Sashe 54
Yar Garuwa Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
"Shekaru sha tara 19 baya,na kasance malamin makarantar islamiyyane kamar yadda kuka ji suna na ABUBAKAR SA'ADU wanda akafi sani da MALAM BUBA,kaf garin nan idan ka tambaya tun daga kan manya da yara babu wanda bai sanniba saboda baiwa da Allah yayimin ta ilimin islama,ta wannan baiwar ne har na samu nake koyar da mutane da dama cikin garin nan namu,a lolacin ina da mata d'aya wacce itace LADIYO,muna zaune da ita lafiya tun bayan aurenmu wanda yake tun na saurayi da budurwa,tsahon rayuwar da mukayi da ita a wannan lokacin Allah baisa tana da rabon haihuwa ba,har muka kai kimanin shekaru goma Allah baisa ko da b'atan wata ta tab'a yiba,a kwana a tashi maganganu sunata yawo a gari kan matata bata tab'a haihuwaba,kai in tak'aice mukuma wasu har samuna suke sunamin magana kan idan na amince zasu bani auren k'annensu wasu suce y'ay'a ga mutanen da suka manyata kenan a wannan gari,gidanmu kuwa wajen mahaifana suma ba a kyale suba da wannan maganar,sai dai na basu hak'uri tare da godiya saboda karramawa da girmamani da sukayi wanda har ya jawo sunamin kyauta mai girma amma ni kuma ban karb'a ba,kwanci tashi asarar mai rai a shekara ta sha d'aya da aurenmu sai nayi wata tafiya zuwa garin DUTSE inda za a gudanar da wata *SEMINER* ta addini,cikin hukuncin Allah bayan zuwana garin duk yinin duniya idan muka gama abunda za muyi a gurin seminer sai mu fita don zaga gari.A wata ranar *LITININ* wacce bana jin zan iya mantawa da ita a iya tsahon rayuwata,kamar kullum mun fito muna zaga gari muka had'u da wata y'ar matashiyar budurwa kyakykyawa da ita,wacce ko ni idan aka bani abun zane ba lallaine na iya zana wacce ta kaitaba bare kuma wacce ta fita saboda kyau da Allah yayi mata sam bata da makusa ta kowane b'angare,nan dai maganganu iri-iri sukaita fitowa daga bakunan abokan tafiyata kan yaba kyau irin nata,jin abun da sukeyi yasa ni dai nayi shiru ban furta komaiba muka ci gaba da tafiya,wani ikon Allah yarinyar tana tafiya a gaba garemu mu kuma muna bayanta kusan duk hanyar data bi to ko muma ita muke bi daga dukkan alamu kuma aikenta akayi,mun biyo wata hanya ne kuma muka ga yarinyar na k'ok'arin shiga gida inda a nan wani mutum daya fara manyanta daga dukkan alamu kuma mahaifintane ya dakatar da ita,babban abun burgewa a tare da ita lokacin data tarar da shi a zaune tun daga nesa da shi kad'an ta cire takalmanta,sannan ta durk'usa ta gaida shi,bayan nan ta shige gida..
Tun daga wannan lokacin naji zuciyata ta kwad'aita da yanayin tarbiyya irin ta wannan baiwar Allah wacce ko sunanta ban saniba bare na tabbatar da nan ne gidansu ko a'a.
Tun daga wannan ranar bamu sake biyo hanyar ba sai da muka kwana uku,sannan a yammaci na hud'u na shirya cikin shiga ta kamala kamar ko wane lokaci na d'auko hanya,ban zame ko inaba sai hanyar da muka gamu da wannan baiwar Allah,ina tafiya ina kuma duba gine-gine da yanayin unguwan har Allah yasa na kawo dai-dai wannan k'ofar gida data shiga,nan ko na samu guri na tsaya ina kuma k'arewa unguwar kallo,layin shiru babu mutane sosai zuwa wani lokaci sai wani yaro daga mak'otansu ya fito nan dai zuciyata ta rayamin na tambayi yaron ko Allah zaisa ya santa,banyi wani dogon tunaniba ko na kira yaron na tambayeshi ko yasan wata a gidan nan?,nan na siffanta masa ita da yanayuita,bud'ar bakin yaro ya furta eh yasanta sunanta *FALMATA* na masa dai y'an tambayoyi wanda bazasu gagara yaro ya amsaba ya bani amsa dai² da saninsa,sannan na zaro murtala na dank'a masa had'e da yi masa godiya,a guje yaron yabar gurin yana murna.Na jima tsaye a gurin kafin na bar unguwar.Tun daga wannan ranar ya zamemin d'abi'a kusan kullum saina je unguwar amma haka zan dawo ba tare da nayi magana da itaba.
Bayan sati uku da faruwar wannan lamari ne kuma muka kammala abunda ya kaimu garin,nan muka shiga shirye-shiryen komawa gida,to kuma a cikin wannan lokacin ne na yanke shawaran tunkarar gidansu da magana ko nasamu nasara ko akasin haka,nan na shirya na ko kama hanyar gidansu,cikin sa'a ina zuwa unguwar tun daga nesa na hango wannan dattijo na ranar farko zaune a k'ofar gida,da sallama na tarar da shi bayan mun gaisa ban tsaya k'wauron bakiba nayi masa bayanin abunda ke tafe dani,nan dai yayi dariya shima mutumin sannan yayimin albishir d'in cewa shi ne mahaifinta,kuma yaji dad'in abunda nayi,sannan ya d'ora da fad'in zai samu yarinyar zasuyi magana idan har ta nuna ta amince to idan kuwa ta nuna akasin haka tofa sai dai nayi hak'uri dan shi kam ba zai mata doleba duk abunda take so shima shi yake so kuma shi zai bata,bayan nan yamin tambayoyi akan inda nake da sana'ata,ban b'oye komaiba na daga abunda ya shafeni na shaida masa,daga k'arshe kuma nayi masa sallama gami da godiya na kama hanyar komawa inda na fito.
Kamar yadda yayimin alk'awarin bayan kwanaki na dawo dan jin yadda sukayi,kuwa na sake shiryawa daga garinmu dan a lokacin mun riga da mun koma gidajenmu,bayan naje mun gaisa da shi ya sanarmin da yadda sukayi,daga nan kuma ya shiga gidan da kansa ya kirawota,mun gaisa da ita bayan nan kuma tayi shiru saboda kunya da take da ko kallona bata iyayi a wannan lokaci,ban b'ata lokaciba na gabatar da kaina a gurinta a matsayin d'an takara na neman aurenta.
In tak'aita muku labari haka soyayya gami da shak'uwa suka k'ullu a tsakaninmu da FALMATA,wanda ba'a d'auki lokaciba mahaifina kafin ya rasu sukaje nemamin auranta,kun dai san yadda ake sa rana a k'auye ba'a d'aukan lokaci kamar na birni su sukan sa lokaci tak'aitacce ne,sun yanke ranar aure watanni biyu masu zuwa,inda kowane b'angare aka shiga shiri,da farko LADIYO bata nuna damuwarta kan auren da zanyi ba ganin yadda mahaifiyata take sonta,bayan auren kuma sai wasu halayya na banza suka fara sako kai cikin al'amuranta wanda da gani kasan zuga ce take aiki a kanta.
Muna zaune da FALMATA lafiya k'alau tun bayan aurenmu da ita da yake ita ba mai magana bace komai nata cikin sanyi take yinsa,wannan yasa ko da ake zugo LADIYO idan ta takaleta da fad'ama bata biye mata sai dai tayi shigewarta d'aki ta barta nan,haka itama zata k'araci masifar fad'anta ta bar gurin,ganin babu nasara sai ta canja salo inda a hankali ta soma jan FALMATA a jiki a gaban kowa tana nuna mata soyayya amma a zuciyarta babu wannan,ganin haka sai mutane suke sha'awar yadda suke zaune da juna,har wasuma suke fad'in ai MALAM BUBA yayi dacen mata na gari babu fad'a tsakaninsu.
Kwanci tashi har muka shafe tsahon shekara aurena da FALMATA amma shiru babu wani labari ganin haka sai hankalin LADIYO ya dad'a kwanciya,ta sake sakankancewa babu su babu haihuwa tunda ga wata nanma na aura amma shiru itama babu labari,haka dai akaita tsegumi da gutsiri tsoma akan nine bana haihuwa,wani hukinci da iko sai ubangiji a cikin shekara ta biyu da aurenmu da FALMATA sai Allah ya azurtata da samun juna biyu wanda babu wani ko wata da ya ankara da hakan da yake babu wani laulayi da tayi,har cikinta ya kai kimanin wata shida,ita dai ajikinta taji chanji wanda mafi yawancin lokaci takan sanarmin amma sai nace mata kada ta damu babu komai,a lokacin data sake sanarmin tanajin abu na mata motsi a ciki sai nake fad'awa iya cewa ga abunda ta fad'a min,bud'ar bakin iya sai tacemin micijin ciki ke damunta,nan ta had'oni da jik'e-jik'en magunguna na gargajiya na kawo mata..."
Nan MALAM BUBA ya dakata yana kallonsu da murmushi a fuskarsa sannan ya d'ora da fad'in
"Kun san wani abun al'abi a cikin wannan labarin?"
Babu wanda yayi magana cikinsu sai dai wasu cikinsu sun kad'a masa kai
"To ku saurara kuji.....Abun da zai baku mamaki shi ne,har cikinta yakai wata tara babu wanda ya gane sai dai ita da kanta ta fuskanci akwai wani bak'on al'amari a tare da ita wanda ganin hakan kuma da tayi baisa ta sanar da kowaba, a lokacin ni kuma nakanje fatauci daga wannan gari zuwa wannan kuma nakan kwashi watanni uku-biyar ban waiwayo gida ba,to kunji dalili kenan daya sa babu wanda ya gane tana d'auke da juna biyu har tsahon lokacin...
Masu iya magana kance "RANAR WANKA BA A B'OYON CIBI" k'warai kuwa haka yake wata ranar alhamis ciwo ya tasammata a cikin d'aki tun cikin dare addu'a kawai take saboda a lokacin bana gari,kuma gidan ya rage daga ita sai LADIYO wacce take nata d'akin daban itama,haka ciwon yake zuwa yana lafawa har dai Allah ya taimaka akayi asuba,a yanda take a haka ta lallab'a tayi sallar asuba,bayan nan kuma gari ya dad'a haske ciwo ya dad'a tadowa fiye da karon farko,tana wannan hali ne Allah ya kawo LADIYO shima zuwa tayi ta dubata ganin bata fitoba,samunta da tayi cikin ciwo wannan yasata hanzarin tafiya gidanmu ta kira mahaifiyata,ko kafin su k'araso gida har Allah ya sauketa lafiya,lokacin da suka shigo basuyi arba da komaiba sai da kukan jaririya nan suka k'arasa da sauri dan ganewa idanuwansu abunda suka ji gaskiyane ko kuwa,da zuwa suka tarar da ita a gefe tana maida numfashi jaririya a gefe tana tsala kuka babu b'ata lokaci iya ta gyarasu duka,tofa a lokacin ne kuma iya taimin aike kan lallai-lallai inzo gida tana son ganina a cikin kwanakin,lokacin da sak'onta ya riskeni banyi wata-wataba na shirya kayana sannan na kamo hanyar dawowa gida.
Bayan dawowata na tarar da wannan abun farin ciki daya sameni,aikuwa nayi murna sosai da ganin wannan kyauta da ubangiji yamin,bayan kwanaki 7 yarinya taci sunan mahaifiyata *KHADIJATUL KHUBRA*,tun daga ranar da FALMATA ta haihu sai LADIYO ta dad'a taso da halayenta na farko ya zamana ko d'akin FALMATA ta daina zuwa,tun kuma ranar data haihu mahaifiyata ta dawo gidan d'akin FALMATA ta tare ta shiga bata kulawa da gyara ta musamman wannan dalilin yasa LADIYO kishi mai tsanani amma sai ta dinga dannewa bata nunawa a fili,sai daifa abunda ke zuciyarta kenan a duk lokacin data bud'e ido taga FALMATA da sabuwar jaririyar ji take kamar ta cinna musu wuta su k'one gaba d'aya kowama ya huta.
Tun daga wannan lokacin naji zuciyata ta kwad'aita da yanayin tarbiyya irin ta wannan baiwar Allah wacce ko sunanta ban saniba bare na tabbatar da nan ne gidansu ko a'a.
Tun daga wannan ranar bamu sake biyo hanyar ba sai da muka kwana uku,sannan a yammaci na hud'u na shirya cikin shiga ta kamala kamar ko wane lokaci na d'auko hanya,ban zame ko inaba sai hanyar da muka gamu da wannan baiwar Allah,ina tafiya ina kuma duba gine-gine da yanayin unguwan har Allah yasa na kawo dai-dai wannan k'ofar gida data shiga,nan ko na samu guri na tsaya ina kuma k'arewa unguwar kallo,layin shiru babu mutane sosai zuwa wani lokaci sai wani yaro daga mak'otansu ya fito nan dai zuciyata ta rayamin na tambayi yaron ko Allah zaisa ya santa,banyi wani dogon tunaniba ko na kira yaron na tambayeshi ko yasan wata a gidan nan?,nan na siffanta masa ita da yanayuita,bud'ar bakin yaro ya furta eh yasanta sunanta *FALMATA* na masa dai y'an tambayoyi wanda bazasu gagara yaro ya amsaba ya bani amsa dai² da saninsa,sannan na zaro murtala na dank'a masa had'e da yi masa godiya,a guje yaron yabar gurin yana murna.Na jima tsaye a gurin kafin na bar unguwar.Tun daga wannan ranar ya zamemin d'abi'a kusan kullum saina je unguwar amma haka zan dawo ba tare da nayi magana da itaba.
Bayan sati uku da faruwar wannan lamari ne kuma muka kammala abunda ya kaimu garin,nan muka shiga shirye-shiryen komawa gida,to kuma a cikin wannan lokacin ne na yanke shawaran tunkarar gidansu da magana ko nasamu nasara ko akasin haka,nan na shirya na ko kama hanyar gidansu,cikin sa'a ina zuwa unguwar tun daga nesa na hango wannan dattijo na ranar farko zaune a k'ofar gida,da sallama na tarar da shi bayan mun gaisa ban tsaya k'wauron bakiba nayi masa bayanin abunda ke tafe dani,nan dai yayi dariya shima mutumin sannan yayimin albishir d'in cewa shi ne mahaifinta,kuma yaji dad'in abunda nayi,sannan ya d'ora da fad'in zai samu yarinyar zasuyi magana idan har ta nuna ta amince to idan kuwa ta nuna akasin haka tofa sai dai nayi hak'uri dan shi kam ba zai mata doleba duk abunda take so shima shi yake so kuma shi zai bata,bayan nan yamin tambayoyi akan inda nake da sana'ata,ban b'oye komaiba na daga abunda ya shafeni na shaida masa,daga k'arshe kuma nayi masa sallama gami da godiya na kama hanyar komawa inda na fito.
Kamar yadda yayimin alk'awarin bayan kwanaki na dawo dan jin yadda sukayi,kuwa na sake shiryawa daga garinmu dan a lokacin mun riga da mun koma gidajenmu,bayan naje mun gaisa da shi ya sanarmin da yadda sukayi,daga nan kuma ya shiga gidan da kansa ya kirawota,mun gaisa da ita bayan nan kuma tayi shiru saboda kunya da take da ko kallona bata iyayi a wannan lokaci,ban b'ata lokaciba na gabatar da kaina a gurinta a matsayin d'an takara na neman aurenta.
In tak'aita muku labari haka soyayya gami da shak'uwa suka k'ullu a tsakaninmu da FALMATA,wanda ba'a d'auki lokaciba mahaifina kafin ya rasu sukaje nemamin auranta,kun dai san yadda ake sa rana a k'auye ba'a d'aukan lokaci kamar na birni su sukan sa lokaci tak'aitacce ne,sun yanke ranar aure watanni biyu masu zuwa,inda kowane b'angare aka shiga shiri,da farko LADIYO bata nuna damuwarta kan auren da zanyi ba ganin yadda mahaifiyata take sonta,bayan auren kuma sai wasu halayya na banza suka fara sako kai cikin al'amuranta wanda da gani kasan zuga ce take aiki a kanta.
Muna zaune da FALMATA lafiya k'alau tun bayan aurenmu da ita da yake ita ba mai magana bace komai nata cikin sanyi take yinsa,wannan yasa ko da ake zugo LADIYO idan ta takaleta da fad'ama bata biye mata sai dai tayi shigewarta d'aki ta barta nan,haka itama zata k'araci masifar fad'anta ta bar gurin,ganin babu nasara sai ta canja salo inda a hankali ta soma jan FALMATA a jiki a gaban kowa tana nuna mata soyayya amma a zuciyarta babu wannan,ganin haka sai mutane suke sha'awar yadda suke zaune da juna,har wasuma suke fad'in ai MALAM BUBA yayi dacen mata na gari babu fad'a tsakaninsu.
Kwanci tashi har muka shafe tsahon shekara aurena da FALMATA amma shiru babu wani labari ganin haka sai hankalin LADIYO ya dad'a kwanciya,ta sake sakankancewa babu su babu haihuwa tunda ga wata nanma na aura amma shiru itama babu labari,haka dai akaita tsegumi da gutsiri tsoma akan nine bana haihuwa,wani hukinci da iko sai ubangiji a cikin shekara ta biyu da aurenmu da FALMATA sai Allah ya azurtata da samun juna biyu wanda babu wani ko wata da ya ankara da hakan da yake babu wani laulayi da tayi,har cikinta ya kai kimanin wata shida,ita dai ajikinta taji chanji wanda mafi yawancin lokaci takan sanarmin amma sai nace mata kada ta damu babu komai,a lokacin data sake sanarmin tanajin abu na mata motsi a ciki sai nake fad'awa iya cewa ga abunda ta fad'a min,bud'ar bakin iya sai tacemin micijin ciki ke damunta,nan ta had'oni da jik'e-jik'en magunguna na gargajiya na kawo mata..."
Nan MALAM BUBA ya dakata yana kallonsu da murmushi a fuskarsa sannan ya d'ora da fad'in
"Kun san wani abun al'abi a cikin wannan labarin?"
Babu wanda yayi magana cikinsu sai dai wasu cikinsu sun kad'a masa kai
"To ku saurara kuji.....Abun da zai baku mamaki shi ne,har cikinta yakai wata tara babu wanda ya gane sai dai ita da kanta ta fuskanci akwai wani bak'on al'amari a tare da ita wanda ganin hakan kuma da tayi baisa ta sanar da kowaba, a lokacin ni kuma nakanje fatauci daga wannan gari zuwa wannan kuma nakan kwashi watanni uku-biyar ban waiwayo gida ba,to kunji dalili kenan daya sa babu wanda ya gane tana d'auke da juna biyu har tsahon lokacin...
Masu iya magana kance "RANAR WANKA BA A B'OYON CIBI" k'warai kuwa haka yake wata ranar alhamis ciwo ya tasammata a cikin d'aki tun cikin dare addu'a kawai take saboda a lokacin bana gari,kuma gidan ya rage daga ita sai LADIYO wacce take nata d'akin daban itama,haka ciwon yake zuwa yana lafawa har dai Allah ya taimaka akayi asuba,a yanda take a haka ta lallab'a tayi sallar asuba,bayan nan kuma gari ya dad'a haske ciwo ya dad'a tadowa fiye da karon farko,tana wannan hali ne Allah ya kawo LADIYO shima zuwa tayi ta dubata ganin bata fitoba,samunta da tayi cikin ciwo wannan yasata hanzarin tafiya gidanmu ta kira mahaifiyata,ko kafin su k'araso gida har Allah ya sauketa lafiya,lokacin da suka shigo basuyi arba da komaiba sai da kukan jaririya nan suka k'arasa da sauri dan ganewa idanuwansu abunda suka ji gaskiyane ko kuwa,da zuwa suka tarar da ita a gefe tana maida numfashi jaririya a gefe tana tsala kuka babu b'ata lokaci iya ta gyarasu duka,tofa a lokacin ne kuma iya taimin aike kan lallai-lallai inzo gida tana son ganina a cikin kwanakin,lokacin da sak'onta ya riskeni banyi wata-wataba na shirya kayana sannan na kamo hanyar dawowa gida.
Bayan dawowata na tarar da wannan abun farin ciki daya sameni,aikuwa nayi murna sosai da ganin wannan kyauta da ubangiji yamin,bayan kwanaki 7 yarinya taci sunan mahaifiyata *KHADIJATUL KHUBRA*,tun daga ranar da FALMATA ta haihu sai LADIYO ta dad'a taso da halayenta na farko ya zamana ko d'akin FALMATA ta daina zuwa,tun kuma ranar data haihu mahaifiyata ta dawo gidan d'akin FALMATA ta tare ta shiga bata kulawa da gyara ta musamman wannan dalilin yasa LADIYO kishi mai tsanani amma sai ta dinga dannewa bata nunawa a fili,sai daifa abunda ke zuciyarta kenan a duk lokacin data bud'e ido taga FALMATA da sabuwar jaririyar ji take kamar ta cinna musu wuta su k'one gaba d'aya kowama ya huta.