Sashe 39
Yar Garuwa Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
*T* ana daga gefen titin tana ci gaba da tafiyanta wanda jin k'aran motan da tayi baisa tayi yunk'urin tsayawaba saima ci gaba da tayi kamar ta samu sak'on k'in tsayawar.
Yanayin yanda garin yake ne ya bata damar k'ara sauri saboda wasu irin thunderstorm da ke tashi akai-akai.
Tsayawan da motan yayi a dai² lokacin hakan ya farune sakamakon motan dake fidda hayak'i bayaga engine en motan da ya d'auki zafi,fitowa suka yi suka bud'e gaban motan ko dan su samu hayak'in ya sarara,wannan dalilin shi yaja musu tilas suka tsaya a gefen hanya'n.
Bayan motan suka duba cikin irin galan da masu mota ke zuba ruwa saboda gudun ko ta kwana irin wannan a tafiya.
Shiru sukayi suna kallon juna,saboda rashin ruwan a tare da su sannan suka kuma maida hankalinsu kan hanya'n da yarinyan nan tabi,can nesa dasu sosai suka hangota dan kam tsakaninsu da ita da tazara mai nisa.
"MAN wai ya zamuyi ne kam kanafa kallon yadda garin nan yake dad'a had'ewafa kuma ka tsaya anan kana wani kallona"
Harara BB ya bankawa KHALEEL dake magana,yanayin yadda yayi masa ne yasa shi shek'ewa da dariya,sai da yayi mai isarsa sannan ya kama hanya cikin sauri don tsayar da ita tun kafin ta b'acewa ganinsu.
Cikin sauri yake bin bayanta wanda da k'yar ya samu ya isa bayanta a dai² lokacin da take k'ok'arin karkatawa ta shiga hanyan da zai sadata da cikin gari.
Sallama yayi mata yana daga bayanta dan yasan hakan dai shi ne kad'ai abunda zaisa ta tsaya.
Cikin sa'a kuwa ya samu ya tsaya tare da juyowa don ganin waye ne mai maganar duk da tasan hanyan babu mutane sosai,duba da yanayin da aka tashi da shi a garin.
Idanu KHUBRA ta bud'e sosai ganin fuskar dake tsaye gabanta,tunani ta d'an tsaya yi kanta d'age a sama tana son tuna inda tasan fuskansa.
Magana yake yi wanda sam ta kasa bashi amsa saboda yadda ta lula duniyar tunani,har sai da yayi magana da d'an k'arfi sannan tayi firigigit da dawo duniyar da take tare da fad'in
"Ammm!kace mene?"
Shiru yayi yad'an tsaya yana binta da kallon mamaki da kuma tunanin inda yasan mai wannan muryan,kallo sosai ya k'ureta da shi sai dai bai gano komai kan fuskartaba,dalilin daya katse shi kenan daga tunanin da yake.
Yana shirin yin magana BB ya iso gurin yana fad'in
"MAN lafiya ka zo ka zauna ka wani shanyani a jeji bayan kana ganin yadda garin yake"
Shiru yayi lokacin da ya k'araso ya gansu tsaye suna kallon-kallo tsakanin su.
Kallonsu yayi sun kafe juna da ido,a hankali KHUBRA ta maida kallonta kan BB da isowarsa gurin kenan,dad'a fiddo idonta waje tayi da sauri kuma ta maida kanta k'asa had'e da dafe chest enta jin yadda zuciyanta keta skipping kamar zai fito waje.
Tun daga sama har zuwa k'asa BB yake kallonta a zuciyarsa yake magana
"Ina nasan mai wannan kamannin?anya ko itance ko kuwa mafarkine nake yi?"
Sake kallonta yayi da yadda take tsaye jikinta na vibrating da gani kasan akwai abunda ya bata tsoro wanda yasa ta shiga yanayi irin na rashin gaskiya haka,da sauri ya katse shirun ta hanyar magana da ya sasu kallonsa
"Ammm!baiwar Allah taimako muke buk'ata"
Ba tare da ta kalleshiba ta furta
"Taimako akan me kenan?"
Sake kallonta yayi yanzun kam ya samu shaida ta biyu da take bayyana masa hasashen da yake yi akanta,abu d'aya yake nema don tabbatar da gaskiyar lamarin.
"Muna buk'atar ruwane zamu sa a mota,mun d'an samu matsala ne so motan yana can kan hanya"
Har lokacin duk maganar da yake yi yana yine idanunsa na kanta,yayin da ita kuma duk take jinta a takure saboda yadda take jin idanunsu a kanta.
KHALEEL ya koma kamar wani idol yayi shiru yana sauraren muryanta dake masa yawo cikin kansa,so yake ya tuna inda yasan wannan muryan,yayin da a b'angaren BB shima hakan take dan shi kam gani yake a yanzun yana da yak'inin itance da kashi 50%,babban abunda yasa bai gama amincewa da itanceba ganin yadda wannan take b'aka,ga yanayin suturan dake jikinta sannan ya tsinceta cikin yanayin da baya tunanin KHUBRA zata shiga.
Duk sunyi shiru har sai da yayi k'arfin hali tare da danne zuciyarsa kan lallaifa wannan ba waccan KHUBRA'N da suke tsammani bace,kawai dai yanayin halittane da kuma su d'in da suke cikin yanayi na rud'u yasa suke ganin kamar itan ce da gaske.
Kautar da tunanin yayi tare da fad'in
"Amm!ina fatan dai ba zaki damuba dan da d'an tafiya tsakanin nan da gurin da mukayi parking"
"A'a babu komai,muje kawai"
Ta fad'a tana juya akalar kuran nata da niyyan komawa bayan garin inda suka bar motan nasu.
A baya suka shiga binta tana tura kuran nata,duk wani motsi nata akan idanunsa hakan yake yana ankare da ita,suna tsaka da tafiyan ne wata matashiya ta taho kanta d'auke da robber yellow da alama daga rafi take ta gansu suna tafiya,kallon mamaki tabisu da shi kafin tayi magana
"A'a KHUBRA ina kuma zaki nufa haka bayan kin d'ebo ruwan kike k'ok'arin komawa"
Cak!KHUBRA ta tsaya a gurin kamar anyi pausing enta ba tare da ta k'ara one step forward ba.
"Shi kenan HAFSAT kin tonamin asiri,wayyyo Allah ka kawomin d'auki"
Abunda ta furta kenan k'asa-k'asa idanunta a runtse ba tare da tayi tsammanin wani cikinsu zaiji me ta fad'aba.
A hankali ya furta
"ALHAMDULILLAH ALAA KULLI HALIN!
ALHAMDULILLAHIL-LAZIIY BI NI'IMATIHI TATIMMUS-SALIHAT!!!"
Yanzun kam ya gama samun shaidan da ya bayyana masa itan ce dai wacce yake hasashe d'ari bisa d'ari yanzun ya tabbatar da hakan.
"Amma to ya akayi ta koma haka ne kam?"
Yayima kansa tambayan ba tare da tunanin samun amsa daga gare shiba.
Matsawa yayi a hankali ya d'auke hat en dake kanta tare da sake k'ureta da kallo,ko tantama baya yi yanzun kam daya ga fuskarta ya gama yin amanna akan yak'ininsa gaskiya ne.
"Why KHUBRA zaki nuna baki ganemuba a yanzun?me yasa?me yasa za kiyi haka??"
Cike da tsawa ya k'arashe maganar tasa.
Kuka ne ya kufce mata wanda daga ji kasan mai yinsa cike yake da fargaba da kuma tsoron halin da take ciki,ta jima tana kukan wanda su dake tsaye gurin suka kasa magana sai kallonta kawai da suke yi,ganin bata da niyyan dainawane yasa KHALEEL yin magana
"Ina tunanin yanzu kam ba kuka ne abunda ya kamata kiyi ba,godiya ya kamata kiyiwa Allah da yayi sanadiyyar had'uwarmu,kafin mu wuce gida kuma"
"A'aaaa!! babu inda zani........ni kam babu inda zani........bazan biku ko inaba.........kawai kuyi tafiyanku ku k'yaleni a nan.........bazan biku ba!"
Ta fad'a lokacin da kukanta ya dad'a tsananta,tana ta kuka mai tsuma zuciya.
HAFSAT dake tsaye har lokacin duk abunda ya faru akan idonta,duk wani furucinsu da maganganunsu ya tabbatar mata da akwai wata alak'a tsakanin wad'annan samari da *KHUBRA Y'AR GARUWA* ,cillli tayi da robber dake kanta take ta felle k'afafunta ta yanki hanya sai cikin gari,gudu take shek'awa wanda ba ita ta tsaya ba sai gaban BABA ZUWAIRA dake ta hada-hadar sallamar customer's,cike da haki take maganaa
"BABA kiyi sauri ga KHUBRA can a bayan gari da wasu samari sai kuka take yi kuma"
Ambaton sunan KHUBRA da tayi shi ya dakatar da ita daga abunda take yi ta mik'e tsaye cikin firgici dafe chest enta
"Y'ar nan maza sanar da ni inda kika ganta tun kafin wani abu ya sameta"
Cike da rud'ewa take musamman jin ance KHUBRA'N tana kuka shi ne babban tashin hankalinta saboda tunanin BABA ZUWAIRA a wannan halin samarin tareta sukayi zasu mata "FYA'DE".
HAFSAT a gaba BABA ZUWAIRA a bayanta yayinda tayi k'wallo da kayan abincin ta marawa HAFSA'N baya sunata faman fakaka sauri kamar wad'anda zasu tashi sama..
Kukanta take tuk'uru yayin da ta kuma jajirce kai da fata ba inda zata bisu itakam,suna tsaka da wannan tak'addamar su BABA ZUWAIRA suka iso gurin,har kuma lokacin ta kasa yin shiru daga kukan da take yi.
"Y'ar nan ina fatan kina lafiya"
BABA ZUWAIRA ta fad'a tana shafa jikin KHUBRA'N dake tsaye.
Da sauri KHUBRA ta k'ank'ameta tana sake sakin kuka
"Ni bazan bisuba,a nan zan ci gaba da zama gurinki"
Maganarta ta d'aurewa BABA ZUWAIRA kai cike da mamaki ta d'agota suna kallon juna ta kuma furta
"Yi shiru ki sanar da ni,ina ne baza ki bisu ba?"
"Gida zasu maida ni,ni kuma ba zan bisu ba,ni gaskiya a nan zan ci gaba da zama gurinki"
Kallonsu tayi d'aya bayan d'aya,sai yanzun ta soma d'aukan haske game da lamarin nasu da kuma inda maganar KHUBRAN ta nufa,cike da jin dad'in Allah ya kawowa y'ar tata k'arshen wannan rayuwar k'uncin take fad'in
"ALHAMDULILLAH!Lallai Allah shi ne abun godiya a kowane irin yanayi,Allah ya amshi rok'onmu da addu'o'inmu da muka jima munayi,Allah mun gode maka"
Idanunta d'auke da k'wallar farin ciki take ta magana,kafin talli KHUBRA
"Bai kamata muci gaba da tsaiwa a nanba,muje gida tukun sai muyi magana ina ganin hakan zaifi"
Fuskarta d'auke da wani irin expression da ba zai fassaruba suka mik'i hanya da niyyan komawa cikin gari,inda KHALEEL yayi saurin zuba ruwa a motan ya biyo bayansu dan su kam har sunyi gaba basu tsaya jiran shiga motaba....
《《》》
Shigowanta gidan kenan daga hospital,shima daga dukkan alamu ta dawone dan yin wasu uzurorin kafin ta koma.
Wayanta ne ya shiga kuka a parlor saboda nan ta ajiye hand bag en da ta shigo da shi yanzun,tana shirin shiga kitchen kasancewar gidan babu kowa duk yaran sun tafi skul saboda yau en ta kama monday ne shi yasa take ta komai cikin sauri duk dan ta kammala kafin dawowarsu.
Kukan wayan da ta jiyo shi ya fito da ita daga kitchen en cikin sauri ta d'auka dai² lokacin da kiran ya zama missed,d'an janye key en tayi sannan ta duba number da aka kiratan da shi,kafin tayi wani yunk'uri wani kiran ya sake shigowa cikin sauri ta d'auka
"Assalamu alaikum!SON mutanen DUTSE ince dai ba cewa za kayi kuna hanya ba ko?"
Sai da yayi wani murmushi mai cike da sauti wanda yake nuna yana tattare sa tsantsar farin ciki sannan ya amsa mata
"UMMINAH barka da safiya da fatan duk kuna lafiya"
"Lafiya k'alau muke SON ya mutanen gidan?"
"Wallahi suna lafiya UMMI duk suna gaidaku"
"Muna amsawa kun samesu lafiya dai ko?"
Yanayin yanda garin yake ne ya bata damar k'ara sauri saboda wasu irin thunderstorm da ke tashi akai-akai.
Tsayawan da motan yayi a dai² lokacin hakan ya farune sakamakon motan dake fidda hayak'i bayaga engine en motan da ya d'auki zafi,fitowa suka yi suka bud'e gaban motan ko dan su samu hayak'in ya sarara,wannan dalilin shi yaja musu tilas suka tsaya a gefen hanya'n.
Bayan motan suka duba cikin irin galan da masu mota ke zuba ruwa saboda gudun ko ta kwana irin wannan a tafiya.
Shiru sukayi suna kallon juna,saboda rashin ruwan a tare da su sannan suka kuma maida hankalinsu kan hanya'n da yarinyan nan tabi,can nesa dasu sosai suka hangota dan kam tsakaninsu da ita da tazara mai nisa.
"MAN wai ya zamuyi ne kam kanafa kallon yadda garin nan yake dad'a had'ewafa kuma ka tsaya anan kana wani kallona"
Harara BB ya bankawa KHALEEL dake magana,yanayin yadda yayi masa ne yasa shi shek'ewa da dariya,sai da yayi mai isarsa sannan ya kama hanya cikin sauri don tsayar da ita tun kafin ta b'acewa ganinsu.
Cikin sauri yake bin bayanta wanda da k'yar ya samu ya isa bayanta a dai² lokacin da take k'ok'arin karkatawa ta shiga hanyan da zai sadata da cikin gari.
Sallama yayi mata yana daga bayanta dan yasan hakan dai shi ne kad'ai abunda zaisa ta tsaya.
Cikin sa'a kuwa ya samu ya tsaya tare da juyowa don ganin waye ne mai maganar duk da tasan hanyan babu mutane sosai,duba da yanayin da aka tashi da shi a garin.
Idanu KHUBRA ta bud'e sosai ganin fuskar dake tsaye gabanta,tunani ta d'an tsaya yi kanta d'age a sama tana son tuna inda tasan fuskansa.
Magana yake yi wanda sam ta kasa bashi amsa saboda yadda ta lula duniyar tunani,har sai da yayi magana da d'an k'arfi sannan tayi firigigit da dawo duniyar da take tare da fad'in
"Ammm!kace mene?"
Shiru yayi yad'an tsaya yana binta da kallon mamaki da kuma tunanin inda yasan mai wannan muryan,kallo sosai ya k'ureta da shi sai dai bai gano komai kan fuskartaba,dalilin daya katse shi kenan daga tunanin da yake.
Yana shirin yin magana BB ya iso gurin yana fad'in
"MAN lafiya ka zo ka zauna ka wani shanyani a jeji bayan kana ganin yadda garin yake"
Shiru yayi lokacin da ya k'araso ya gansu tsaye suna kallon-kallo tsakanin su.
Kallonsu yayi sun kafe juna da ido,a hankali KHUBRA ta maida kallonta kan BB da isowarsa gurin kenan,dad'a fiddo idonta waje tayi da sauri kuma ta maida kanta k'asa had'e da dafe chest enta jin yadda zuciyanta keta skipping kamar zai fito waje.
Tun daga sama har zuwa k'asa BB yake kallonta a zuciyarsa yake magana
"Ina nasan mai wannan kamannin?anya ko itance ko kuwa mafarkine nake yi?"
Sake kallonta yayi da yadda take tsaye jikinta na vibrating da gani kasan akwai abunda ya bata tsoro wanda yasa ta shiga yanayi irin na rashin gaskiya haka,da sauri ya katse shirun ta hanyar magana da ya sasu kallonsa
"Ammm!baiwar Allah taimako muke buk'ata"
Ba tare da ta kalleshiba ta furta
"Taimako akan me kenan?"
Sake kallonta yayi yanzun kam ya samu shaida ta biyu da take bayyana masa hasashen da yake yi akanta,abu d'aya yake nema don tabbatar da gaskiyar lamarin.
"Muna buk'atar ruwane zamu sa a mota,mun d'an samu matsala ne so motan yana can kan hanya"
Har lokacin duk maganar da yake yi yana yine idanunsa na kanta,yayin da ita kuma duk take jinta a takure saboda yadda take jin idanunsu a kanta.
KHALEEL ya koma kamar wani idol yayi shiru yana sauraren muryanta dake masa yawo cikin kansa,so yake ya tuna inda yasan wannan muryan,yayin da a b'angaren BB shima hakan take dan shi kam gani yake a yanzun yana da yak'inin itance da kashi 50%,babban abunda yasa bai gama amincewa da itanceba ganin yadda wannan take b'aka,ga yanayin suturan dake jikinta sannan ya tsinceta cikin yanayin da baya tunanin KHUBRA zata shiga.
Duk sunyi shiru har sai da yayi k'arfin hali tare da danne zuciyarsa kan lallaifa wannan ba waccan KHUBRA'N da suke tsammani bace,kawai dai yanayin halittane da kuma su d'in da suke cikin yanayi na rud'u yasa suke ganin kamar itan ce da gaske.
Kautar da tunanin yayi tare da fad'in
"Amm!ina fatan dai ba zaki damuba dan da d'an tafiya tsakanin nan da gurin da mukayi parking"
"A'a babu komai,muje kawai"
Ta fad'a tana juya akalar kuran nata da niyyan komawa bayan garin inda suka bar motan nasu.
A baya suka shiga binta tana tura kuran nata,duk wani motsi nata akan idanunsa hakan yake yana ankare da ita,suna tsaka da tafiyan ne wata matashiya ta taho kanta d'auke da robber yellow da alama daga rafi take ta gansu suna tafiya,kallon mamaki tabisu da shi kafin tayi magana
"A'a KHUBRA ina kuma zaki nufa haka bayan kin d'ebo ruwan kike k'ok'arin komawa"
Cak!KHUBRA ta tsaya a gurin kamar anyi pausing enta ba tare da ta k'ara one step forward ba.
"Shi kenan HAFSAT kin tonamin asiri,wayyyo Allah ka kawomin d'auki"
Abunda ta furta kenan k'asa-k'asa idanunta a runtse ba tare da tayi tsammanin wani cikinsu zaiji me ta fad'aba.
A hankali ya furta
"ALHAMDULILLAH ALAA KULLI HALIN!
ALHAMDULILLAHIL-LAZIIY BI NI'IMATIHI TATIMMUS-SALIHAT!!!"
Yanzun kam ya gama samun shaidan da ya bayyana masa itan ce dai wacce yake hasashe d'ari bisa d'ari yanzun ya tabbatar da hakan.
"Amma to ya akayi ta koma haka ne kam?"
Yayima kansa tambayan ba tare da tunanin samun amsa daga gare shiba.
Matsawa yayi a hankali ya d'auke hat en dake kanta tare da sake k'ureta da kallo,ko tantama baya yi yanzun kam daya ga fuskarta ya gama yin amanna akan yak'ininsa gaskiya ne.
"Why KHUBRA zaki nuna baki ganemuba a yanzun?me yasa?me yasa za kiyi haka??"
Cike da tsawa ya k'arashe maganar tasa.
Kuka ne ya kufce mata wanda daga ji kasan mai yinsa cike yake da fargaba da kuma tsoron halin da take ciki,ta jima tana kukan wanda su dake tsaye gurin suka kasa magana sai kallonta kawai da suke yi,ganin bata da niyyan dainawane yasa KHALEEL yin magana
"Ina tunanin yanzu kam ba kuka ne abunda ya kamata kiyi ba,godiya ya kamata kiyiwa Allah da yayi sanadiyyar had'uwarmu,kafin mu wuce gida kuma"
"A'aaaa!! babu inda zani........ni kam babu inda zani........bazan biku ko inaba.........kawai kuyi tafiyanku ku k'yaleni a nan.........bazan biku ba!"
Ta fad'a lokacin da kukanta ya dad'a tsananta,tana ta kuka mai tsuma zuciya.
HAFSAT dake tsaye har lokacin duk abunda ya faru akan idonta,duk wani furucinsu da maganganunsu ya tabbatar mata da akwai wata alak'a tsakanin wad'annan samari da *KHUBRA Y'AR GARUWA* ,cillli tayi da robber dake kanta take ta felle k'afafunta ta yanki hanya sai cikin gari,gudu take shek'awa wanda ba ita ta tsaya ba sai gaban BABA ZUWAIRA dake ta hada-hadar sallamar customer's,cike da haki take maganaa
"BABA kiyi sauri ga KHUBRA can a bayan gari da wasu samari sai kuka take yi kuma"
Ambaton sunan KHUBRA da tayi shi ya dakatar da ita daga abunda take yi ta mik'e tsaye cikin firgici dafe chest enta
"Y'ar nan maza sanar da ni inda kika ganta tun kafin wani abu ya sameta"
Cike da rud'ewa take musamman jin ance KHUBRA'N tana kuka shi ne babban tashin hankalinta saboda tunanin BABA ZUWAIRA a wannan halin samarin tareta sukayi zasu mata "FYA'DE".
HAFSAT a gaba BABA ZUWAIRA a bayanta yayinda tayi k'wallo da kayan abincin ta marawa HAFSA'N baya sunata faman fakaka sauri kamar wad'anda zasu tashi sama..
Kukanta take tuk'uru yayin da ta kuma jajirce kai da fata ba inda zata bisu itakam,suna tsaka da wannan tak'addamar su BABA ZUWAIRA suka iso gurin,har kuma lokacin ta kasa yin shiru daga kukan da take yi.
"Y'ar nan ina fatan kina lafiya"
BABA ZUWAIRA ta fad'a tana shafa jikin KHUBRA'N dake tsaye.
Da sauri KHUBRA ta k'ank'ameta tana sake sakin kuka
"Ni bazan bisuba,a nan zan ci gaba da zama gurinki"
Maganarta ta d'aurewa BABA ZUWAIRA kai cike da mamaki ta d'agota suna kallon juna ta kuma furta
"Yi shiru ki sanar da ni,ina ne baza ki bisu ba?"
"Gida zasu maida ni,ni kuma ba zan bisu ba,ni gaskiya a nan zan ci gaba da zama gurinki"
Kallonsu tayi d'aya bayan d'aya,sai yanzun ta soma d'aukan haske game da lamarin nasu da kuma inda maganar KHUBRAN ta nufa,cike da jin dad'in Allah ya kawowa y'ar tata k'arshen wannan rayuwar k'uncin take fad'in
"ALHAMDULILLAH!Lallai Allah shi ne abun godiya a kowane irin yanayi,Allah ya amshi rok'onmu da addu'o'inmu da muka jima munayi,Allah mun gode maka"
Idanunta d'auke da k'wallar farin ciki take ta magana,kafin talli KHUBRA
"Bai kamata muci gaba da tsaiwa a nanba,muje gida tukun sai muyi magana ina ganin hakan zaifi"
Fuskarta d'auke da wani irin expression da ba zai fassaruba suka mik'i hanya da niyyan komawa cikin gari,inda KHALEEL yayi saurin zuba ruwa a motan ya biyo bayansu dan su kam har sunyi gaba basu tsaya jiran shiga motaba....
《《》》
Shigowanta gidan kenan daga hospital,shima daga dukkan alamu ta dawone dan yin wasu uzurorin kafin ta koma.
Wayanta ne ya shiga kuka a parlor saboda nan ta ajiye hand bag en da ta shigo da shi yanzun,tana shirin shiga kitchen kasancewar gidan babu kowa duk yaran sun tafi skul saboda yau en ta kama monday ne shi yasa take ta komai cikin sauri duk dan ta kammala kafin dawowarsu.
Kukan wayan da ta jiyo shi ya fito da ita daga kitchen en cikin sauri ta d'auka dai² lokacin da kiran ya zama missed,d'an janye key en tayi sannan ta duba number da aka kiratan da shi,kafin tayi wani yunk'uri wani kiran ya sake shigowa cikin sauri ta d'auka
"Assalamu alaikum!SON mutanen DUTSE ince dai ba cewa za kayi kuna hanya ba ko?"
Sai da yayi wani murmushi mai cike da sauti wanda yake nuna yana tattare sa tsantsar farin ciki sannan ya amsa mata
"UMMINAH barka da safiya da fatan duk kuna lafiya"
"Lafiya k'alau muke SON ya mutanen gidan?"
"Wallahi suna lafiya UMMI duk suna gaidaku"
"Muna amsawa kun samesu lafiya dai ko?"