Sashe 36
Yar Garuwa Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Parlor'n shiru babu abunda ke tashi sai k'ira'ar SHEIKH-MANSHAWIIY cikin tashar nan ta SAUDI-QUR'AN...
Ta yi shiru tana sauraron karatun sukayi sallama a bakin parlor'n had'e da shigowa,kowanne fuska babu annuri...
Da sauri UMMI ta shiga fad'in
"Al-hamdulillah!!
SON ina ka shiga yau tun safe?kasa hankalina duk ya tashi sai nemanka nake...
Ina kaje kam duk layukan wayankama suna shiga baka d'auka?"
Shiru yayi yana dad'a yin k'asa da kai,sai shigewa bayan BB yake,kamar wanda yake tsoron fad'in abunda aka tambayeshi...
Shiru UMMI tayi tana kallon ikon Allah tare da rik'e hab'anta...
Wucewa BB yayi ya zauna saman cuitions en dake parlor'n,cikin sanyin murya yake gaida UMMI datake binsu da kallon mamaki...
Ta k'asan idonsa yake kallon UMMI da take tsaye itama har lokacin bata zauna ba,kuma ta kasa barin gurin...
"Wai daga ina kukema tukun duk kun wani yimin shiru kunk'i magana...
Na tambayeka kai kuma kak'i bani amsa ko?"
"Kiyi hak'uri UMMI wallahi uzuri ne yasa muka fita bamu sanar dakeba,amma in sha Allah bazai sake faruwaba"
BB ya fad'a yana hararan KHALEEL da ya kasa zama,sai yanzu da BB yayi magana tukun ya matso kusa da UMMI..
"Allah UMMI ba da niyya nayiba matsala ce tasa muka fita bamu sanar mikiba,kuma daima lokacinfa bana jin kin tashi...
Yawwa UMMI kin hak'ura ko?"
Cike da shagwab'a yayi maganar yana had'e hannunsa alaman ban hak'uri...
Murmushi tayi tana matsowa inda yake,ganin tana murmushi shima ya shiga murmusawa..
Kunnensa ta rik'e ta d'an murd'a kad'an...
"Argghh!UMMI wallahi da zafi,zafa ki ciremin kunne,dan Allah kiyi hak'uri,nayi miki alk'awari baran sake ba"....
Duk maganar yana yin tane dafe da side en fuskansa da ummi ta rik'e idansa a rufe....
Shikam BB yana zaune yana kallon ikon Allah....
Sakin kunnen tayi tana fad'in
"Gobema idan ka tashi fita kada ka fad'amin kaji ko"
BB ta kalla tana murmushi,sai dai yanayinsa kad'ai ta karanta tasha jinin jikinta kan yadda ta ganshi,zama tayi lokacin shima KHALEEL ya zauna yana murza kunnensa dan da alama har lokacin bai daina masa zafiba.....
"KHALEED lafiya kuwa kake na ganka cikin damuwa,anya kuwa babu wani abu dake damunka"...
Ta d'an yi shiru na wasu sakanni kafin taci gaba da magana,sai da tayi masa nasiha mai shiga rai da ta dad'a sanyaya masa jiki da har yake jin kamar zai yi kuka a lokacin....
KHALEEL yayi gyaran murya yana fad'in
"UMMI gaskiya ba lafiyaba dan kam yau al'amura duk sun dad'a cakud'ewa".....
Nan ya kwashe komai ya sanar da ita daya faru a safiyar ta yau....
Salati take ta zabgawa ta dafe bakinta da hannu,sai juya zancen take tana kad'a kai....
Sun jima parlor'n shiru babu mai magana zuwa wani lokaci sannan UMMI taja ajiyan zuciya tare da kallonsu
"Yanzun waye kuka bari a gurinta?"
Kallon-kallo suka shiga yi tsakanin su biyun,basu bata amsaba sai da ta sake mai²ta musu tambayan...
"Amm!UMMI ai babu kowa gurinta yanzun muma dawowarmu kenan,ZUHRA kuma tana gida mun barota za tayi abincin da za a tafi da shi hospital en"
"Too!Amma kuma labarin ita ASHNA fa ina fatan dai kun sanar da hukuma halin da ake ciki ko?"
BB ne ya shiga kad'a kai alamar a'a,har za tayi magana KHALEEL ya tari numfashinta
"Ehh!UMMI na sanar da D.P.O d'azun ta waya,amma lokacin naso ace zuwa muka yi,sai dai kuma muna hospital shi ne dalilin da yasa bamu jeba"
"To Alhamdulillah tunda hukuma sunsan da b'atan nata,ammafa ni wannan al'amari yana d'auremin kai...
B'atan y'an mata biyu lokaci guda,kuma tazaran sace ta farko da ta biyu duk a cikin shekara d'aya...
Kaiii!Allah yayi mana magani,ubangiji ya tseratar damu daga sharrin masu sharri"
Duk suka amsa da amin,sannan KHALEEL ya gyara zama yana shirin korowa UMMI labarin abunda ya kawosu a yanzun...
"UMMI to amma mufa zuwa mukayi ki samo mana wacce zata zauna a asibitin,wa kike tunanin zamu samu ya zauna da MAMA?
Ina nufin kisa a samo wata matar da zata yi jinyan MAMA har zuwa lokacin da zata samu sauk'i...
Kinga ko da biyanta nema sai ayi idan zamu samu hakan"
Yayi shiru yana jiran jin amsan da zata bayar...
Murmushi tayi irin nasu na manya duk da bana tsammanin zata wuce 45 year's...
"Lallaima yaran nan wato kuna so a samo wata matar daban tayi jinyar MAMA ko?"
Shiru babu wanda ya iya amsawa saima kallonta da suke suna kuma kallon junansu....
"Ina ganin babu buk'atar nemo wata mata da zata yi wannan aikin,ni aikin me nake da ya wuce zaman gida tunda Allah yasa DADDYNKU baya nan bari na kirashi na sanar masa halin da ake ciki sai mu wuce,yanzun babu kowa a gurinta bai kamata a bar mara lafiya shi kad'ai ba,ya kamata ace mun hanzarta sai na kula da ita zuwa lokacin da Allah zaisa ta samu sauk'i...
Daga nan kuma sai ku koma gida ku d'aukomin su ZUHRA da kayansu,bai kamata ace an barsu su kad'ai a cikin gidaba tunda ba wani girmane da su ba,ni zan kula dasu zuwa lokacin da HAJIYAN zata samu sauk'i,in sha Allah kuma zan kula da HAJIYAN,Allah ya bata lafiya mai d'orewa...
Su kuma Allah ya bayyana mana inda suke idan da rabon mu sake had'uwa da su"...
Ta k'are maganar fuskarta da annuri shimfid'e samanta
Suma maganar ta UMMI kam tayi musu dad'i sosai wanda har suka rasa bakin magana...
Cike da jin dad'i sukema UMMI godiya cike kuma da jin dad'i mara misaltuwa.....
"To amma UMMI akwai fa wata sabuwar matsalar"
KHALEEL ya katse musu maganar da suke dai² lokacin
Da mamaki take kallonsa
"Matsala kuma ta me kenan?"
Bayanin tafiyar da zasu yi zuwa DUTSE suka yi mata da manufar da zata kaisu...
"To amma yaushe kuka shirya yin tafiyar?"
Tayi tambayar tana son sanin lokacin da suka yanke tafiyar
"UMMI ai mu da a gobema muke son tafiya,tunda dai ance da sanyin safiya ake kama fara koh??"
"Gaskiya ne to Allah ya biyaku da samako mafi kyau kan wannan niyyar taku"
Taji dad'i sosai da bayanin da sukayi mata ta kuma yi musu fatan alkhairi cikin abunda zai kaisu,da addu'o'in samun nasara,daga haka ta mik'e ta shiga shirin tafiya hospital gurin MAMA......
《《》》
ZUHRA har ta gama abunda za tayi a kitchen en ta fito,babu kowa cikin parlor sai FATAHIYYA kad'ai dasu HANEEF...
"Ina su YAYA KHALEEL suka shiga kuma?"
Tayi tambayan tana jiran jin amsan da zasu bata...
FATAHIYYA kam kasa magana tayi dan da ganin alamu taji matsa a gurin BB..
Rik'on da yayi mata bana wasaba,shi yasa har yanzun tana nan tana faman murza wuyanta,danma Allah ya taimaketa KHALEEL na gurin ya kai mata d'auki da kam sai tafi haka jin jiki....
"YAYA ZUHRA sun fita,amma kamar dai masallaci suka tafi"
"To ama kuma idan masallaci ne ai ya kamata ace zuwa yanzun tuni sun dawo tunda gashi har ana sallan la'asar nefa"
"Amma YAYA ZUHURA bakya ganin ko sun jira suyi la'asar enne kafin su dawo"
KHALEEFA ya fad'a
"Ehhh!to kumafa haka ne....
Maza kuje kuyi sallah kuzo kuci abinci kunji ammafa ayiwa MAMA addu'ah kunji ko?"
Cikin sauri suka tashi suka nufi yin sallah,da yake sun san warning en da BB yayi musu kan rashin yin sallah,idan aka bashi labarin ba suyi sallah ba su da shi...
Shi yasa tana yi musu magana suka yi saurin tashi dan yin sallah....
Bayan lokaci mai tsayi suna zaman jiran BB ya dawo dan tafiya hospital en,amma shiru har bayan salla'n Maghreb....
Sai bayan da aka idar da sallah'n ishaa sannan suka shigo gidan shima a gurguje suka shigo,nan KHALEEL yayima ZUHRA bayani dan shi kam BB ko tsayawa baiyiba ya shige ciki...
Haka suka shige kowa dan had'a kayan da yake buk'ata sannan suka fito lokacin KHALEEL har yayi waje,a parlor BB ya tadda su nan ko ya tsaya kansu fuska a d'aure ya jaa musu kunne kan duk wanda aka ce masa yayi wani abu na badai-daiba to ya kuka da kansa dan kam zaima yaro hukunci dai-dai da abunda yayi...
Jikin FATAHIYYA ya sake yin sanyi dan ita kam tana tunanin wannan fad'an na BB da ita yake ba kowaba shi yasa ta dad'a sunkuyar da kanta k'asa uwa wata munafuka...
Har suka bar gidan babu wanda yake k'wak'wk'waran motsi cikin motan haka suka isa gidan su KHALEEL inda zasu soma sabuwar rayuwa da babu MAMA cikinta......
《《》》
'Dakin take k'arewa kallo tana yamutsa face,ko gama shiga d'akin bata yiba ta ji an rufe k'ofan d'akin...
Tab'e baki tayi taci gaba da abunda take na daga yamutsa fuska haka har ta isa bakin mirror en d'akin...
Kan stool en gurin ta zauna tana d'ora kanta kan k'afarta duk ta wani takure kamar wacce take jin mugun sanyi...
Kusan awa guda bata ji motsin kowaba hakan yasa ta sauka daga kan stool en saboda ta gaji da zaman gurin..
Can wani space da ta gani tsakanin closets da bango ta shige ta dad'a takurewa sai yanzun data ga dare yayi sosai wani tsoro ya shigeta duk tunanin gida da MAMA shi yafi damunta,ko wane hali su MAMA suke ciki da sukaji labarin an sace ta...
Wannan tunanin da tayi shi yasata sa kuka mai tsuma zuciya tana yi tana surutai ita kad'ai
"Wayyoo!!! ni shi kenan bazan sake ganin MAMA ba da su ZUHRA,wayyoo!!! Allah sun sace ni ba zasu sake barina naga MAMANA ba"
Tana tsaka da kukan aka turo k'ofan had'e da shigowa,dube-dube ya gamayi cikin d'akin amma bai gantaba kuma dai ya tabbatar da ya kulle d'akin tana ciki....
K'arasa shigowa yayi cikin d'akin bayan jiran da yayi da magana yaji shiru,ya nufi door en toilet amma wayam babu kowa...
Can tsakanin closets da bango ya hango k'afafunta da yake d'akin akwai haske,gurin ya nufa yana mamakin me kuma take yi a nan?
K'arasawa yayi gurin da take da niyyar yin magana sai dai me tun kafin ya isa ya fara jiyo kukanta da ba'a ji sosai sai an matso kusa da ita...
"BEAUTY me ya sameki kike kuka?"......
~Tofa wata sabuwa inji y'an chacha,su ASHNA kuma an koma BEUTY ammafa ba a bakinaba a bakin BIGGY~...
《《》》
Ta yi shiru tana sauraron karatun sukayi sallama a bakin parlor'n had'e da shigowa,kowanne fuska babu annuri...
Da sauri UMMI ta shiga fad'in
"Al-hamdulillah!!
SON ina ka shiga yau tun safe?kasa hankalina duk ya tashi sai nemanka nake...
Ina kaje kam duk layukan wayankama suna shiga baka d'auka?"
Shiru yayi yana dad'a yin k'asa da kai,sai shigewa bayan BB yake,kamar wanda yake tsoron fad'in abunda aka tambayeshi...
Shiru UMMI tayi tana kallon ikon Allah tare da rik'e hab'anta...
Wucewa BB yayi ya zauna saman cuitions en dake parlor'n,cikin sanyin murya yake gaida UMMI datake binsu da kallon mamaki...
Ta k'asan idonsa yake kallon UMMI da take tsaye itama har lokacin bata zauna ba,kuma ta kasa barin gurin...
"Wai daga ina kukema tukun duk kun wani yimin shiru kunk'i magana...
Na tambayeka kai kuma kak'i bani amsa ko?"
"Kiyi hak'uri UMMI wallahi uzuri ne yasa muka fita bamu sanar dakeba,amma in sha Allah bazai sake faruwaba"
BB ya fad'a yana hararan KHALEEL da ya kasa zama,sai yanzu da BB yayi magana tukun ya matso kusa da UMMI..
"Allah UMMI ba da niyya nayiba matsala ce tasa muka fita bamu sanar mikiba,kuma daima lokacinfa bana jin kin tashi...
Yawwa UMMI kin hak'ura ko?"
Cike da shagwab'a yayi maganar yana had'e hannunsa alaman ban hak'uri...
Murmushi tayi tana matsowa inda yake,ganin tana murmushi shima ya shiga murmusawa..
Kunnensa ta rik'e ta d'an murd'a kad'an...
"Argghh!UMMI wallahi da zafi,zafa ki ciremin kunne,dan Allah kiyi hak'uri,nayi miki alk'awari baran sake ba"....
Duk maganar yana yin tane dafe da side en fuskansa da ummi ta rik'e idansa a rufe....
Shikam BB yana zaune yana kallon ikon Allah....
Sakin kunnen tayi tana fad'in
"Gobema idan ka tashi fita kada ka fad'amin kaji ko"
BB ta kalla tana murmushi,sai dai yanayinsa kad'ai ta karanta tasha jinin jikinta kan yadda ta ganshi,zama tayi lokacin shima KHALEEL ya zauna yana murza kunnensa dan da alama har lokacin bai daina masa zafiba.....
"KHALEED lafiya kuwa kake na ganka cikin damuwa,anya kuwa babu wani abu dake damunka"...
Ta d'an yi shiru na wasu sakanni kafin taci gaba da magana,sai da tayi masa nasiha mai shiga rai da ta dad'a sanyaya masa jiki da har yake jin kamar zai yi kuka a lokacin....
KHALEEL yayi gyaran murya yana fad'in
"UMMI gaskiya ba lafiyaba dan kam yau al'amura duk sun dad'a cakud'ewa".....
Nan ya kwashe komai ya sanar da ita daya faru a safiyar ta yau....
Salati take ta zabgawa ta dafe bakinta da hannu,sai juya zancen take tana kad'a kai....
Sun jima parlor'n shiru babu mai magana zuwa wani lokaci sannan UMMI taja ajiyan zuciya tare da kallonsu
"Yanzun waye kuka bari a gurinta?"
Kallon-kallo suka shiga yi tsakanin su biyun,basu bata amsaba sai da ta sake mai²ta musu tambayan...
"Amm!UMMI ai babu kowa gurinta yanzun muma dawowarmu kenan,ZUHRA kuma tana gida mun barota za tayi abincin da za a tafi da shi hospital en"
"Too!Amma kuma labarin ita ASHNA fa ina fatan dai kun sanar da hukuma halin da ake ciki ko?"
BB ne ya shiga kad'a kai alamar a'a,har za tayi magana KHALEEL ya tari numfashinta
"Ehh!UMMI na sanar da D.P.O d'azun ta waya,amma lokacin naso ace zuwa muka yi,sai dai kuma muna hospital shi ne dalilin da yasa bamu jeba"
"To Alhamdulillah tunda hukuma sunsan da b'atan nata,ammafa ni wannan al'amari yana d'auremin kai...
B'atan y'an mata biyu lokaci guda,kuma tazaran sace ta farko da ta biyu duk a cikin shekara d'aya...
Kaiii!Allah yayi mana magani,ubangiji ya tseratar damu daga sharrin masu sharri"
Duk suka amsa da amin,sannan KHALEEL ya gyara zama yana shirin korowa UMMI labarin abunda ya kawosu a yanzun...
"UMMI to amma mufa zuwa mukayi ki samo mana wacce zata zauna a asibitin,wa kike tunanin zamu samu ya zauna da MAMA?
Ina nufin kisa a samo wata matar da zata yi jinyan MAMA har zuwa lokacin da zata samu sauk'i...
Kinga ko da biyanta nema sai ayi idan zamu samu hakan"
Yayi shiru yana jiran jin amsan da zata bayar...
Murmushi tayi irin nasu na manya duk da bana tsammanin zata wuce 45 year's...
"Lallaima yaran nan wato kuna so a samo wata matar daban tayi jinyar MAMA ko?"
Shiru babu wanda ya iya amsawa saima kallonta da suke suna kuma kallon junansu....
"Ina ganin babu buk'atar nemo wata mata da zata yi wannan aikin,ni aikin me nake da ya wuce zaman gida tunda Allah yasa DADDYNKU baya nan bari na kirashi na sanar masa halin da ake ciki sai mu wuce,yanzun babu kowa a gurinta bai kamata a bar mara lafiya shi kad'ai ba,ya kamata ace mun hanzarta sai na kula da ita zuwa lokacin da Allah zaisa ta samu sauk'i...
Daga nan kuma sai ku koma gida ku d'aukomin su ZUHRA da kayansu,bai kamata ace an barsu su kad'ai a cikin gidaba tunda ba wani girmane da su ba,ni zan kula dasu zuwa lokacin da HAJIYAN zata samu sauk'i,in sha Allah kuma zan kula da HAJIYAN,Allah ya bata lafiya mai d'orewa...
Su kuma Allah ya bayyana mana inda suke idan da rabon mu sake had'uwa da su"...
Ta k'are maganar fuskarta da annuri shimfid'e samanta
Suma maganar ta UMMI kam tayi musu dad'i sosai wanda har suka rasa bakin magana...
Cike da jin dad'i sukema UMMI godiya cike kuma da jin dad'i mara misaltuwa.....
"To amma UMMI akwai fa wata sabuwar matsalar"
KHALEEL ya katse musu maganar da suke dai² lokacin
Da mamaki take kallonsa
"Matsala kuma ta me kenan?"
Bayanin tafiyar da zasu yi zuwa DUTSE suka yi mata da manufar da zata kaisu...
"To amma yaushe kuka shirya yin tafiyar?"
Tayi tambayar tana son sanin lokacin da suka yanke tafiyar
"UMMI ai mu da a gobema muke son tafiya,tunda dai ance da sanyin safiya ake kama fara koh??"
"Gaskiya ne to Allah ya biyaku da samako mafi kyau kan wannan niyyar taku"
Taji dad'i sosai da bayanin da sukayi mata ta kuma yi musu fatan alkhairi cikin abunda zai kaisu,da addu'o'in samun nasara,daga haka ta mik'e ta shiga shirin tafiya hospital gurin MAMA......
《《》》
ZUHRA har ta gama abunda za tayi a kitchen en ta fito,babu kowa cikin parlor sai FATAHIYYA kad'ai dasu HANEEF...
"Ina su YAYA KHALEEL suka shiga kuma?"
Tayi tambayan tana jiran jin amsan da zasu bata...
FATAHIYYA kam kasa magana tayi dan da ganin alamu taji matsa a gurin BB..
Rik'on da yayi mata bana wasaba,shi yasa har yanzun tana nan tana faman murza wuyanta,danma Allah ya taimaketa KHALEEL na gurin ya kai mata d'auki da kam sai tafi haka jin jiki....
"YAYA ZUHRA sun fita,amma kamar dai masallaci suka tafi"
"To ama kuma idan masallaci ne ai ya kamata ace zuwa yanzun tuni sun dawo tunda gashi har ana sallan la'asar nefa"
"Amma YAYA ZUHURA bakya ganin ko sun jira suyi la'asar enne kafin su dawo"
KHALEEFA ya fad'a
"Ehhh!to kumafa haka ne....
Maza kuje kuyi sallah kuzo kuci abinci kunji ammafa ayiwa MAMA addu'ah kunji ko?"
Cikin sauri suka tashi suka nufi yin sallah,da yake sun san warning en da BB yayi musu kan rashin yin sallah,idan aka bashi labarin ba suyi sallah ba su da shi...
Shi yasa tana yi musu magana suka yi saurin tashi dan yin sallah....
Bayan lokaci mai tsayi suna zaman jiran BB ya dawo dan tafiya hospital en,amma shiru har bayan salla'n Maghreb....
Sai bayan da aka idar da sallah'n ishaa sannan suka shigo gidan shima a gurguje suka shigo,nan KHALEEL yayima ZUHRA bayani dan shi kam BB ko tsayawa baiyiba ya shige ciki...
Haka suka shige kowa dan had'a kayan da yake buk'ata sannan suka fito lokacin KHALEEL har yayi waje,a parlor BB ya tadda su nan ko ya tsaya kansu fuska a d'aure ya jaa musu kunne kan duk wanda aka ce masa yayi wani abu na badai-daiba to ya kuka da kansa dan kam zaima yaro hukunci dai-dai da abunda yayi...
Jikin FATAHIYYA ya sake yin sanyi dan ita kam tana tunanin wannan fad'an na BB da ita yake ba kowaba shi yasa ta dad'a sunkuyar da kanta k'asa uwa wata munafuka...
Har suka bar gidan babu wanda yake k'wak'wk'waran motsi cikin motan haka suka isa gidan su KHALEEL inda zasu soma sabuwar rayuwa da babu MAMA cikinta......
《《》》
'Dakin take k'arewa kallo tana yamutsa face,ko gama shiga d'akin bata yiba ta ji an rufe k'ofan d'akin...
Tab'e baki tayi taci gaba da abunda take na daga yamutsa fuska haka har ta isa bakin mirror en d'akin...
Kan stool en gurin ta zauna tana d'ora kanta kan k'afarta duk ta wani takure kamar wacce take jin mugun sanyi...
Kusan awa guda bata ji motsin kowaba hakan yasa ta sauka daga kan stool en saboda ta gaji da zaman gurin..
Can wani space da ta gani tsakanin closets da bango ta shige ta dad'a takurewa sai yanzun data ga dare yayi sosai wani tsoro ya shigeta duk tunanin gida da MAMA shi yafi damunta,ko wane hali su MAMA suke ciki da sukaji labarin an sace ta...
Wannan tunanin da tayi shi yasata sa kuka mai tsuma zuciya tana yi tana surutai ita kad'ai
"Wayyoo!!! ni shi kenan bazan sake ganin MAMA ba da su ZUHRA,wayyoo!!! Allah sun sace ni ba zasu sake barina naga MAMANA ba"
Tana tsaka da kukan aka turo k'ofan had'e da shigowa,dube-dube ya gamayi cikin d'akin amma bai gantaba kuma dai ya tabbatar da ya kulle d'akin tana ciki....
K'arasa shigowa yayi cikin d'akin bayan jiran da yayi da magana yaji shiru,ya nufi door en toilet amma wayam babu kowa...
Can tsakanin closets da bango ya hango k'afafunta da yake d'akin akwai haske,gurin ya nufa yana mamakin me kuma take yi a nan?
K'arasawa yayi gurin da take da niyyar yin magana sai dai me tun kafin ya isa ya fara jiyo kukanta da ba'a ji sosai sai an matso kusa da ita...
"BEAUTY me ya sameki kike kuka?"......
~Tofa wata sabuwa inji y'an chacha,su ASHNA kuma an koma BEUTY ammafa ba a bakinaba a bakin BIGGY~...
《《》》