Sashe 43
Yar Garuwa Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
BIGGY zaune a parlor yanata tunanin maganar BEAUTY'NSA da har yau bai san takaimaman sunantaba,yau kimanin kwanaki sati guda kenan da tayi masa maganar tana son ya taimaketa ya maidata gida,kuma tun daga ranan ne bai sake komawa d'akinba sai dai ya aika a kai mata abinci.
Tunanin hanyar da zaibi ya magance duk wata damuwa dake neman kunno masa kai yake,yana nan yana tunani kiran HAJIYA LAURA ya shigo wayansa,kallon saman screen en yake ya k'ureshi da ido kamar mai son gano wani abu a jikin sunan dake lilo saman wayan,har kiran ya katse ba tare da yayi yunk'urin d'auka ba.
Yana kallo wani kiran ya sake shigowa wayan amma baiyi yunk'urin d'aukaba,haka tayi ta kira har ta gaji ta kyaleshi.
Tun safe yake gurin a zaune ba tare da yayi yunk'urin yin komaiba har misalin k'arfe 4:00pm sallah kad'ai ke fad'a shi a zaman gurin saboda duk iskancin BIGGY baya tab'a yadda sallah ta wuceshi,kamar wanda aka tsikara ya mike yana nufan hanyan bedroom en da take ciki.
Zaune take kamar kowane lokaci ta had'a kai da guiwa tana ta jan zuciya saboda kukan da ta jima tana yi.
Zama yayi a gabanta wanda yasa tayi saurin d'ago jajayen idanunta ta kalleshi tana jiran jin dame yazo yau kuma.
Kallon yanayinsa tayi duk ya wani koma silent da shi,kanta ta sunkuyar tana sauraron jin me zai ce.
Har kusan mintuna biyar ya d'iba yana zaune yayi shiru ba tare da ya iya furta komaiba,sannan yayi ajiyan zuciya cikin sanyin murya dake nuni da mai maganar yana tare da wani yanayi na damuwa a hankali ya furta
"BEAUTY dan Allah kiyi hak'uri da abunda ya faru,tun daga ranar da muka d'aukoki har zuwa yau da nake zaune a kusa dake ina son ki yafemin,tabbas shigowarki rayuwata ya sauyamin tsarina kuma ya canja ni gaba d'ayana,tun daga lokacin dana rasa mahaifana ban sake tunanin zan koma mutumin dake da tausayi a zuciyarsa ba ko dai² da d'igo d'aya amma zuwanki yana neman mai dani wani a rayuwa,zuwanki ya kawo haske cikin rayuwata,nayi alfahari da hakan ta faru,amma ina so kiyi hak'uri da abunda mukayi miki sannan".
Yayi shiru na d'an wani lokaci yana nazarin me zai fad'a kuma wanda zaisa tayi magana
Kallonsa kad'ai ta tsaya yi tana mamakin kalmomin da suke fitowa daga bakinsa,tausayinsa ne ya bijiro mata jin shi d'in marayane,wasu siraran hawaye ta goge tana d'aga masa kai ba tare da tayi magaba.
"In sha Allah daga yau babu wanda zai sake sani aikata irin wannan d'anyen aikin,rashin iyaye ba hauka bane da har wani zai dinga juyamin tunani ta har sani aikata ayyukan marasa imani"..
'Dan murmushi ASHNA ta sake yi tana sauraron maganarsa dake tafiya kai tsaye cikin zuciyarta
Tashi yayi da niyyan barin d'akin,wanda ASHNA sam bata san me yake afkuwa ba,saboda yadda take ta tunanin abubuwa da dama akansa,dai² bakin k'ofa ya dakata sannan cikin sanyi yace
"Ammm!ina ganin yanzun ya kamata kiyi shirin komawa gida,yanzun in Allah ya yarda zan maida ke"
Yana kaiwa nan a maganarsa yayi waje da sauri dan bata damar shiryawa.
Dariya game da hawayen farin ciki suka had'e mata lokaci guda,farin cikinta a wannan lokacin baya misaltuwa,cikin gaggawa ta kimtsa sannan ta fito daga d'akin rana ta farko tun bayan shiganta d'akin kenan da ta fito a hankali take bin corridor en tana wucewa har ta iso dai² stair's,sakkowa take jikinta yayi mata sanyi duk da tafi damuwa da son komawa gida,a parlor ta tarar da shi yana zaune ya d'ora hab'arsa a kan hannayensa da alama tunani yake,sai dai kuma sakkowanta yasa shi binta da kallo had'e da k'irk'irar murmushi,hakan ya tabbatar da baiyi nisa a tunaninba kenan.Mik'ewa yayi ita kuma tana binsa a baya har suka isa parking space na gidan,sai yanzun ta samu daman kallon gidan,babbane sosai ko dan da dare ne wancan ranan shi yasa bata iya tantancewaba.
A hankali ta d'age kafad'anta tana fad'in
"Ohooo ina ruwana a ciki wai kam???"
Kafin ta sake yunk'urin yin wani tunani har ya bud'e motan tare da mata nuni data shiga,babu musu ko ta shige shi kuma ya zagaya d'ayan side en ya zauna sannan yayi starting motan,cikin k'ank'anin lokaci suka fice daga gidan suka hau hanyan da zata sadasu da RIJIYAR ZAKI...
《《》》
Shirun da DR en yayi ne ya dad'a tada mata hankali to kuma me yake son sanar da ita haka,bakinta har rawa yake yi wajen son tambayarsa abunda ya gani a jikin result en nata.
"Dan Allah likita ka sanar dani abunda yake faruwa da har yasa kayi shiru kak'i sanarmin"
Wani ajiyan zuciya ya sauke sannan ya sake kallonta.
"No hajiya ba wani abu ke damunkiba kawai dai zazzab'i ne maybe kuma akwai abunda bakya amfani da shi da kika soma using nasa cikin y'an kwanakin nan,so ina ganin babu wata matsala,yanzun zan d'oraki kan magunguna idan yaso nan da wani lokaci idan bakiji sauk'iba sai ki dawo don a chanja miki da wasu"
Wani wawan ajiyan zuciya ta sauke sannan a hankali ta iya furta
"Ai ni wallahima DR har ka bani tsoro da kalamanka na farko kwata-kwata banyi tsammanin wannan ne abunda zai fito daga bakinkaba"
A kaikaice ya kalleta saboda rashin amincewa da maganar tata,shi kam baisan dalili ba da yasa yake mata wani irin kallo,saurin yin rubutu yayi ya mika mata card en sannan ya furta
"Hajiya ai babu abun tada hankali anan saboda jininki ya nuna 'NEGATIVE' da ya koma 'POSITIVE' ne zamu iya cewa akwai matsala"
Duk bayanin da yake mata ba wani gane negative da positive da tayi saboda bata san me hakan ke nufiba,murmushi tayi kawai ta amsa card en tana masa godiya sannan ta fice..
Bayan fitanta ya tsaya yana bin k'ofan da kallo,haka kad'ai yake tunani wannan matar da gani kaga irin y'an duniyan nan,kome ya tuna kuma yayi saurin kawar da tunanin ta hanyar janyo ragowar file's dake kan table en ya shiga bud'ewa yana ci gaba da aikinsa....
《《》》
Sallah yaketa jerowa babu sassautawa tun yanayi yana iya gane abunda yake karantawa har ya zamana idanunsa sun koma sai haske kad'ai yake gani cikinsu babu wani abu da yake iya shaidawa cikin d'akin bare har ya iya nuna muhallinsa,zaman tahiya yayi sannan ya sallame,zuciyarza tayi k'uncin da baya iya bambance tsakanin fari da bak'i.
Zama yayi had'e da tank'washe kafarsa cikin yanayi dake nuni da yana tattare da matsananciyar damuwa da bata da iyaka a wannan lokacin.
Yarinyarsa ce ta fad'o masa tunaninta duk ya addabeshi,take ya goge fuskarsa ya fito daga d'akin,d'an k'aramin d'akin da yayi bak'i wanda ke nuni da d'akin girki ne ya nufa da niyyan tasota tayi sallah a tunaninsa tana ciki kawai dai sha'afa yayi bai tasheta ba hakan yasa yake ta sauri dan yadda shima yake ganin yau d'in ya makara.
Babu komai cikin d'akin face tarkacen kwanukan girki,tsayawa yayi turus yana bin gurin da kallo,wani irin tunani ya soma yi wanda a k'arshensa babu komai sai tsananin firgici da yasa ABBAN KHUBRA sake nufar d'akin LADIYO kamar zai tashi sama dan sauri...
《《》》
Tun shigansu d'akin da MAMA ke kwance kamar gawa bakinta da hancinya sakaye cikin abun daidaita numfashi,kowa jikinsa ya dad'a sanyaya kamar an jefi kaza da gishiri.
Kusa da gadon MAMA KHUBRA ta matsa saboda tun shigowarsu hankalinta na kanta abun tausayi haka ta zauna gefenta hannunta ta rik'o had'e da damk'ewa cikin nata,nan da nan hawaye suka soma sakkowa daga idanunta,sheshek'an kukanta kad'ai suka tsinkayo BB,UMMI,KHALEEL dama su kansu sauran da suke cikin d'akin,sai dai abunda tayi ya basu matuk'ar mamaki dan suna da tabbacin irin k'iyayan da MAMA kewa KHUBRA.
Cikin muryar kuka take tambayan ZUHRA
"Me ya samu MAMA'N haka?"
Cikin ALHINI ta bata amsan duk abunda ya faru sannan kuma da dalilin kwanciyan MAMA'N jinya.
Bakinta ta shiga motsawa tana mata addu'a wacce ANNABI (S.A.W) ya koyar damu a duk lokacin da wani yake halin jinya wato
_(AS-ALULLAHAL AZIIYM RABBAL ARSHIL AZIIYM AN-YASHFIYAKII ×7)_
Sannan ta sake k'arawa da
_(LAA BA'ASA 'DAHURUN IN-SHA-ALLAH)_
Idanun BB na kanta duk abunda take sai dai ba kowa ne zai gane hakanba saboda ta tsakanin lashes ensa yake kallonta hannayensa zube cikin aljihunsa.
Juyowa KHUBRA tayi da niyyan yiwa ZUHRA magana hannun MAMA dake cikin nata ya motsa,cikin saurin ta juya don tabbatarwa,k'afarta ta sake motsawa sannan sauran wasu sassa na jikinta da suka motsa,a hankali kuma idanunta suka soma bud'ewa.
Duk abunda ake babu wanda ya kula da halin da ake ciki,kabbara KHUBRA tayi wanda yasa su saurin matsowa kusa da gadon suna tambayan lafiya,idanun MAMA da suke bud'ewa da ta kafe fuskar MAMAN da kallo ne yasa su kallon abunda takewa irin wannan kallon cikin wani yanayi na jin dad'i gaba d'ayan d'akin suka d'auki kabbara suma,masu hawaye nayi masu murna nayi saboda halin da suke ciki a wannan lokacin na tashin MAMA ba tare da sunyi tsammanin afkuwar hakanba.....
《《》》
Parking sukayi dai² bakin get en gidan suna shirin fitowa BABA MAI GADI ya fito daga gidan da y'ar radio ensa a hannu,kallonsu yayi yana shirin tambayan wanda suka zo nema idanunsa suka sauka kan ASHNA dake kan gaba.
"K'aaluu innalillahi wa-inna ilaihi raji'un,me zan gani haka?HAJIYA da gaske kece ko kuwa fatalwa nayi gamo da ita?"
Yana tambaya yana kuma had'awa da jaa baya,maimakon tayi magana da fad'a kamar yadda ta saba musu sai yaji sab'anin hakan wanda ya dad'a jefa shi cikin taradaddin anya kuwa itance da gaske?
"Nice BABA ba fatalwa bace"
Ta fad'a tana d'an murmusawa..
Al-ajabi yake na sauyin da ya gani a tare da ita da yasa shi kasa magana,har suka wuce suna niyyan shiga gidan ya dakatar da su ta hanyar fad'in
"Babu kowa cikin gidan HAJIYA"
Da sauri suka juyo suna kallonsa,cikin rud'ewa kuma ta fara magana
"Ina suka tafi suka barni?dan Allah BABA suna ina ?"
"Kiyi hak'uri HAJIYA amma gidan nan ya kai tsawon kwanaki babu kowa cikinsa,HAJIYA ce babu lafiya tana kwance a asibiti cikin mawuyacin halin da ko sanin wanda ke kanta bata iya yi"....
Tunanin hanyar da zaibi ya magance duk wata damuwa dake neman kunno masa kai yake,yana nan yana tunani kiran HAJIYA LAURA ya shigo wayansa,kallon saman screen en yake ya k'ureshi da ido kamar mai son gano wani abu a jikin sunan dake lilo saman wayan,har kiran ya katse ba tare da yayi yunk'urin d'auka ba.
Yana kallo wani kiran ya sake shigowa wayan amma baiyi yunk'urin d'aukaba,haka tayi ta kira har ta gaji ta kyaleshi.
Tun safe yake gurin a zaune ba tare da yayi yunk'urin yin komaiba har misalin k'arfe 4:00pm sallah kad'ai ke fad'a shi a zaman gurin saboda duk iskancin BIGGY baya tab'a yadda sallah ta wuceshi,kamar wanda aka tsikara ya mike yana nufan hanyan bedroom en da take ciki.
Zaune take kamar kowane lokaci ta had'a kai da guiwa tana ta jan zuciya saboda kukan da ta jima tana yi.
Zama yayi a gabanta wanda yasa tayi saurin d'ago jajayen idanunta ta kalleshi tana jiran jin dame yazo yau kuma.
Kallon yanayinsa tayi duk ya wani koma silent da shi,kanta ta sunkuyar tana sauraron jin me zai ce.
Har kusan mintuna biyar ya d'iba yana zaune yayi shiru ba tare da ya iya furta komaiba,sannan yayi ajiyan zuciya cikin sanyin murya dake nuni da mai maganar yana tare da wani yanayi na damuwa a hankali ya furta
"BEAUTY dan Allah kiyi hak'uri da abunda ya faru,tun daga ranar da muka d'aukoki har zuwa yau da nake zaune a kusa dake ina son ki yafemin,tabbas shigowarki rayuwata ya sauyamin tsarina kuma ya canja ni gaba d'ayana,tun daga lokacin dana rasa mahaifana ban sake tunanin zan koma mutumin dake da tausayi a zuciyarsa ba ko dai² da d'igo d'aya amma zuwanki yana neman mai dani wani a rayuwa,zuwanki ya kawo haske cikin rayuwata,nayi alfahari da hakan ta faru,amma ina so kiyi hak'uri da abunda mukayi miki sannan".
Yayi shiru na d'an wani lokaci yana nazarin me zai fad'a kuma wanda zaisa tayi magana
Kallonsa kad'ai ta tsaya yi tana mamakin kalmomin da suke fitowa daga bakinsa,tausayinsa ne ya bijiro mata jin shi d'in marayane,wasu siraran hawaye ta goge tana d'aga masa kai ba tare da tayi magaba.
"In sha Allah daga yau babu wanda zai sake sani aikata irin wannan d'anyen aikin,rashin iyaye ba hauka bane da har wani zai dinga juyamin tunani ta har sani aikata ayyukan marasa imani"..
'Dan murmushi ASHNA ta sake yi tana sauraron maganarsa dake tafiya kai tsaye cikin zuciyarta
Tashi yayi da niyyan barin d'akin,wanda ASHNA sam bata san me yake afkuwa ba,saboda yadda take ta tunanin abubuwa da dama akansa,dai² bakin k'ofa ya dakata sannan cikin sanyi yace
"Ammm!ina ganin yanzun ya kamata kiyi shirin komawa gida,yanzun in Allah ya yarda zan maida ke"
Yana kaiwa nan a maganarsa yayi waje da sauri dan bata damar shiryawa.
Dariya game da hawayen farin ciki suka had'e mata lokaci guda,farin cikinta a wannan lokacin baya misaltuwa,cikin gaggawa ta kimtsa sannan ta fito daga d'akin rana ta farko tun bayan shiganta d'akin kenan da ta fito a hankali take bin corridor en tana wucewa har ta iso dai² stair's,sakkowa take jikinta yayi mata sanyi duk da tafi damuwa da son komawa gida,a parlor ta tarar da shi yana zaune ya d'ora hab'arsa a kan hannayensa da alama tunani yake,sai dai kuma sakkowanta yasa shi binta da kallo had'e da k'irk'irar murmushi,hakan ya tabbatar da baiyi nisa a tunaninba kenan.Mik'ewa yayi ita kuma tana binsa a baya har suka isa parking space na gidan,sai yanzun ta samu daman kallon gidan,babbane sosai ko dan da dare ne wancan ranan shi yasa bata iya tantancewaba.
A hankali ta d'age kafad'anta tana fad'in
"Ohooo ina ruwana a ciki wai kam???"
Kafin ta sake yunk'urin yin wani tunani har ya bud'e motan tare da mata nuni data shiga,babu musu ko ta shige shi kuma ya zagaya d'ayan side en ya zauna sannan yayi starting motan,cikin k'ank'anin lokaci suka fice daga gidan suka hau hanyan da zata sadasu da RIJIYAR ZAKI...
《《》》
Shirun da DR en yayi ne ya dad'a tada mata hankali to kuma me yake son sanar da ita haka,bakinta har rawa yake yi wajen son tambayarsa abunda ya gani a jikin result en nata.
"Dan Allah likita ka sanar dani abunda yake faruwa da har yasa kayi shiru kak'i sanarmin"
Wani ajiyan zuciya ya sauke sannan ya sake kallonta.
"No hajiya ba wani abu ke damunkiba kawai dai zazzab'i ne maybe kuma akwai abunda bakya amfani da shi da kika soma using nasa cikin y'an kwanakin nan,so ina ganin babu wata matsala,yanzun zan d'oraki kan magunguna idan yaso nan da wani lokaci idan bakiji sauk'iba sai ki dawo don a chanja miki da wasu"
Wani wawan ajiyan zuciya ta sauke sannan a hankali ta iya furta
"Ai ni wallahima DR har ka bani tsoro da kalamanka na farko kwata-kwata banyi tsammanin wannan ne abunda zai fito daga bakinkaba"
A kaikaice ya kalleta saboda rashin amincewa da maganar tata,shi kam baisan dalili ba da yasa yake mata wani irin kallo,saurin yin rubutu yayi ya mika mata card en sannan ya furta
"Hajiya ai babu abun tada hankali anan saboda jininki ya nuna 'NEGATIVE' da ya koma 'POSITIVE' ne zamu iya cewa akwai matsala"
Duk bayanin da yake mata ba wani gane negative da positive da tayi saboda bata san me hakan ke nufiba,murmushi tayi kawai ta amsa card en tana masa godiya sannan ta fice..
Bayan fitanta ya tsaya yana bin k'ofan da kallo,haka kad'ai yake tunani wannan matar da gani kaga irin y'an duniyan nan,kome ya tuna kuma yayi saurin kawar da tunanin ta hanyar janyo ragowar file's dake kan table en ya shiga bud'ewa yana ci gaba da aikinsa....
《《》》
Sallah yaketa jerowa babu sassautawa tun yanayi yana iya gane abunda yake karantawa har ya zamana idanunsa sun koma sai haske kad'ai yake gani cikinsu babu wani abu da yake iya shaidawa cikin d'akin bare har ya iya nuna muhallinsa,zaman tahiya yayi sannan ya sallame,zuciyarza tayi k'uncin da baya iya bambance tsakanin fari da bak'i.
Zama yayi had'e da tank'washe kafarsa cikin yanayi dake nuni da yana tattare da matsananciyar damuwa da bata da iyaka a wannan lokacin.
Yarinyarsa ce ta fad'o masa tunaninta duk ya addabeshi,take ya goge fuskarsa ya fito daga d'akin,d'an k'aramin d'akin da yayi bak'i wanda ke nuni da d'akin girki ne ya nufa da niyyan tasota tayi sallah a tunaninsa tana ciki kawai dai sha'afa yayi bai tasheta ba hakan yasa yake ta sauri dan yadda shima yake ganin yau d'in ya makara.
Babu komai cikin d'akin face tarkacen kwanukan girki,tsayawa yayi turus yana bin gurin da kallo,wani irin tunani ya soma yi wanda a k'arshensa babu komai sai tsananin firgici da yasa ABBAN KHUBRA sake nufar d'akin LADIYO kamar zai tashi sama dan sauri...
《《》》
Tun shigansu d'akin da MAMA ke kwance kamar gawa bakinta da hancinya sakaye cikin abun daidaita numfashi,kowa jikinsa ya dad'a sanyaya kamar an jefi kaza da gishiri.
Kusa da gadon MAMA KHUBRA ta matsa saboda tun shigowarsu hankalinta na kanta abun tausayi haka ta zauna gefenta hannunta ta rik'o had'e da damk'ewa cikin nata,nan da nan hawaye suka soma sakkowa daga idanunta,sheshek'an kukanta kad'ai suka tsinkayo BB,UMMI,KHALEEL dama su kansu sauran da suke cikin d'akin,sai dai abunda tayi ya basu matuk'ar mamaki dan suna da tabbacin irin k'iyayan da MAMA kewa KHUBRA.
Cikin muryar kuka take tambayan ZUHRA
"Me ya samu MAMA'N haka?"
Cikin ALHINI ta bata amsan duk abunda ya faru sannan kuma da dalilin kwanciyan MAMA'N jinya.
Bakinta ta shiga motsawa tana mata addu'a wacce ANNABI (S.A.W) ya koyar damu a duk lokacin da wani yake halin jinya wato
_(AS-ALULLAHAL AZIIYM RABBAL ARSHIL AZIIYM AN-YASHFIYAKII ×7)_
Sannan ta sake k'arawa da
_(LAA BA'ASA 'DAHURUN IN-SHA-ALLAH)_
Idanun BB na kanta duk abunda take sai dai ba kowa ne zai gane hakanba saboda ta tsakanin lashes ensa yake kallonta hannayensa zube cikin aljihunsa.
Juyowa KHUBRA tayi da niyyan yiwa ZUHRA magana hannun MAMA dake cikin nata ya motsa,cikin saurin ta juya don tabbatarwa,k'afarta ta sake motsawa sannan sauran wasu sassa na jikinta da suka motsa,a hankali kuma idanunta suka soma bud'ewa.
Duk abunda ake babu wanda ya kula da halin da ake ciki,kabbara KHUBRA tayi wanda yasa su saurin matsowa kusa da gadon suna tambayan lafiya,idanun MAMA da suke bud'ewa da ta kafe fuskar MAMAN da kallo ne yasa su kallon abunda takewa irin wannan kallon cikin wani yanayi na jin dad'i gaba d'ayan d'akin suka d'auki kabbara suma,masu hawaye nayi masu murna nayi saboda halin da suke ciki a wannan lokacin na tashin MAMA ba tare da sunyi tsammanin afkuwar hakanba.....
《《》》
Parking sukayi dai² bakin get en gidan suna shirin fitowa BABA MAI GADI ya fito daga gidan da y'ar radio ensa a hannu,kallonsu yayi yana shirin tambayan wanda suka zo nema idanunsa suka sauka kan ASHNA dake kan gaba.
"K'aaluu innalillahi wa-inna ilaihi raji'un,me zan gani haka?HAJIYA da gaske kece ko kuwa fatalwa nayi gamo da ita?"
Yana tambaya yana kuma had'awa da jaa baya,maimakon tayi magana da fad'a kamar yadda ta saba musu sai yaji sab'anin hakan wanda ya dad'a jefa shi cikin taradaddin anya kuwa itance da gaske?
"Nice BABA ba fatalwa bace"
Ta fad'a tana d'an murmusawa..
Al-ajabi yake na sauyin da ya gani a tare da ita da yasa shi kasa magana,har suka wuce suna niyyan shiga gidan ya dakatar da su ta hanyar fad'in
"Babu kowa cikin gidan HAJIYA"
Da sauri suka juyo suna kallonsa,cikin rud'ewa kuma ta fara magana
"Ina suka tafi suka barni?dan Allah BABA suna ina ?"
"Kiyi hak'uri HAJIYA amma gidan nan ya kai tsawon kwanaki babu kowa cikinsa,HAJIYA ce babu lafiya tana kwance a asibiti cikin mawuyacin halin da ko sanin wanda ke kanta bata iya yi"....