Sashe 24
Yar Garuwa Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
''Innalillahi wa-inna ilaihi raji'un''
Bakinta keta maimaitawa har sai da ta samu nutsuwa kafin wasu tambayoyin suka shiga tseren fitowa daga bakinta
''Yaushe?kuma a ina hakan ta faru? garin yaya?ita HAJIYA MURJA tana wane sakacin aka d'auke y'ar mutane?ko kuwa bata sani ba?''
Kallon UMMIN nasa ya shiga yi uwa wanda ya fara ganinta yau
''Wallahi UMMI abunda na manta ban tambayi KHALEED ba kenan......
Amma gaskiya UMMI ina zargin da sa hannun HAJIYANSA''
Ta gefe ya d'an kalleta yana mai rik'e bakinsa,tunawa da warning da tayi masa
''Amma kiyi hak'uri UMMI idan na fad'i abunda ba dai² ba''
Kai ta kad'a masa kafin cike da mamaki ta soma magana
''Tabbas ko ni da kaina jin wannan maganar yasamin zargin HAJIYA MURJA....Da gangan akayi......Ko tantama babu wannan aikin shiryashi akayi,akwai sa hannu cikinsa''
Shiru dukansu sukayi suna jinjina lamarin...
''Allah ya kyauta,Allah ka kare baiwarka a duk inda take''
Abunda ya iya fitowa daga bakinta kenan ta sake yin shiru tana jaddada al'amarin a zuciyarta....
《《》》
ZUHRA ce ta fito da kumburarren fuskanta zata kitchen danko k'ishi ke damunta,ta fito da niyyan d'auko ruwa,dai² zata wuce ta k'ofan MAMA ta ji ana magana k'asa²,kunnenta ta d'ora jikin k'ofan take ko kalaman da ta jiyo suka sake firgitata....
''Ehhh!ba damuwa HAJIYA LAURA ai kin gamamin komai da kika samomin mafita''
Dariya ta saki mai k'arfi kafin ta ci gaba
''Wallahi kuwa mun rabu da kaska.....Yo to ta inama za ayi wata Housemaid zata zo tana neman juyamin kai.......maza biyu lokaci guda fa duk sun haukace kanta,shi wancan da yafi kowa haukama harda turomin mahaifiyarsa bayan ga y'an mata nan ina da su bai zab'i kowacce ba sai ita........Uhmm!shi kuma KHALEED......Ai ki barni da su tunda yanzun munyi maganinsu.....Allah kuwa,to ameen...Sai kin jini''
Jin maganganun tayi suna mata yawo akai,kenan zarginta ya zama gaskiya kan MAMA,hawayene suka sake b'alle mata,dafe bakinta tayi tana jiyo maganar MAMA,daga jima ka san da kanta take
''Ya zama dole na raba gidan nan da duk wani abu da zai sake tunamin da ke......
Barima kiga na tashi kaf kayanki dake gidan nan k'onasu zanyi,mun dai rabu da kaska sai aje can a sha jinin wani''
Jin kalamanta na k'arshe yasa ZUHRA saurin mik'ewa hanyan fita daga parlor ta nufa tana tafe tana hard'ewa kamar za ta kifa,har ta fice daga parlorn...
Kansa ya had'e da steering motan ya shiga tunanin da bai san me yake tunawa ba,tsawon mintuna arba'in yana cikin motan ba tare da ya iya fitowa ba,kuma har lokacin ya kasa kashe motan...
Fitowan ZUHRA daga cikin parlor tana waigawa tana kallon hanya tamkar wacce wani abun tsoro ya biyo,shi kuma ya d'ago yana bud'e motan had'e da kashewa ya fice,tafiya yake jikinsa babu k'wari...
Buge juna suka yi da sauri ta d'ago ba tare da iya yin maganaba ta d'aga masa hannunta alamar ban hak'uri,tayi gaba abunta,tana kuma ci gaba da waiwayen hanya....
Kallonta kawai yayi,yanayin da take ciki ya tabbatar masa akwai damuwa,har zai shiga parlor ya fasa a baya ya bi hanyan da ta bi,har k'ofan d'akin..
A ciki ya tsintota tana ta faman binciken kayan dake d'akin,da k'yar ta iya gano keys en d'akin,kayan ta shiga d'iba tana zubawa a closet dake had'e cikin wall en d'akin.....
Yana tsaye bakin d'akin yana kallonta har ta kammala ta fito,da sauri ta maida k'ofan ta rufe had'e da danna mata key.....
Sai da ta juyo zata bar gurin sannan ta ganshi tsaye ya hard'e hannayensa a chest yana kallonta...
《《》》
Sai da ta gama kukan sannan ta mik'e ta karkad'e kayanta da suka b'aci da k'asa,zuciyarta cike da kishin kanta da tausayin rayuwarta ta sake d'ora hannunta a kan marik'in kuran....
Dannawa ta shiga yi,duk k'ok'arinta bai wuce taga ta taimaki kanta ba,addu'ah ta soma duk wacce tazo bakinta yi take kan neman taimako daga mahalicci,cikin ikon Allah tana ta k'ok'arin turawa bakinta kuma bai fasa ambaton Allah ba,tafiya kuran ya soma ta juyo da akalar kuran zuwa garin da suka bari yanzun....
Da k'yar take iya turawa,fuskanta zuwa jikinta duk yayi gumi kan wahalar da tasha na turo kuran,idan ta gaji ta tsaya ta huta haka taita fama har ta fara shigowa cikin garin....
Jama'a sai kallonta suke da mamaki yayin da wasu ke binta,ita kam ko a jikinta,dan ta d'aura aniyar neman halak enta,sana'a babu fashi yanzun ta soma duk abunda mutane za suyi babu ruwanta,za ta toshe kunnenta daga tsaigumin su,haka taita turawa tana wucewa,line ta soma bi d'aya bayan d'aya,wani line en idan ta shiga za ta tarar da shi cike da mutane y'an gulma wad'anda labari ya iske,ba maza ba mata,hatta da k'ananan yara binta suke duk inda tayi,ita ko ko a jikinta....
Ganin wannan sabon al'amari yasa mutane siyan ruwan ga wand'an dama basuyi niyyaba duk dan su shaida labarin da ya iske su,duk gidan da suka siya dai kaga wasu daga cikin y'ay'ansu maza suna saukewa suna shiga da shi,idan sun juye su bata kud'inta da jarkanta,haka zata k'ara gaba su kuma su bita da idanu...
Kafin wani lokaci babu komai cikin kuran nata duka ruwan an siye babu sauran,bakin wata bishiya ta zauna tana lissafa kud'in naira d'ari biyu #200 cif,hamdala tayiwa Allah kafin ta huta abunta,bakin kasuwa ta sake komawa ta nemi mai abinci a gurin,tunani ta tsaya yi to na nawama ya kamata ta siya ne?
Ta d'an jima tana yanke shawara,kan ta bayar duka ko a'a.....
Mik'awa tayi duka ba tare da ta tantance ko yayi yawa ko baiba...
Mai abincin ce ta kalleta da alamar mamaki tana fad'in
''Ke ko y'ar nan me za kiyi da abinci har na d'ari biyu,ai yayi miki yawa,ungo wannan''
Ta mik'o mata d'ari da hamshin,d'an murmushin k'arfin hali tayi ta karb'a tana mata godiya...
''A robber zan zuba miki ko kuwa a leda?na ga kamar bak'uwace ke ko?''
'Dan murmushin ta sake yi tana fad'in
''Eehh!ni bak'uwa ce''
''Allah sarki ai na ga alama tun zuwanki gurin nan''
Bata kuma magana ba ta karb'i abincintan a gefe ta samu guri ta zauna,ko rabi bata iya cinyewa ba ta mik'e tana dawowa matar da robber enta da sauran abincin ciki,kallon mamaki tayi mata kafin ta iya tambayarta
''Me ya faru kika dawo da shi haka?''
''Uhmm!babu komai wollah babata na k'oshi ne''
Kalmominta da ta kira matar da shi wato ''BABATA'' su suka sa matar yin k'wallar farin ciki,kasancewarta bata tab'a haihuwa ba,har Allah ya d'auki ran mijin nata,tun daga nan kuma bata kuma wani auren ba...
Ganin matar na hawaye ya sanyayawa KHUBRA jiki,haka taita kallonta uwa wata doluwa....
''Y'ar nan gidan wa kika zo a garin nan?''
Tambayar ta bawa KHUBRA mamaki,amma sai bata nuna ba
''Ban san kowa ba a garin nan,nima kawoni akayi nan''
Da mamaki matar ke kallon KHUBRAN tana fad'in
''Kawoki akayi kuma?''
Kai ta kad'a mata,mik'ewa tayi tana kad'e jikinta da niyyan barin gurin
''Yanzun ina kika nufa y'ata?''
''Zan wuce ne''
'Dan tunanin matar tayi da sauri kuma ta katse KHUBRA dake haramar barin gurin
''Y'ata idan za ki yarda kuma kin amince ba zan tab'a cutar da ke ba,kuma idan har kin d'aukeni uwa a gareki......
Zaki iya bina gidana mu zauna tare,kin ganni nan tsawon shekaru talatin da biyar da aurena Allah bai tab'a azurtani da d'aba,amma yau na farko kin kirani MAHAIFIYA wannan dalilin yasa naji ina k'aunarki,tabbas zan rik'eki a matsayin y'a,idan har kin amince''....
Ta k'arashe maganar ta tare da goge wani layin hawaye dake kan fuskanta....
'Dan tak'aitaccen murmushin yak'e tayi,kafin zuciyarta ta tuna mata abunda aka mata yanxun da ko awanni biyar ba ayiba....
Da sauri kuma wata zuciyar ta bata amsa da cewa
''Haba KHUBRA duniyar nanfa ba duka aka zama d'ayaba,ya kamata ki tuna yadda rayuwar ki ta faro,wasu na sonki wasu na k'inki,kada kiyi saurin yanke hukunci,kiyi addu'ah dan shi ne gatanki a rayuwa a kuma duniyarki''......
Siririyar ajiyar zuciya tayi,kafin ta furta
''Na amince BABATA amma da sharad'i''
Matar tana murna ta kalleta
''Koma wane irin sharad'ine na yarje miki fad'i kome kike so in sha Allah bazan gazaba''
''Dama ina so ne nace...... Baba don Allah kada ki hanani neman abunda zan rufawa kaina asiri,komai tsafta,k'azanta,k'ask'anci ko samu da sana'ar take d'auke da shi''....
Kallonta kawai matar tayi
''In sha Allah bazan hanaki ba.....
Amma wace irin sana'a ce wannan?''
''Ba wata sana'a bace illa *GARUWA.............''*
A d'an tsorace ta kalli KHUBRAN,ita ko sai murmushi take abunta,da fuskanta da har yanzun tak'i komawa dai²....
Gudun kada tayi magana akan sana'ar ta KHUBRAN tak'i amincewa da buk'atarta,yasa taja baki tayi shiru,tana nai fad'in
''To shi kenan Allah ya wuce mana gaba,yayi miki jagora''
KHUBRA ta amsa da ameen.....
''To yanzun dai da kin bari sai zuwa gobe ko dan mu tafi tare kinga kyaga gidan namu ko?''
Ta fad'a tana d'an murmushi,itama KHUBRAN murmushi tayi ta sake neman guri ta zauna,tana ta kallon mutane da keta zuwa siyan abinci,tana zaune har abincin ya k'are tas,tana kallo matar ta kammala had'a kayan al-majirai suka d'aukan mata kayan nan ta juyo tana kallon KHUBRA
''Taso mu tafi y'ata''
Babu musu ta shiga bin matar a baya suna tafe tana tura kuranta na ruwa har suka isko wani k'aramin gida,nan suka shiga suka nemi guri KHUBRA ta adana kuranta da niyyan gobe da wuri zata fita sana'anta.....
《《》》
Kallonta yayi duk ta wani birkice
''Me yake damunki SISNAH?''
Bata iya bashi amsaba,hannunsa kad'ai ta jaa zuwa guarding suna tafe tana waiwayawa tana kallon hanya,guri suka samu suka zauna sannan a d'an tsorace ta juyo
''YAYANAH wallahi ina jin tsoro kada wani abu ya samu KHUBRA......Duk abunda ya faru BB MAMA ta san komai kuma wollahi da hannuta komai da ya faru,MAMA ce sila......Dan Allah YAYANAH ka nemomin ita pleasee''
Ta k'arasa tana rintse idanunta....
Tashin hankalinsa k'aruwa yayi jin ta ambaci MAMA,amma ya akayi tasan da sa hannun MAMAN a ciki?Yama kansa tambayan.....
''Me yasa kikace da sa hannun MAMA?''
Ya mata tambaya yana mai jin fad'uwar gaba,dan bai san wane amsane zai fito daga bakintaba
''YAYA Allah ina jin tsoro sosai.....YAYA yanzun na fito naji tana waya,amma bansan da wa suke magananba....Wallahi YAYA ita tasa aka sace KHUBRA''
Bakinta keta maimaitawa har sai da ta samu nutsuwa kafin wasu tambayoyin suka shiga tseren fitowa daga bakinta
''Yaushe?kuma a ina hakan ta faru? garin yaya?ita HAJIYA MURJA tana wane sakacin aka d'auke y'ar mutane?ko kuwa bata sani ba?''
Kallon UMMIN nasa ya shiga yi uwa wanda ya fara ganinta yau
''Wallahi UMMI abunda na manta ban tambayi KHALEED ba kenan......
Amma gaskiya UMMI ina zargin da sa hannun HAJIYANSA''
Ta gefe ya d'an kalleta yana mai rik'e bakinsa,tunawa da warning da tayi masa
''Amma kiyi hak'uri UMMI idan na fad'i abunda ba dai² ba''
Kai ta kad'a masa kafin cike da mamaki ta soma magana
''Tabbas ko ni da kaina jin wannan maganar yasamin zargin HAJIYA MURJA....Da gangan akayi......Ko tantama babu wannan aikin shiryashi akayi,akwai sa hannu cikinsa''
Shiru dukansu sukayi suna jinjina lamarin...
''Allah ya kyauta,Allah ka kare baiwarka a duk inda take''
Abunda ya iya fitowa daga bakinta kenan ta sake yin shiru tana jaddada al'amarin a zuciyarta....
《《》》
ZUHRA ce ta fito da kumburarren fuskanta zata kitchen danko k'ishi ke damunta,ta fito da niyyan d'auko ruwa,dai² zata wuce ta k'ofan MAMA ta ji ana magana k'asa²,kunnenta ta d'ora jikin k'ofan take ko kalaman da ta jiyo suka sake firgitata....
''Ehhh!ba damuwa HAJIYA LAURA ai kin gamamin komai da kika samomin mafita''
Dariya ta saki mai k'arfi kafin ta ci gaba
''Wallahi kuwa mun rabu da kaska.....Yo to ta inama za ayi wata Housemaid zata zo tana neman juyamin kai.......maza biyu lokaci guda fa duk sun haukace kanta,shi wancan da yafi kowa haukama harda turomin mahaifiyarsa bayan ga y'an mata nan ina da su bai zab'i kowacce ba sai ita........Uhmm!shi kuma KHALEED......Ai ki barni da su tunda yanzun munyi maganinsu.....Allah kuwa,to ameen...Sai kin jini''
Jin maganganun tayi suna mata yawo akai,kenan zarginta ya zama gaskiya kan MAMA,hawayene suka sake b'alle mata,dafe bakinta tayi tana jiyo maganar MAMA,daga jima ka san da kanta take
''Ya zama dole na raba gidan nan da duk wani abu da zai sake tunamin da ke......
Barima kiga na tashi kaf kayanki dake gidan nan k'onasu zanyi,mun dai rabu da kaska sai aje can a sha jinin wani''
Jin kalamanta na k'arshe yasa ZUHRA saurin mik'ewa hanyan fita daga parlor ta nufa tana tafe tana hard'ewa kamar za ta kifa,har ta fice daga parlorn...
Kansa ya had'e da steering motan ya shiga tunanin da bai san me yake tunawa ba,tsawon mintuna arba'in yana cikin motan ba tare da ya iya fitowa ba,kuma har lokacin ya kasa kashe motan...
Fitowan ZUHRA daga cikin parlor tana waigawa tana kallon hanya tamkar wacce wani abun tsoro ya biyo,shi kuma ya d'ago yana bud'e motan had'e da kashewa ya fice,tafiya yake jikinsa babu k'wari...
Buge juna suka yi da sauri ta d'ago ba tare da iya yin maganaba ta d'aga masa hannunta alamar ban hak'uri,tayi gaba abunta,tana kuma ci gaba da waiwayen hanya....
Kallonta kawai yayi,yanayin da take ciki ya tabbatar masa akwai damuwa,har zai shiga parlor ya fasa a baya ya bi hanyan da ta bi,har k'ofan d'akin..
A ciki ya tsintota tana ta faman binciken kayan dake d'akin,da k'yar ta iya gano keys en d'akin,kayan ta shiga d'iba tana zubawa a closet dake had'e cikin wall en d'akin.....
Yana tsaye bakin d'akin yana kallonta har ta kammala ta fito,da sauri ta maida k'ofan ta rufe had'e da danna mata key.....
Sai da ta juyo zata bar gurin sannan ta ganshi tsaye ya hard'e hannayensa a chest yana kallonta...
《《》》
Sai da ta gama kukan sannan ta mik'e ta karkad'e kayanta da suka b'aci da k'asa,zuciyarta cike da kishin kanta da tausayin rayuwarta ta sake d'ora hannunta a kan marik'in kuran....
Dannawa ta shiga yi,duk k'ok'arinta bai wuce taga ta taimaki kanta ba,addu'ah ta soma duk wacce tazo bakinta yi take kan neman taimako daga mahalicci,cikin ikon Allah tana ta k'ok'arin turawa bakinta kuma bai fasa ambaton Allah ba,tafiya kuran ya soma ta juyo da akalar kuran zuwa garin da suka bari yanzun....
Da k'yar take iya turawa,fuskanta zuwa jikinta duk yayi gumi kan wahalar da tasha na turo kuran,idan ta gaji ta tsaya ta huta haka taita fama har ta fara shigowa cikin garin....
Jama'a sai kallonta suke da mamaki yayin da wasu ke binta,ita kam ko a jikinta,dan ta d'aura aniyar neman halak enta,sana'a babu fashi yanzun ta soma duk abunda mutane za suyi babu ruwanta,za ta toshe kunnenta daga tsaigumin su,haka taita turawa tana wucewa,line ta soma bi d'aya bayan d'aya,wani line en idan ta shiga za ta tarar da shi cike da mutane y'an gulma wad'anda labari ya iske,ba maza ba mata,hatta da k'ananan yara binta suke duk inda tayi,ita ko ko a jikinta....
Ganin wannan sabon al'amari yasa mutane siyan ruwan ga wand'an dama basuyi niyyaba duk dan su shaida labarin da ya iske su,duk gidan da suka siya dai kaga wasu daga cikin y'ay'ansu maza suna saukewa suna shiga da shi,idan sun juye su bata kud'inta da jarkanta,haka zata k'ara gaba su kuma su bita da idanu...
Kafin wani lokaci babu komai cikin kuran nata duka ruwan an siye babu sauran,bakin wata bishiya ta zauna tana lissafa kud'in naira d'ari biyu #200 cif,hamdala tayiwa Allah kafin ta huta abunta,bakin kasuwa ta sake komawa ta nemi mai abinci a gurin,tunani ta tsaya yi to na nawama ya kamata ta siya ne?
Ta d'an jima tana yanke shawara,kan ta bayar duka ko a'a.....
Mik'awa tayi duka ba tare da ta tantance ko yayi yawa ko baiba...
Mai abincin ce ta kalleta da alamar mamaki tana fad'in
''Ke ko y'ar nan me za kiyi da abinci har na d'ari biyu,ai yayi miki yawa,ungo wannan''
Ta mik'o mata d'ari da hamshin,d'an murmushin k'arfin hali tayi ta karb'a tana mata godiya...
''A robber zan zuba miki ko kuwa a leda?na ga kamar bak'uwace ke ko?''
'Dan murmushin ta sake yi tana fad'in
''Eehh!ni bak'uwa ce''
''Allah sarki ai na ga alama tun zuwanki gurin nan''
Bata kuma magana ba ta karb'i abincintan a gefe ta samu guri ta zauna,ko rabi bata iya cinyewa ba ta mik'e tana dawowa matar da robber enta da sauran abincin ciki,kallon mamaki tayi mata kafin ta iya tambayarta
''Me ya faru kika dawo da shi haka?''
''Uhmm!babu komai wollah babata na k'oshi ne''
Kalmominta da ta kira matar da shi wato ''BABATA'' su suka sa matar yin k'wallar farin ciki,kasancewarta bata tab'a haihuwa ba,har Allah ya d'auki ran mijin nata,tun daga nan kuma bata kuma wani auren ba...
Ganin matar na hawaye ya sanyayawa KHUBRA jiki,haka taita kallonta uwa wata doluwa....
''Y'ar nan gidan wa kika zo a garin nan?''
Tambayar ta bawa KHUBRA mamaki,amma sai bata nuna ba
''Ban san kowa ba a garin nan,nima kawoni akayi nan''
Da mamaki matar ke kallon KHUBRAN tana fad'in
''Kawoki akayi kuma?''
Kai ta kad'a mata,mik'ewa tayi tana kad'e jikinta da niyyan barin gurin
''Yanzun ina kika nufa y'ata?''
''Zan wuce ne''
'Dan tunanin matar tayi da sauri kuma ta katse KHUBRA dake haramar barin gurin
''Y'ata idan za ki yarda kuma kin amince ba zan tab'a cutar da ke ba,kuma idan har kin d'aukeni uwa a gareki......
Zaki iya bina gidana mu zauna tare,kin ganni nan tsawon shekaru talatin da biyar da aurena Allah bai tab'a azurtani da d'aba,amma yau na farko kin kirani MAHAIFIYA wannan dalilin yasa naji ina k'aunarki,tabbas zan rik'eki a matsayin y'a,idan har kin amince''....
Ta k'arashe maganar ta tare da goge wani layin hawaye dake kan fuskanta....
'Dan tak'aitaccen murmushin yak'e tayi,kafin zuciyarta ta tuna mata abunda aka mata yanxun da ko awanni biyar ba ayiba....
Da sauri kuma wata zuciyar ta bata amsa da cewa
''Haba KHUBRA duniyar nanfa ba duka aka zama d'ayaba,ya kamata ki tuna yadda rayuwar ki ta faro,wasu na sonki wasu na k'inki,kada kiyi saurin yanke hukunci,kiyi addu'ah dan shi ne gatanki a rayuwa a kuma duniyarki''......
Siririyar ajiyar zuciya tayi,kafin ta furta
''Na amince BABATA amma da sharad'i''
Matar tana murna ta kalleta
''Koma wane irin sharad'ine na yarje miki fad'i kome kike so in sha Allah bazan gazaba''
''Dama ina so ne nace...... Baba don Allah kada ki hanani neman abunda zan rufawa kaina asiri,komai tsafta,k'azanta,k'ask'anci ko samu da sana'ar take d'auke da shi''....
Kallonta kawai matar tayi
''In sha Allah bazan hanaki ba.....
Amma wace irin sana'a ce wannan?''
''Ba wata sana'a bace illa *GARUWA.............''*
A d'an tsorace ta kalli KHUBRAN,ita ko sai murmushi take abunta,da fuskanta da har yanzun tak'i komawa dai²....
Gudun kada tayi magana akan sana'ar ta KHUBRAN tak'i amincewa da buk'atarta,yasa taja baki tayi shiru,tana nai fad'in
''To shi kenan Allah ya wuce mana gaba,yayi miki jagora''
KHUBRA ta amsa da ameen.....
''To yanzun dai da kin bari sai zuwa gobe ko dan mu tafi tare kinga kyaga gidan namu ko?''
Ta fad'a tana d'an murmushi,itama KHUBRAN murmushi tayi ta sake neman guri ta zauna,tana ta kallon mutane da keta zuwa siyan abinci,tana zaune har abincin ya k'are tas,tana kallo matar ta kammala had'a kayan al-majirai suka d'aukan mata kayan nan ta juyo tana kallon KHUBRA
''Taso mu tafi y'ata''
Babu musu ta shiga bin matar a baya suna tafe tana tura kuranta na ruwa har suka isko wani k'aramin gida,nan suka shiga suka nemi guri KHUBRA ta adana kuranta da niyyan gobe da wuri zata fita sana'anta.....
《《》》
Kallonta yayi duk ta wani birkice
''Me yake damunki SISNAH?''
Bata iya bashi amsaba,hannunsa kad'ai ta jaa zuwa guarding suna tafe tana waiwayawa tana kallon hanya,guri suka samu suka zauna sannan a d'an tsorace ta juyo
''YAYANAH wallahi ina jin tsoro kada wani abu ya samu KHUBRA......Duk abunda ya faru BB MAMA ta san komai kuma wollahi da hannuta komai da ya faru,MAMA ce sila......Dan Allah YAYANAH ka nemomin ita pleasee''
Ta k'arasa tana rintse idanunta....
Tashin hankalinsa k'aruwa yayi jin ta ambaci MAMA,amma ya akayi tasan da sa hannun MAMAN a ciki?Yama kansa tambayan.....
''Me yasa kikace da sa hannun MAMA?''
Ya mata tambaya yana mai jin fad'uwar gaba,dan bai san wane amsane zai fito daga bakintaba
''YAYA Allah ina jin tsoro sosai.....YAYA yanzun na fito naji tana waya,amma bansan da wa suke magananba....Wallahi YAYA ita tasa aka sace KHUBRA''