaji mutumin nan yana neman b'allo mana ruwa,idan har ABBA yana raye a wane bigere yake rayuwa,ko kuwa yasan inda ABBAN yake da har ya fad'i haka?‘’
Saurin katse tunaninsa yayi ya sake maida hankalinsa kan abunda BB zai fad'a...
"Too Alhamdulillah da har kuwa yana raye,amma me ya faru tsawon wannan shekaru ya kasa zuwa ya ganmu bayan yasan muna raye kuma muna cikin garin nan,idanma ace bana raye shin ba ga y'an uwansa nanba da suke ciki d'aya,ko kuwa shi kenan ya yanke zumunci da mu?"