← Book details Yar Garuwa Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 71 OF 86

Sashe 71

Yar Garuwa Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Bata kuma magana ba,dan kam ba saita tambayaba,ta gane abunda take nufi,k'ulewa sukayi cikin d'akin tana koya mata wasu abubuwan a tunaninta KHUBRA bata san komai ba,ita ko kallonta kawai take,a zuciyarta fad'i take
"Y'ar uwata kenan ke a ganinki dan na rayu a k'auye babu abunda na sani..Amma kuwa idan har haka ne to da zamana a nan bai amfana min komai ba,ko dan banyi boko ba ai hakan ba yana nufin babu abunda na iyaba,duk wannan soyayyar ai akwaita cikin ilimin addini,kuma akwai littafin da ABBANAH yake karantamin,hasalima sai dai na koya miki wani abun..."
Tagumin da tayi ta zubawa ZUHRA ido,ita ZUHRA a tunaninta sauraronta take har ta k'are yi mata hud'ubar kwalliya dasa matsatstsun kaya wad'anda zasu jaa hankalinsa,tare suka shirya dinner su kuma su BB suna nan cikin parlour suna hiransu suma,har suka gama sannan KHUBRA ta wuce bed room inda tabar ZUHRA a gurinsu,wanka ta sake sannan ta shirya cikin short nicker iya cinyanta,da wani half vest,lafaya ta d'auko mai kauri ta nad'a sannan ta kama gashinta ta nad'e shi kamar yadda indiyawa suke yi yayi gammo,simple make-up tayi bakinta ya sha white lipgloss,sai k'yalli yake kamar an sanyashi cikin tandun mai,b'arin turare tayima jikinta sannan tayi juyi a gaban mirror,tana shirin fita ya shigo yana kiranta,tsaye yayi yana k'are mata kallo yadda ta koma masa kamar wata SONAM KAPOOR a cikin phrem rhatan dhan phayoo,hugging enta yayi ta baya suna tsaye gaban mirror en suna kallon juna ta ciki,a hankali ya juyo da ita suna fuskantar juna,hab'arta ya d'ago da hannunsa yana matso da fuskarsa dai² nata,cikin sauri ta dakatar da shi tana fad'in
"YAYANAH kasanfa ba mu kad'aine cikin gidanba..."
Idonsa ya runtse yana sakin wani gajeren tsaki,haushin su KHALEEL yake saboda zuwansu ya masa shamaki da kasancewa tare da ita,dariya take ta k'unshewa dan ta kula da yanayin da yake a ranar,kanta ta sunk'e tana yin k'asa da shi,hab'arta ya sake d'agowa yana fad'in
"Bazan hanaki dariyaba,dan dama d'azunma har tsokanata kikeba kuma a gaban idonsu ko..?"

Shiru tayi babu amsa sai idanunta da take juyawa tana kallonsa,wani killer smile ya saki yana fad'in
"Tunda babu amsa nima baran barki ki fita haka nanaba,musamman wannan lips en naki da kika laftawa mai...emmmm! wai ma da haka zaki fita ne...?"

Kallon rashin fahimta ta masa shi ko gira ya d'age mata,ita kuma ta kafe shi da ido tana jiran jin me zai fad'a,hannu yasa ya rufe mata ido a hankali ya had'e bakinsu guri guda,sai da ya tabbatar ya shanye lipgloss data sa tas,sannan yaja hannunta sukayi waje inda suka bar KHALEEL da ZUHRA na jiran fitowarsu,zaman da ZUHRA ke gyarawa ya tabbabtar da itama ba k'alau ba,d'an murmushi KHUBRA tayi tana d'auke kanta daga kansu ganin sai kame-kame ZUHRA'N keyi,haka dai suka gama dinner kafin sabon hira ya b'alle ZUHRA kam duk mamakin KHUBRA take yi,ganin yadda tayi shigan kamar indi'a a zuciyarta ko fad'i take
"Lallai CWEETY ina miki kallon babu abunda kika iya a b'angaren soyayya ashe kyace sai dai ni na koya...Dole mana BB ya haukace miki,mai mata irin wannan ai dole ko wane lokaci a samu gadon baccinsu a yamutse.."
Kallon agogo BB yake,dan tun d'azun shi yake ta kallo tun da akayi salla'n isha ganin babu maganar zasu tafi yasa ya fara magana fuska babu wani wadataccen fara'a
"Wai ku kam sai yaushe zaku tafi ne...?"

"Koranmu kuma za kayi ne..? ko kuwa dan mun zo gidan kane hakan..?"
Banza yayi masa babu amsa,dan kansa kuma KHALEEL en ya kalli ZUHRA yana fad'in
"HABEEBTEEY! Tashi mu tafi kinji tun yanzun an fara korarmu.."
Kamar mai jira ko yana rufe baki ta mik'e tana had'a kayanta,suna gamawa KHALEEL ya kalli BB
"To MAN! mu mun wuce tunda ka gaji da ganinmu.."

"Ehh! ko me zaka fad'a sai dai ka fad'a bani kuma da lokacinka yau kam.."
Murmushi KHALEEL yayi sannan ya kama hannun ZUHRA suka yi waje su kuma suna binsu a baya don rakasu.Sai da suka bar gidan sannan suka juyo da nufin komawa ciki,tafiyar da takeyi kamar bata so ne yaga ya masa tsayi janta yayi ta tsaya,kafin tayi magana ya rabata da k'asa,ko ba a fad'a mataba kam tasan nufinsa,hannayenta tasa ta zagaye wuyansa,kai tsaye bedroom ya wuce da ita yana sakin sanyayyar ajiyar zuciya dan kam tsawon kwana uku kenan ba tare da ya sake mata komai ba,yau kam ai sai yadda Allah yayi da ita dan ko ita da kanta ta tabbatar da haka,musamman yadda yake mata rawar k'afa tun safe,bare kuma yanzun da suke neman kad'aita da juna cikin d'aki d'aya shimfid'a kuma d'aya..................

*COMMENT FOR MORE PAGE'S........* 💃💃💃💃💃

*~#TEAM KHUBRA-KHALEED.~*

*_®єαl $mαѕhєr._* 😉
💠💠💠💠💠

*Y'AR GARUWA......*
*(ɬɧɛ mơʂɬ ɧɛąrɬ ɬơųcɧıŋɠ ʂɬơrყ).*

🕊🕊🕊🕊
🌹🌹🌹

*fαcєвσσk grσup:* https://www.facebook.com/groups/369678263526212/
SMASHER,HUBBEEY,DIDEEYLOV & GENTLE NOVEL'S [email protected]

*©®2018*
*5/ɑմցմՏԵ,2018*

*ʂɬơrყ ąŋɖ wrıɬɛɛŋ*
*ცყ*
_HAWWA M.U {$мaѕнer}_
🕊🕊🕊🕊🕊
🌹🌹🌹🌹

_BISMILLAHIR-RAHMANIR-RAHEEM..._
*~___________________________~*
_Congratulations for the compilation of your amazing,wonderful and romantic novel dear *AMINA UMAR FANA (AUFANA)* Allah yasa sak'onki ya isarma al'ummar da akayi dominsu,Allah kuma ya baki ikon fara na gaba lafiya.._
*~___________________________~*

*DEVOTED TO:*
_BILKISU M.ADAM (Y'AR ABBA)_

*BESTOWED TO:*
_MURJA SALIS (NA'IKKE)._

*AND*

_FATIMA ABUBAKAR (FATEEY AFIRST)._

5⃣9⃣

*S* aman bed ya kwantar da ita sannan a hankali ya shiga warware lafayan data nad'a kamar sarii har ya kammala ware shi tas daga jikinta,arba yayi da arnan kayan dake mak'ale jikinta sam tunaninsa bai kawo masa cewa zata iya sa irin wad'annan kayanba,wani murmushi ne ya sake escaping daga bakinsa,sosai kayan dake jikinta suka amsheta musamman da suka kasance dai-dai ita,d'an nickers en nata ya kalla wanda da kad'an yafi pant da kuma mitsitsiyar rigar jikita wacce yanayin kwanciyan da tayi yasa halittun jikinta bayyana ta dai² wuyan rigan,da k'arfi ya sauke ajiyan zuciya saboda kasancewar irin rakin data yita ta zuba masa cikin satin aurensu yasa ya d'aga mata k'afa har na tsawon kwanaki uku,k'ark'arinsa da ita idan sun gama shirin kwanciya ta shige jikinsa kamar mage,shi kuma haka zai rungumeta ba tare da yayi mata komaiba,sai dai yau kam baya jin zai iya hak'uri musammanma yadda ta yita kunno shi tun safe,dole ne yau kam ya sauke mata gajiyan kwana uku.Tafiyan tsutsa ya soma mata daga cikinta har zuwa dai² chest enta da suka riga suketa tsokane masa ido,tafiyan tsuntsan da yake mata yasa ta shiga mirgina kai gefe tana dariya wanda yasa ta rufe idanunta,dariyan shima yake dan da alama kam tana enjoying abunda yake mata,ci gaba yayi ba tare daya sauraraba har hannayensa suka samu daman shigewa ta k'asan ficilar riganta wacce da kad'an tafi bra,salon da yake gabatar mata a lokacin shiya dad'a hautsinata lokaci guda service enta ya harba,romantic kisses ya shiga aika mata tun daga tafin k'afarta har ya haura zuwa saman maranta,daga nan yaci gaba da yin sama har ya iso dai² inda yayima hannayensa matsuguni yana wasa dasu,ruwan kisses en da yake sakar mata yasa itama batayi k'asa a guiwaba ta biye masa saboda kasancewar a cikin y'an kwanakin kusan za a iya cewa indai ta wannan fannin ne BB ya rigada ya gama biya mata babin,wanda itama babu b'ata lokaci ta haddace har tana neman k'ari,cike da shauk'i suke kissing juna wanda ya dad'a hautsina musu tunani kafin wani lokaci tuni har sunyi watsi da kayan dake sanye jikinsu,rumfa yayi mata suna kuma ci gaba da aikawa junansu sak'onni masu girma,wanda a k'arshen wannan dare sai da KHUBRA ta gane girman bambanci na halittarsu,dan kam BB ko kad'an bai saurara mataba sai da yaji network ensa ya kawo full,sannan ya koma gefe yana rungume da ita suna maida numfashi.
Shi da kansa yakanyi mamakin dalilin da yasa ya koyi wannan jaraban bayan da ba haka yakeba musamman satinsu na farko da aure sam bai wani iya hak'uri,ko mene ne dalilin ohhoon masa,sai da suka gama maida numfashin wahala sannan yayi sama da ita sai toilet,cikin kumfan suka dad'a shantakewa ko tunanin dare yana ci gaba dayi basuyi ba,sai da suka shafe tsawon wani lokaci a ciki sannan daga bisani kuma sukayi abunda ya kaisu suka fito yana rungume da abarsa kamar baby'n robber.Bacci mai cike da shauk'i da kuma sukuni na kasancewarsu tare yayi gaba da su.

*A MONTH LEAP.*

A wata safiya bayan sun tashi kamar yadda suka saba suna manne da juna a haka suka had'a break fast,sun ciyar da junansu inda ya kasance fiye da rabin cin abincin nasu ya zama tsokana da haka dai suka kammala,sannan suka koma saman cuistion tana saman jikinsa cike da soyayya da kuma kulawa ya kalleta yana sakin mata k'ayataccen murmushinsa da ba kowa yake wa irinsaba,cikin k'asa da murya a dai² kunnenta ya furta
"JODI yau kam ina so muje gida mu gaisa dasu MAMA fa..."
Da sauri ta d'ago tana murmushi
"Allah YAYANAH....? kamar kuwa kasan dama ina son ganinsu inata kewarsu fa.."
Murmushi ya sake yi kafin ya d'aga mata kai cikin wani irin kallo mai wuyar fassara murya can k'asan mak'oshinsa ya furta
"Mene ne abun kewarsu bayan kina tare dani...Ko kuwa kinfi sonsu fiye dani...?"
Yatsanta ta d'ora kan lips ensa tana kad'a masa kai alamar a'a
"Haba YAYANAH taya zaka ce haka,bayan kaine gaba d'aya rayuwata...Bana jin a duniya kam idan har a b'angaren soyayya ne idan aka cire son ALLAH da MANZONSA (S.A.W) daya zama wajibi akansu,sannan ABBANAH bana jin bayan wannan akwai wanda zai zo bayan nan sama da kai....Idan baka manta bama ai na fad'a maka da soyayyarka na girma tun ban gama sanin kainaba har ya zamana na fahimci hakan.Kaga ko idan haka ne wannan kalmar sai dai tayi gefe dan bata kamaci mutum irinka ba."
Fuskarsa da matsanancin farin ciki yake kallonta kafin yayi magana yana kallon cikin eye ball enta
"JODI ni kam ina son sanin ta yaya akayi kika gane ni a matsayin *MUTUMIN MAFARKINKI* dan wancan labarin kin b'oyemin baki sanar dani ba..."
Murmushin itama tayi wanda ya bayyanar da hak'oranta cikin salon tsokana ta furta
"Da wad'annan idanun naka masu kama dana kyanwa..."
Sai da yayi dariya sosai sannan ya kalleta yana fad'in
"A haka kuma kika gani kika mace a soyayyar mai idanun kyanwar ba..."
Chapter 71 · 0% Book details