Sashe 25
Yar Garuwa Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Shiru yayi ya kasa magana kansa sai dad'a sarawa yake kan ciwon da yake masa vains en kansa duk sun gama bayyana a fili....
''Kuma YAYA ko ta ce sai ta k'ona duk wani abu da ya shafi KHUBRA shi yasa na rufe d'akintan......YAYA ansa key en ka adana ni kasan MAMA zata iya buguna amma dan Allah kada ka bari ta sani kaji BB nah''
Ta fad'a tana d'ora masa key en a hannunsa,da sauri ta mik'e ta bar gurin tana had'awa da gudu,har ta shige bed room enta basu had'u da kowaba,da sauri ta maida k'ofan ta rufe.....
A hankali ya mik'e yana tafiya,har bakin k'ofan bedroom en,key en ya sanya ya bud'e yana shiga ya maida k'ofan ya rufe yana mai locking enta ta ciki.....
Kan katifanta ya kwanta yana sauke ajiyan zuciya,yanayin d'akin kad'ai ya bashi nutsuwa ko ba komai k'amshinta da yayi remaiming ciki ya kwantar masa da hankali,yana haka wani bacci mai dad'i wanda ta jima rabon da yayi shi ya d'auke shi.....
《《》》
Cikin d'aki matar ta mata iso tana mata shimfid'a,a hankali ta shiga ta zauna tana ta kallon ko ina na d'akin,zama matar tayi tana fad'in
''Ohhhh!niko ko sunanki ban tambaya ba,ina can d'okin tahowa da ke''
A hankali ta furta ''Suna na KHUBRA''
''Allah sarki ni kinga suna na ZUWAIRA''
'Dan murmushi kawai KHUBRAN tayi sai dai tambayan matar ya sa fuskarta saurin rikid'ewa zuwa tsantsar tashin hankalii..........
*~#KEEP FOLLOWING FAN'S....~*
*Mu tara bayan sallah da yardar Allah,da fatan Allah ya karb'i ibadunmu,na barku lafiya,Allah ya sada mu da alkhairinsa....Ameen thumma ameen.*
*~UR'S & ONLY~*
*_REAL SMASHER._*
💠💠💠💠💠
*Y'AR GARUWA......*
*(ɬɧɛ mơʂɬ ɧɛąrɬ ɬơųcɧıŋɠ ʂɬơrყ).*
🕊🕊🕊🕊
🌹🌹🌹
*©®2018*
*19/ʝųŋɛ,2018*
*ʂɬơrყ ąŋɖ wrıɬɛɛŋ*
*ცყ*
_HAWWA M.U {$мaѕнer}_
🕊🕊🕊🕊🕊
🌹🌹🌹🌹
_BISMILLAHIR-RAHMANIR-RAHEEM..._
*~________________________~*
_Ina taya d'aukacin al'ummar musulmi na duniya murnan sallah da fatan ubangiji ya amshi ibadunmu ya kuma sanyamu cikin y'antattun bayinsa.....ameen._ 👏👏
*HAPPY EID-EL-FI'DR.*
*~________________________~*
*DEVOTED TO:*
_BILKISU M.ADAM (Y'AR ABBA)_
*BESTOWED TO:*
_MURJA SALIS (NA'IKKE)._
*AND*
_FATIMA ABUBAKAR (FATEEY AFIRST)._
*2⃣9⃣*
*"O* ohh! Ni ko na miki wata tambaya d'azun sai dai amsan da kika bani ya tsayamin a rai,na kasa fuskantar abunda kike nufi
"...
'Dan d'agowa tayi tana kallon matar saboda rashin fuskantar maganar ta new mother en nata..
Gane hakan da tayi shi yasa tayi d'an murmushin yak'e kafin ta furta
"A d'azun na miki tambaya kan gurin wa kika zo a garin nan,sai dai amsan da kika bani yasa nake son sanin me yasa aka sato ki kuma wane azzalumi ne ya aikata miki haka?"
Fuskanta cike da tashin hankali haka ta sunkuyar da kai k'asa,dan kam ta tabbata mai afkuwa na shirin faruwa,tunda matar ta soma tambayanta lallaine a k'arshe matar ta koretama gaba d'aya,wannan tunanin shi yasa ta dad'a sunkuyar da kanta k'asa gudun kada matar ta gane k'aryan da take shirin yankowa bata iya d'agowa ba,idanuntan nan sun dad'a fitowa kan tsoro da ya cika zuciyanta,duk da dai tasan ba wai laifinta ne yasa aka aikata mata hakanba...
Tana nan zaune tayi shiru amsa tambayan ya gagareta tana ta taradaddin sanar da BABA ZUWAIRA,ta tsinkayo muryanta tana fad'in
"Niko KHUBRA idan babu damuwa zan so sanin daga wane gari kika fito da kuma asalinki?"
Jin wannan tambayan yasa ta sauke ajiyan zuciya a tunaninta ta tsira daga wancan tambayan,shi yasama cikin k'warin gwuiwa ta bata amsan
"Daga KANO nake,BABATA dan Allah nan wane gari ne? ban san ina ne nan ba" KHUBRA ta fad'a yayin da wasu hawaye masu d'umi suka fara sakko mata,gefen hijab na jikinta ta kama tana gogewa,duk wani motsinta idon matar na kanta tana binta da kallon tausayi...
"Allah sarki nanma duk cikin kano kike ae sai dai nan muna daf da jihar jigawa,sunan wannan garin ZAKIRAI,amma cikin kano wani gari kike?"
Raba ido ta hau yi tana son tuno sunan unguwan da suke,tunani take ko zata iya tuno sunan unguwan da suke,amma ta kasa.....
Katseta BABA ZUWAIRA tayi da wata tambayan
"Ke kuwa mene ne ya faru dake da har wasu suka satoki daga gidanku kuma hannun iyayeki zuwa wannan gari,kuma me kika aikata musu da zafi har haka?"
Kukanta tayi k'ok'arin had'iyewa,kafin cikin nutsuwarta ta soma da fad'in
"Dan Allah MAMA kiyi hak'uri kuma ki yarda da ni,ko da na fad'a miki gaskiya baza ki koreni ba"...
'Dan tsagaitawa tayi ta d'ago kanta tana kallon new mother enta BABA ZUWAIRA..
Kai ta soma kad'a mata kafin ta bud'e baki cikn sanyin jiki ta furta "In sha Allah babu abunda zai faru,ke dai ina son ki fad'amin gaskiyarki,dan da ganinki bana tsammanin k'arya daga gareki,ina fatan kuma zaki d'aukeni matsayin mahaifiya ki sanar da ni komai"..
"In sha Allah" KHUBRA ta fad'a a zahiri,yayin da can k'asan zuciyarta take fad'in "kiyimin afuwa amma kam tabbas bazan iya sanar dake *SIRRIN RAYUWATA* ba",in sha Allah dana fad'a dama sai Allah ya baka iko,kuma k'arya wajen kare kai ta halatta,tana kaiwa nan ta datse tunanin had'e da sauke wata nannauyar ajiyar zuciya...
"Kamar yadda na sanar miki ni sunana KHADIJA amma mahaifina na kirana da KHUBRA,saboda kasancewar sunan mahaifiyarsa gare ni wannan dalilin yasa mutanema ke kirana da KHUBRA kamar yadda mahaifina ke kirana,mahaifiyata Allah yayi mata rasuwa tun ina jaririya"
Daga nan ta shiga bata labarin irin zamanta a gidansu ZUHRA,sai dai ta b'oye alak'arta da gidan da kuma irin zaman da take,hakama alak'arta da MA'U,LADIYO da ma k'auyensu,abunda ta iya sanar mata kad'ai kishiyar mamanta ce take son ta auri k'aninta ita kuma bata so,kan wannan dalilin ta d'ora mata karan tsana,tun daga ranar take zuga mahaifinta,ganin yak'i amincewa ne yasa tasa aka satota daga gidan wanda k'arshe suka yasar da ita a bakin kasuwar garin nan.....
Shiru tayi tana jan numfashi a hankali,kanta har lokacin yana k'asa saboda tunaninta tana d'agowa suka had'a ido matar zata gane k'arya ta mata..
"Allah sarki y'ata,in sha Allah da sannu duk mai hannu a ciki sai ya ga sakamako,amma mai zai hana na d'oraki a hanya ki koma gida,saboda kinga baki san halin da mahaifinki yake ciki ba".....
Cikin sauri KHUBRA ta katseta da muryar tausayi, "dan Allah BABATA kiyi hak'uri kada kuma ki ce nak'i bin shawararki,wallahi ina son sanin halin da mahaifina yake ciki,amma ina tsoron zuwa gida saboda ban san me zan je na tarar ba,ki kyale ni na zauna tare da ke har zuwa wani d'an lokaci,in sha Allah da kaina zan miki maganar tafiyata idan lokaci yayi" ta k'arasa tana goge fuskarta da hijab enta...
Yanayin yadda tayi maganar shi ya sanyayawa matar jiki,tausayin KHUBRAN duk ya lullub'e mata zuciya haka take ta bin KHUBRAN da kallon tausayi..
"Shi kenan babu komai KHUBRATA in Allah ya yarda zaki ci gaba da zama a nan,Allah yasa hakan ya zama alkhairi a garemu baki d'aya"
Tako amsa da ameen,wani sashe na zuciyanta yana farin ciki da amincewar da matar tayi....
《《》》
Daf da za a shiga masallaci ya farka har an idar da kiran sallan maghreb,da sauri ya mik'e ganin garin yayi duhu,agogon dake d'akin ya kalla,da mamaki a kan fuskansa cikin rashin gasgatawa ya nufi window yana mai d'aga cottains en aiko take ya gasgata abunda ya gani danko rana ta jima da fad'uwa,da sauri ya juya ya shige toilet en d'akin....
Cikin sauri ya idar da alwalan lokacin har an tayar da sallah a nan saman carfet ya kabbara sallah da yake yana iya jiyo masallacin kuma gudun kada ya rasa jam'i kafin ya fita...
After ya idar yayi nafila,nan ya zauna yana addu'ah..
Ko da ya idarma kasa fita yayi ya kishingid'a jikin katifan yana tunanin baccin da yayi cikin d'akin,yayi nisa cikin tunani ya jiyo ana jijjiga k'ofan a d'an zafafe ya mik'e saboda yadda ake bugun k'ofan kamar za a karyata,shifa yanzun baya son damuwa kamar yadda yake jin haushin kowa a gidan idan aka d'auke ZUHRA da damuwarsu take kusan iri d'aya...
Key en yasa ya bud'e k'ofan kamar an cillota ta shiga k'ok'ari fad'owa kansa cikin sauri ya kauce ta hanyar ja baya kad'an a kan hanyan,Allah ya taimaketa ta rik'e k'ofan bata kai ga fad'uwa k'asa ba,ganin tana k'ok'arin shigowa yasa ya tare hanyan,ta hanyar tsaiwa tsakiya...
'Dagowa tayi cikin fushi ta furta "KHALEED yaushe na fara wasa da kai da zaka tsayamin a hanya?.........Ammm!mene ma ya kawoka d'akin nan tukuna kana neman wani abune ciki?"
Kamar an dasa gini haka ya mata ko "A" bai furta mata ba,kuma yak'i barin gurin...
Hannunsa ta kamo da niyyar janyeshi daga gurin saboda a tunaninta zata iya,sai dai ko gizau baiba,ganin ta kasa yasa shi sakin wani murmushin yak'e mai sauti da yasata kallonsa....
Had'e fuska tayi alaman babu wasa..
"KHALEED kaa matsa a nan ko kuwa sai ranka ya b'aci dan yanzun zan baka mamaki?"
"Uhhhmmm!MAMA ai an gama bani mamaki duk duniya,abunda kika aikatama kad'ai ya isa ya gama bani mamaki,amma MAMA ki tuna idan kin aikata haka akan y'ar wani shin bakya tunanin naki y'ay'an? idan Allah ya tashi kamaki me zaki fad'a masa lokacin da kika tsinci kanki a gabansa a lokacin da kowacce gab'a ta jikinki sai ta bada shaida akan abunda ta aikata,MAMA ki tuna da lahirarki sannan ki tuna irin tanadin da kika yi mata''.......
"Kaiiiiiiiiii! dakata ni sa'arka ce da zakamin wa'azi?kada ka manta ni na haifeka ba kai ka haifeniba da zaka tsaya kana fad'an maganar da ranka yaso,kuma yanzun maza ka kauce ka bani hanya".....
Cikin tsawa da fusata take magana tana jifansa da wasu mugayen harara....
'Dan murmushi ya sake yi mai ciwo yana kallonta,shi kam yau yaga ikon Allah,gaskiyan ne bata so a fad'a mata kenan?.......
"Shi kenan MAMA duk abunda kikayi dai² ne,amma ki sani nasan duk wani shirinki akan KHUBRA da kika sa aka d'auke,sai dai hanzari ba guduba duk wani yunk'uri da za kiyi idanun jami'an tsaro na kanki,saboda haka babu laifi kiyi duk abunda kike ganin ya kamata"......
Mari ta d'aukeshi da shi da yayi saurin sashi yin shiru yana dafe da gefen fuskansa da ido ya bita,lokacin ita kuma ta juya ta bar gurin cikin sauri.....
Wani murmushin ya sake yi,kafin ya juya ya kulle k'ofan yana mai barin gurin shima,zuciyansa duk ta cushe da tunani....
《《》》
''Kuma YAYA ko ta ce sai ta k'ona duk wani abu da ya shafi KHUBRA shi yasa na rufe d'akintan......YAYA ansa key en ka adana ni kasan MAMA zata iya buguna amma dan Allah kada ka bari ta sani kaji BB nah''
Ta fad'a tana d'ora masa key en a hannunsa,da sauri ta mik'e ta bar gurin tana had'awa da gudu,har ta shige bed room enta basu had'u da kowaba,da sauri ta maida k'ofan ta rufe.....
A hankali ya mik'e yana tafiya,har bakin k'ofan bedroom en,key en ya sanya ya bud'e yana shiga ya maida k'ofan ya rufe yana mai locking enta ta ciki.....
Kan katifanta ya kwanta yana sauke ajiyan zuciya,yanayin d'akin kad'ai ya bashi nutsuwa ko ba komai k'amshinta da yayi remaiming ciki ya kwantar masa da hankali,yana haka wani bacci mai dad'i wanda ta jima rabon da yayi shi ya d'auke shi.....
《《》》
Cikin d'aki matar ta mata iso tana mata shimfid'a,a hankali ta shiga ta zauna tana ta kallon ko ina na d'akin,zama matar tayi tana fad'in
''Ohhhh!niko ko sunanki ban tambaya ba,ina can d'okin tahowa da ke''
A hankali ta furta ''Suna na KHUBRA''
''Allah sarki ni kinga suna na ZUWAIRA''
'Dan murmushi kawai KHUBRAN tayi sai dai tambayan matar ya sa fuskarta saurin rikid'ewa zuwa tsantsar tashin hankalii..........
*~#KEEP FOLLOWING FAN'S....~*
*Mu tara bayan sallah da yardar Allah,da fatan Allah ya karb'i ibadunmu,na barku lafiya,Allah ya sada mu da alkhairinsa....Ameen thumma ameen.*
*~UR'S & ONLY~*
*_REAL SMASHER._*
💠💠💠💠💠
*Y'AR GARUWA......*
*(ɬɧɛ mơʂɬ ɧɛąrɬ ɬơųcɧıŋɠ ʂɬơrყ).*
🕊🕊🕊🕊
🌹🌹🌹
*©®2018*
*19/ʝųŋɛ,2018*
*ʂɬơrყ ąŋɖ wrıɬɛɛŋ*
*ცყ*
_HAWWA M.U {$мaѕнer}_
🕊🕊🕊🕊🕊
🌹🌹🌹🌹
_BISMILLAHIR-RAHMANIR-RAHEEM..._
*~________________________~*
_Ina taya d'aukacin al'ummar musulmi na duniya murnan sallah da fatan ubangiji ya amshi ibadunmu ya kuma sanyamu cikin y'antattun bayinsa.....ameen._ 👏👏
*HAPPY EID-EL-FI'DR.*
*~________________________~*
*DEVOTED TO:*
_BILKISU M.ADAM (Y'AR ABBA)_
*BESTOWED TO:*
_MURJA SALIS (NA'IKKE)._
*AND*
_FATIMA ABUBAKAR (FATEEY AFIRST)._
*2⃣9⃣*
*"O* ohh! Ni ko na miki wata tambaya d'azun sai dai amsan da kika bani ya tsayamin a rai,na kasa fuskantar abunda kike nufi
"...
'Dan d'agowa tayi tana kallon matar saboda rashin fuskantar maganar ta new mother en nata..
Gane hakan da tayi shi yasa tayi d'an murmushin yak'e kafin ta furta
"A d'azun na miki tambaya kan gurin wa kika zo a garin nan,sai dai amsan da kika bani yasa nake son sanin me yasa aka sato ki kuma wane azzalumi ne ya aikata miki haka?"
Fuskanta cike da tashin hankali haka ta sunkuyar da kai k'asa,dan kam ta tabbata mai afkuwa na shirin faruwa,tunda matar ta soma tambayanta lallaine a k'arshe matar ta koretama gaba d'aya,wannan tunanin shi yasa ta dad'a sunkuyar da kanta k'asa gudun kada matar ta gane k'aryan da take shirin yankowa bata iya d'agowa ba,idanuntan nan sun dad'a fitowa kan tsoro da ya cika zuciyanta,duk da dai tasan ba wai laifinta ne yasa aka aikata mata hakanba...
Tana nan zaune tayi shiru amsa tambayan ya gagareta tana ta taradaddin sanar da BABA ZUWAIRA,ta tsinkayo muryanta tana fad'in
"Niko KHUBRA idan babu damuwa zan so sanin daga wane gari kika fito da kuma asalinki?"
Jin wannan tambayan yasa ta sauke ajiyan zuciya a tunaninta ta tsira daga wancan tambayan,shi yasama cikin k'warin gwuiwa ta bata amsan
"Daga KANO nake,BABATA dan Allah nan wane gari ne? ban san ina ne nan ba" KHUBRA ta fad'a yayin da wasu hawaye masu d'umi suka fara sakko mata,gefen hijab na jikinta ta kama tana gogewa,duk wani motsinta idon matar na kanta tana binta da kallon tausayi...
"Allah sarki nanma duk cikin kano kike ae sai dai nan muna daf da jihar jigawa,sunan wannan garin ZAKIRAI,amma cikin kano wani gari kike?"
Raba ido ta hau yi tana son tuno sunan unguwan da suke,tunani take ko zata iya tuno sunan unguwan da suke,amma ta kasa.....
Katseta BABA ZUWAIRA tayi da wata tambayan
"Ke kuwa mene ne ya faru dake da har wasu suka satoki daga gidanku kuma hannun iyayeki zuwa wannan gari,kuma me kika aikata musu da zafi har haka?"
Kukanta tayi k'ok'arin had'iyewa,kafin cikin nutsuwarta ta soma da fad'in
"Dan Allah MAMA kiyi hak'uri kuma ki yarda da ni,ko da na fad'a miki gaskiya baza ki koreni ba"...
'Dan tsagaitawa tayi ta d'ago kanta tana kallon new mother enta BABA ZUWAIRA..
Kai ta soma kad'a mata kafin ta bud'e baki cikn sanyin jiki ta furta "In sha Allah babu abunda zai faru,ke dai ina son ki fad'amin gaskiyarki,dan da ganinki bana tsammanin k'arya daga gareki,ina fatan kuma zaki d'aukeni matsayin mahaifiya ki sanar da ni komai"..
"In sha Allah" KHUBRA ta fad'a a zahiri,yayin da can k'asan zuciyarta take fad'in "kiyimin afuwa amma kam tabbas bazan iya sanar dake *SIRRIN RAYUWATA* ba",in sha Allah dana fad'a dama sai Allah ya baka iko,kuma k'arya wajen kare kai ta halatta,tana kaiwa nan ta datse tunanin had'e da sauke wata nannauyar ajiyar zuciya...
"Kamar yadda na sanar miki ni sunana KHADIJA amma mahaifina na kirana da KHUBRA,saboda kasancewar sunan mahaifiyarsa gare ni wannan dalilin yasa mutanema ke kirana da KHUBRA kamar yadda mahaifina ke kirana,mahaifiyata Allah yayi mata rasuwa tun ina jaririya"
Daga nan ta shiga bata labarin irin zamanta a gidansu ZUHRA,sai dai ta b'oye alak'arta da gidan da kuma irin zaman da take,hakama alak'arta da MA'U,LADIYO da ma k'auyensu,abunda ta iya sanar mata kad'ai kishiyar mamanta ce take son ta auri k'aninta ita kuma bata so,kan wannan dalilin ta d'ora mata karan tsana,tun daga ranar take zuga mahaifinta,ganin yak'i amincewa ne yasa tasa aka satota daga gidan wanda k'arshe suka yasar da ita a bakin kasuwar garin nan.....
Shiru tayi tana jan numfashi a hankali,kanta har lokacin yana k'asa saboda tunaninta tana d'agowa suka had'a ido matar zata gane k'arya ta mata..
"Allah sarki y'ata,in sha Allah da sannu duk mai hannu a ciki sai ya ga sakamako,amma mai zai hana na d'oraki a hanya ki koma gida,saboda kinga baki san halin da mahaifinki yake ciki ba".....
Cikin sauri KHUBRA ta katseta da muryar tausayi, "dan Allah BABATA kiyi hak'uri kada kuma ki ce nak'i bin shawararki,wallahi ina son sanin halin da mahaifina yake ciki,amma ina tsoron zuwa gida saboda ban san me zan je na tarar ba,ki kyale ni na zauna tare da ke har zuwa wani d'an lokaci,in sha Allah da kaina zan miki maganar tafiyata idan lokaci yayi" ta k'arasa tana goge fuskarta da hijab enta...
Yanayin yadda tayi maganar shi ya sanyayawa matar jiki,tausayin KHUBRAN duk ya lullub'e mata zuciya haka take ta bin KHUBRAN da kallon tausayi..
"Shi kenan babu komai KHUBRATA in Allah ya yarda zaki ci gaba da zama a nan,Allah yasa hakan ya zama alkhairi a garemu baki d'aya"
Tako amsa da ameen,wani sashe na zuciyanta yana farin ciki da amincewar da matar tayi....
《《》》
Daf da za a shiga masallaci ya farka har an idar da kiran sallan maghreb,da sauri ya mik'e ganin garin yayi duhu,agogon dake d'akin ya kalla,da mamaki a kan fuskansa cikin rashin gasgatawa ya nufi window yana mai d'aga cottains en aiko take ya gasgata abunda ya gani danko rana ta jima da fad'uwa,da sauri ya juya ya shige toilet en d'akin....
Cikin sauri ya idar da alwalan lokacin har an tayar da sallah a nan saman carfet ya kabbara sallah da yake yana iya jiyo masallacin kuma gudun kada ya rasa jam'i kafin ya fita...
After ya idar yayi nafila,nan ya zauna yana addu'ah..
Ko da ya idarma kasa fita yayi ya kishingid'a jikin katifan yana tunanin baccin da yayi cikin d'akin,yayi nisa cikin tunani ya jiyo ana jijjiga k'ofan a d'an zafafe ya mik'e saboda yadda ake bugun k'ofan kamar za a karyata,shifa yanzun baya son damuwa kamar yadda yake jin haushin kowa a gidan idan aka d'auke ZUHRA da damuwarsu take kusan iri d'aya...
Key en yasa ya bud'e k'ofan kamar an cillota ta shiga k'ok'ari fad'owa kansa cikin sauri ya kauce ta hanyar ja baya kad'an a kan hanyan,Allah ya taimaketa ta rik'e k'ofan bata kai ga fad'uwa k'asa ba,ganin tana k'ok'arin shigowa yasa ya tare hanyan,ta hanyar tsaiwa tsakiya...
'Dagowa tayi cikin fushi ta furta "KHALEED yaushe na fara wasa da kai da zaka tsayamin a hanya?.........Ammm!mene ma ya kawoka d'akin nan tukuna kana neman wani abune ciki?"
Kamar an dasa gini haka ya mata ko "A" bai furta mata ba,kuma yak'i barin gurin...
Hannunsa ta kamo da niyyar janyeshi daga gurin saboda a tunaninta zata iya,sai dai ko gizau baiba,ganin ta kasa yasa shi sakin wani murmushin yak'e mai sauti da yasata kallonsa....
Had'e fuska tayi alaman babu wasa..
"KHALEED kaa matsa a nan ko kuwa sai ranka ya b'aci dan yanzun zan baka mamaki?"
"Uhhhmmm!MAMA ai an gama bani mamaki duk duniya,abunda kika aikatama kad'ai ya isa ya gama bani mamaki,amma MAMA ki tuna idan kin aikata haka akan y'ar wani shin bakya tunanin naki y'ay'an? idan Allah ya tashi kamaki me zaki fad'a masa lokacin da kika tsinci kanki a gabansa a lokacin da kowacce gab'a ta jikinki sai ta bada shaida akan abunda ta aikata,MAMA ki tuna da lahirarki sannan ki tuna irin tanadin da kika yi mata''.......
"Kaiiiiiiiiii! dakata ni sa'arka ce da zakamin wa'azi?kada ka manta ni na haifeka ba kai ka haifeniba da zaka tsaya kana fad'an maganar da ranka yaso,kuma yanzun maza ka kauce ka bani hanya".....
Cikin tsawa da fusata take magana tana jifansa da wasu mugayen harara....
'Dan murmushi ya sake yi mai ciwo yana kallonta,shi kam yau yaga ikon Allah,gaskiyan ne bata so a fad'a mata kenan?.......
"Shi kenan MAMA duk abunda kikayi dai² ne,amma ki sani nasan duk wani shirinki akan KHUBRA da kika sa aka d'auke,sai dai hanzari ba guduba duk wani yunk'uri da za kiyi idanun jami'an tsaro na kanki,saboda haka babu laifi kiyi duk abunda kike ganin ya kamata"......
Mari ta d'aukeshi da shi da yayi saurin sashi yin shiru yana dafe da gefen fuskansa da ido ya bita,lokacin ita kuma ta juya ta bar gurin cikin sauri.....
Wani murmushin ya sake yi,kafin ya juya ya kulle k'ofan yana mai barin gurin shima,zuciyansa duk ta cushe da tunani....
《《》》