← Book details Yar Garuwa Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 61 OF 86

Sashe 61

Yar Garuwa Part 1 Complete Hausa Novel · about 7 min read

"Yo to kai d'in ne ai kake bani mamaki...cikin lokaci k'alilan kamar wani mai shafar jinnu..yau a ganka kana d'aci gobe kuma ka sake rikid'ewa ka koma ba kaiba"

Dariya yayi "To waya sani ne ko na koma cin wahainiya...kasan idan mutum na ci rikid'ewa yake yau ka ganshi a wannan siffar gobe kuma ya sake komawa wata"

Kallonsa kawai KHALEEL yayi ya furta
"Allah ya kyauta..."

"Ameen...!"

"To amma shi wannan glass enfa daka toshe da shi kamar wani sabon makaho,na lafiya ne kuwa?"

Banza ya masa yayi kamar bazai yi maganaba,can kuma kamar wanda aka tilasta ya furta
"Idan baka son ganinsa ba dole aka maka sai ka kalle niba ai...Duk ka wani dami mutane da surutu dama kasan daka tashi karatu ka zama *JOURNALIST* dan naga yanzun abunda kafi k'auna kenan...Mutum sai d'an karen surutu kamar ya had'iya farrot,Allah yasa kada ka koyawa k'anwata wannan zancen..."

Dariya sosai maganar da yadda BB yake da face ensa ya bashi,KHALEEL jinsa yake yafi kowa dace a wannan ranar saboda aminin nasa ya dad'a sakin jiki da shi dan yau kam gashi harda su tsokana,suna ta faman tsokanan juna suka isa masallacin inda ake jiran k'arasowarsu.....

*11:00am*
Aka fara addu'ah sannan bayan gubatar da siga da akayi a cikin massalacin wanda duk abunda ake BB na wajen masallaci yak'i shiga sai KHALEEL en kawai ya shiga,aka fara sanar da d'aurin auren inda mai sanarwar ya fara sanarwar da d'aurin auren ta cikin abun magana kamar haka...

_AN 'DAURA AUREN *IBRAHIM-KHALEEL* DA AMARYARSA *KHADIJATUL-KHUBRA* AKAN SADAKI NAIRA NA GUGAN NAIRA HAR NAIRA DUBU 'DARI BIYAR........_

Ai jin wannan sanarwa take idanun BB dake cikin glass suka soma kawo ruwa,a lokacin kam ya gama tabbatarwa da kansa ya masifar yiwa kansa,ya cuci kansa cutar da baya tsammanin akwai wata cuta da zaiwa kansa kamarta,yasan yayi k'auron baki inda yanzu gashi nan abunda ya jawowa kansa.....Ya tabbata kam yanzun hak'uri ya zame masa dole.
Gefen k'irjinsa ya dafe saboda yadda yaji yana masa zafi lokaci guda tsaiwa ta soma neman ta gagare shi,a daddafe ya nufi mota shi kad'ai yasan me yake ji a guje kuma ya fizgi motan tare da bar in gurin..............😱😱😱😱

_Wayyoooo Allah ínα masoya KHALEED (BB) ku kαwσ αgαjí kαdα wani abu ya same shi........_

_mσvє fσwαrd tσ thє nєхt pαgє..._

*COMMENT FOR MORE PAGE'S*

*~#TEAM KHUBRA-KHALEEL.~*

*_®єαl $mαѕhєr._* 😉
💠💠💠💠💠

*Y'AR GARUWA......*
*(ɬɧɛ mơʂɬ ɧɛąrɬ ɬơųcɧıŋɠ ʂɬơrყ).*

🕊🕊🕊🕊
🌹🌹🌹

*fαcєвσσk grσup:* https://www.facebook.com/groups/369678263526212/

*©® 2018*
*25/ʝųlყ,2018*

*ʂɬơrყ ąŋɖ wrıɬɛɛŋ*
*ცყ*
_HAWWA M.U {$мaѕнer}_
🕊🕊🕊🕊🕊
🌹🌹🌹🌹

_BISMILLAHIR-RAHMANIR-RAHEEM..._
*~________________________~*

_rígíjí gαвjí....wαní kαчα ѕαí αmαlє...mαí kαmαr zuwα kαn αíkα....ídαn вα kαчí kα вαdα gurí dσmín вαnα ч'αr uwα kumα αвσkíчαr αíkí tα zσ dα wαní ѕαвσ mαí tαfє dα ѕαвσn ѕαlσ......_
_kαdα kují ínαtα zuвα ѕurutu gαmє dα в'αв'αtu вα kσwα nαkє nufí вα fαcє *AUNTY MAIMOUNATH O.G* dσmín kuwα вαnαmα tα dαwσ muku dα ѕαвσn nσvєl nαtα mαí cíkє dα dαrαѕí,ílímí,fαd'αkαrwα tαrє kumα dα k'αчαtαrwα ku nєmí nσvєl єntα mαí tαkєn *MEELAT TAMU*..._
_dαurє kα/kí nєmí nαkí α duníчαr ❄ domin kαdα α вαku lαвαrí........kαdαfα ku mαntα dα ѕunαn...._
*MEELAT TAMU.!*
*MEELAT TAMU.!!*
_ku nєmα ku ѕhα kαllσ tαrє dα kαrαtu,kαdα ku ѕαkє α вαku lαвαrííííí..._
*~__________________________~*
_jínjínα tαrє dα gσdíчα gαrєkí mαruвucíчαr zαmαní *HALISSA ADAMOU* ч'αr mutαn nígєr mαвucíчαr *MARAYUMA Y'AY'A NE* kí jímα kíчí k'αrkσ tαwαn αllαh чα k'αrα míkí lαfíчα dα níѕαn kwαnα mαí αmfαní.. *SMASHER & HUBBEEY* nα gσdíчα dα kαrrαmαwαrkí gαrє ѕu.αllαh чα вαr zumuncí._
*~__________________________~*

*DEVOTED TO:*
_BILKISU M.ADAM (Y'AR ABBA)_

*BESTOWED TO:*
_MURJA SALIS (NA'IKKE)._

*AND*

_FATIMA ABUBAKAR (FATEEY AFIRST)._

5⃣3⃣

*K* asa controling temper ensa yayi wanda shi ne babban dalilin da yasa shi baro gurin ko tsayawa jin sauran d'aurin auren baiba ya baro gurin,bai zarce ko inaba sai gida wanda ikon Allah kad'ai ya kai shi,gidan a cike yake da jama'a amma sam BB bai iya gane abunda ke gaban sama bare kuma magana da ake masa da bai sanma suna yiba bare ya iya basu amsa.
Bedroom ya shige nan ko ya shiga watsi da kayan jikinsa d'aya bayan d'aya har ya gama raba jikinsa da kayan ya rage daga shi sai singlet da wandon kayan kifewa yayi a k'asa take wasu hawaye masu matuk'ar k'una suka shiga tsere a saman fuskarsa,a wannan yanayin duk wanda yaganshi dole ne ya tausaya masa saboda ganin garjejen saurayi majiyin k'arfi yana kuka da hawaye dole abun ya baka mamaki game kuma da tsoro coz irin su ba komai ke sasu yin kukaba.
Damuwa ta tarun masa gami da dana sani wacce bata da amfani,a dai-dai wannan lokacin da kowa ke cikin farin ciki da wannan ranar mai cike da tarihi,amma sam a gurin BB babu wannan labarin sai yanzun ya tabbata da ya tafka kuskure game kuma da asara wacce ba zai tab'a samun hanyan da zai gyaraba.
Babu abunda yake banda wani irin haki mai ban tsoro idanunsa sun canja launi zuwa jaa mai duhu,kwanciya yayi nan k'asa dafe da k'irjinsa da yake jinsa kamar zai tarwatse saboda azabar ciwo da yake masa....

*GURIN 'DAURIN AURE.*
Bayan fitowar su KHALEEL lokacin an gama d'aurin aure,Nanfa yayi ta dubawa bai ga BB a gurinba duk yadda yaso ya ganshi abun ya faskara,ko da ya tambaya wad'anda suka ga fitarsa sun sanar masa ya jima da fita,ko da yaji haka k'ok'arin kiransa yayita yi amma wayoyin sai ringing suke ank'i d'auka,duk k'ok'arin da yayita yi babu amsa,hak'ura yayi amma kuma hankalinsa baya tare da shi,kawai dai jama'an da suka kewaye shi ne yasa bai tafi nemansa ba dan yasan ba k'aramin abu ne yasa shi barin gurinba kuma har ya hana shi d'aukan kiransa.
Haka suka wuce gurin reception daga nan,har akayi aka watse abokai da y'an uwa sunata musu Allah ya bada zaman lafiya,ana gamawa ko bai zarce ko inaba sai gidansu BB,direct d'akinsa ya nufa dan yasan can ne kad'ai zai sameshi.
Abunda ya gani ya matuk'ar bashi mamaki game da tsoro wanda baiyi tsammaniba,magana ya shiga yi masa a hankali BB dake kwance k'asa ya d'ago rinannun idanunsa ya kalleshi da sauri kuma ya maida kansa ya kwantar wanda gaba d'ayan veins na kan sun gamaa bayyana.
"Hasbunallahu wa-ni'imal wakeel....!
KHALEED lafiyar ka k'alau kuwa,me yasa kake son zama cikin damuwa? me yake damunka ne kam...?"
Banza yayi masa saima kulle idanunsa da yayi dan bai shiryawa jin maganganun KHALEEL enba yanzun da yake cikin wannan halin

Jiki a sanyaye KHALEEL ya nemi guri ya zauna,a zuciyarsa ya furta
"Ya kamata na sanar masa yanzun ko kuwa....?"
Da hanzari kuma cikin tausayi ya kalli BB yana fad'in
"Tashi za muyi magana yanzun..."
Banza ya sake masa,hannunsa dafe da kansa da yake barazanar tarwatsewa,hakan da yayi masa yasa shi sake kallonsa,duk k'ok'arinsa na ya kwantar masa da hankali yasa shi kuma magana dan ya kore masa damuwan hakan ya faskara dan Sam yak'i bashi had'in kai,wayansa ya shiga pressing cikin apps nasa ya binciko app na *MAHEER MU-AQQILIIY* sauka ne complete amma a app yake nan ya kunna tun daga fatiha suke sauraro tare a lokacin da kuma suke zaman kurame,yini guda sallah kad'ai ke tada su,itama nan suke yinta cikin d'aki babu mai fita,weeding pics da ake da amarya da ango saboda tarihi a wannan ranar kama sam amaryar KHALEEL bata sashi a idanuntaba,dan ko suna can zaman makoki shi da aminin nasa...

B'angaren AMARYA KHUBRA ko tun bayan da aka dawo da labarin an d'aura aure ta dad'a lafkewa kan bed dan ko dama tuni take fama da matsanancin ciwon kai wanda ya saukar mata da zazzab'i mai zafin gaske.
Da k'yar aka samu ta iya shiryawa shima sai da taimakon ZUHRA,tana kwance ZUHRA na gefenta labarin d'aurin aure ya riskesu,jikinta ko ya sake rikicewa,tana kwance cikin duvet amma kana hango yadda jikinta ke vibrating kamar wacce aka jonama shocking.
Duk k'ok'arin da MAMA take akan samun su KHALEEL a waya hakan ya faskara kan dole ta kira line en ABBA,shi enma dai suna tare da mutane lokacin da take kira dalili kenan daya sa bata same shiba,k'arshe dai sai magani aka bata haka da k'yar da sid'in goshi zazzab'in ya sauka sai ciwon kan da yak'i tafiya coz dama haka ciwon kai yake mata baya saurin tafiya idan ta fara.
Chapter 61 · 0% Book details