← Book details Yar Garuwa Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 30 OF 86

Sashe 30

Yar Garuwa Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Zaune take cikin parlor ta hard'e k'afafunta d'aya akan d'aya,ta cije leb'e ta gama cika tamkar zata fashe...
Iska ta furzar mai d'umi tare da fizgo wayarta tana latsawa cikin fusata take magana..

"Haba BIGGY sau nawa zan sanar maka da ina nemanka,ko kuwa so kake sai raina ya gama yin duhu kafin ka zo?"
'Dan dakatawa tayi tana sauraren me zai fad'a

"To amma me yasa baka sanarmin da bakwa garin nanba ka b'oye??"

"Tuba nake ranki ya dad'e amin aikin gafara"

"Shi kenan amma magana nake son yi da kai mai matuk'ar muhimmanci,wanda bana son kowa ya sani,bayan ni da kai sai kuma yaranka,ka dai fuskanci me nake nufi ko?"

"Ehhh!HAJIYA amma idan babu damuwa kiyi maganarki yanzun kawai saboda bana son zuwa gidanki saboda tsaro...
Idan kuma wani aiki nema kiyi min bayanin yadda kike so ya kasance,za ayi miki duk abunda kike buk'ata"...

Jin furucin BIGGY ne yasa ta sakin murmushin mugunta kafin ta fara magana
"Toh! shi kenan,amma da san samu ne da ka zo gida ka same ni idan ya so sai muyi maganar,amma tunda ka sanarmin uzurinka na karb'a hakanma babu damuwa"....

Sai da tayi shiru na wasu y'an lokuta sannan ta soma magana
"Ka san me nake so da kai BIGGY?"

Daga gefensa ya amsa mata da fad'in
"A'a HAJJAJU"

"Ina son duk inda kuke ku je gidan dana saku aiki kwanakin baya,akwai wata yarinya da nake son ku satomin,amma idan kun sace ta kuyi nesa da ita bana son kuma a samu matsala kan wannan aiki,ina son kafin ku satota kuyi bincike sannan kuma ku tabbatar da babu wanda ya ganku...
Zan turo maka da photon yarinyar da zaku sato sannan ku tabbatar idan kun saceta kun sanar da ni a lokacin bayan kun d'aukota...
Ina fatan ka fuskance ni ko?ni kuma zanyi maka bayanin abunda zakuyi bayan nan,da fatan baka manta kwatancen gidanba"...

Dariya BIGGY yayi mai isarsa kafin yayi magana
"Amma HAJIYA ba dai yarinyar da muka sace ce ta dawo ba ko?"

"A'a wannan daban da waccan,wannan da nake son ku sato ina son 'DAUKAR FANSA ne akan mahaifiyarta,saboda ta nunamin ban iyaba shi yasa nake son ajiye mata DARASIN RAYUWA"....

"An gama ranki ya dad'e kamar anyi an gama wannan aikin,za muyi duk yadda kikace"
Sai da suka gama kitsa duk wata mugunta sannan sukayi sallama...

Zuciyar HAJIYA LAURA fal da farin cikin wannan al'amari tana zaune tana kad'a k'afa sai sakin murmushin mugunta take.......
_AYI DAI MU GANI...._

《《》》

*3 MONTH LEAP.*

KHUBRA ce rik'e da kuran ruwanta na sana'ar *GARUWA* k'afarta sanye cikin takalmin *FILLO SHOES* daga saman kanta ko ta kifa *HAT* na gargajiya,takalmin duk ya sha d'inki saboda gajiya da yayi..

Wani yaro ne ya gifo a guje daga wani k'aramin gida yana fad'in
*"Y'AR GARUWA* ki kawo ruwa gidanmu za a siya"

A hanhali taja hulan dake kanta baya kad'an tana kallonsa,fuskanta da d'an fara'a duk da yadda tayi duhu fatarta duk tayi wani iri abun tausayi...
"To amma zo nan"
Ta umarci yaron da yake shirin komawa a guje,jin ta kira shi ne ya matso..
Kunnensa ta d'an kama a hankali tana fad'in
"Suna nane baka saniba ka kirani da *"Y'AR GARUWA"* ko kuwa iskanci ne yasa kayi hakan?"

"A'a na sani"
Ya fad'a yana dafe gefen fuskarsa ta side en da ta rik'e kunnensa....

"Daga yau naji ka sake fad'in wannan sunan sai na mareka,kaji ni ko?"

Da sauri yaron ya gyad'a kansa alamar yaji kuma ya bi...

"Yawwa k'anina,maza to ungo wannan"
Ta sa hannunta cikin jakar dake d'aure jikin west enta ta fiddo da sweet....
Da murnansa ko ya karb'a yana tsalle,yana fad'in
"Daga yau idan ban sake fad'a ba zaki dinga bani alawa?"

"K'warai kuwa zan dunga baka"

"YEEEE!ya" fad'a yana tsalle "Idan zaki dinga bani har YAYA zan dunga ce miki kinji ADDA KHUBRA"

Murmushi KHUBRA tayi tana shafa kansa cikin so da kulawa..
"Maza to jeka gida gani nan zan kawo muku ruwan kaji?"
A guje ya juya ya shige gidan cike da murna...

Tana kallon shigewarsa ta d'an tsaya tana murmushi ita kad'ai tasan halin da ta shiga lokacin da taji yaron ya kirata da ADDANSA,wani siraran hawaye ne yayi layi akan fuskanta,da kyar ta tsaida hawayen nata tana mai goge su.......

~Ni da nake gefe cike da tausayin halin da take ciki "nace KHUBRA har yanzun kina nan da halinki na son kuka"...~
~My HULBATEEY kuwa hawaye naga tana sharewa kan tsananin tausayin yadda taga KHUBRA ta koma....~

*_~KEEP FOLLOWING FAN'S....~_*

*~TEAM KHUBRA.~*

*_REAL SMASHER._*
💠

*Y'AR GARUWA......*
*(ɬɧɛ mơʂɬ ɧɛąrɬ ɬơųcɧıŋɠ ʂɬơrყ).*

🕊🕊🕊🕊
🌹🌹🌹

*©®2018*
*24/ʝųŋɛ,2018*

*ʂɬơrყ ąŋɖ wrıɬɛɛŋ*
*ცყ*
_HAWWA M.U {$мaѕнer}_
🕊🕊🕊🕊🕊
🌹🌹🌹🌹

_BISMILLAHIR-RAHMANIR-RAHEEM..._
*~________________________~*
_Wannan page tukuici ne gareku masoyana tabbas ina jin dad'in kasancewa tare daku kuma ina jin dad'in addu'o'inku gareni Allah ya bar k'auna,jinjina gareku *Fatima Ibrahim,Fatima Zois,Fateema 🌹, Fatima M.D* dama duk wani/wata masoyin/masoyiyar *SMASHER* wollah ina matuk'ar k'aunarku har cikin jini da b'argona nake jinku,Allah ya bar k'auna,ina godiya sosai da sosai,ina yinku irin *#TOTALLY* en nan...*SMASHER* tace ana *_~#ANA MUGU MUGUN TARE..*_~_

*~________________________~*

_*AYSHA B 《AESHAB》* wollah muma muna yinki kuma muna sonki,ki jima kiyi k'arko cweety Allah ya bar k'auna *SHDG* na godiya sosai bisa karamconki garesu.._
*~________________________~*
_Masoya muna buk'atar ku tayamu addu'ah DURLING SIS babu lafiya,fatan zaku dubi buk'atarmu...Allah ya tashi kafad'unki cweet HUBBEEY._
*~________________________~*

*DEVOTED TO:*
_BILKISU M.ADAM (Y'AR ABBA)_

*BESTOWED TO:*
_MURJA SALIS (NA'IKKE)._

*AND*

_FATIMA ABUBAKAR (FATEEY AFIRST)._

*3⃣3⃣*

*D* a kyar ta iya saita nutsuwarta ta kama hanyan shiga gidan da yaron ya fito d'azun,hannunta d'auke da robber 25 litters...
Da sallama ta shiga gidan,bayan sun gaisa da matar gidan ta shiga juye ruwan da ta kawo cikin mazubin da aka nuna mata,bata kai da gama abunda ya kaita ba,ta jiyo yaron nan yana fad'in
"Inna kinga alawana da ADDA KHUBRA ta bani d'azu"

Y'ar yank'wananniyar matar da aka kira da inna ta kalli yaron tana d'an murmushi
"Aaaaaa!aikuwa angode,Allah ya saka da alkhairi.....
Ina fatan dai kace ka gode ko?"

"Laaaa!inna na manta ban fad'aba"
Yaron ya fad'a yana rufe bakinsa da hannu..

Ran inna ne ya b'aci jin furucin yaron dake gabanta,cikin fushi² ta janyo rigarsa
"Sau naw nake fad'a muku duk wanda zai muku kyauta ku dinga cewa an gode,ko ban fad'a muku ba?"

"Dan Allah inna kiyi hak'uri wallahi mantawa nayi"
Kamar zaiyi kuka yake maganar

"Aii ba dainawa za kuyi ba,ina jin saina fara k'wacewa zaku shiga hankalinku,tunda bakwajin magana"

"Wollahi inna bazan k'araba"

"Maza wuce kace mata ka gode,kafin na sab'a maka"

Da gudu yaron ya matso kusa da KHUBRA dake shirin fita yana fad'in
"An gode ADDA KHUBRA"

Batayi magana ba sai murmushi da tayi kad'ai ta d'aga masa hannu,daga haka tayi waje tana sha'awar halayyan matar na ganin yadda tayi tarbiyyan yaranta.....

《《》》

Tun daga wannan lokacin da BIGGY suka yi magana da HAJIYA LAURA suke observation a unguwan na RIJIYAR ZAKI dai² area'n gidan na HAJIYA MURJA...
Sai dai da yake suna da wasu ayyukan na daban a kuma gurare da dama yasa har aka d'auki lokaci mai tsayi ba tare da sun gudanar da aikin da aka sasu ba....

Kamar wani mahaukacin gaske haka yake acting ta yadda kowa ya ganshi ba zai iya ganewa ba cewa mahaukaci ne na gaske ko kuwa na bogi ne?....

Haka yake zagaye line en tun asuba daya shigo cikin unguwan yanata buge² da son korar flies dake neman hawan masa fuska,a k'ok'arinsa na tabbatar da cewa shi mahaukaci ne,kayan jikinsa duk sun yage bayaga wata annakiyar daud'a da duk tabi jikin kayan ta lafe kai ka rantse dama a jikin kayan aka halicceta....

《《》》

Tun bayan wattani uku da suka wuce ne kuma al'amura suka tsaya cak,zuwa wannan lokaci gaba d'aya binciken da ake dangane da b'atan KHUBRA abun ya faskara a kamo bakin zaren,wannan dalilin ne yasa aka fawalla komai duk wasu lamura an mik'asu ga Allah...
Ta inda BB yaq sallami Sergeant da suke masa aiki ta inda suka koma ma'aikata suka ci gaba dqa aikinsu kamar yadda dama suke yi....

A dai² wannan lokacin ne kuma MAMA taso b'allowa BB ruwa akan lallai itafa tana son yayi aure duk dan ta mantar da shi maganar KHUBRA....
Jin maganar ta MAMA yasa shi neman mafita babu shiri dan kam tabbas tunda wannan al'amarin ya faru baya jin akwai wata y'a mace da ta isa ya kalleta bare har ya furta mata kalmar soyayya....

Cikin kwanaki k'alilan ya gama shirinsa cikin sirri babu wanda ya sanarwa zai yi tafiya...
Washe gari da safe ya shigo cikin sauri,a parlor suka had'u da ZUHRA tana fitowa daga kitchen...

"Yawwa CWEETY ansa wannan"
Ya mik'a mata leda en dake hannunsa
"Maza ki adana shi naki ne kinji ko?"

"Toh BB nah na gode Allah ya k'ara arzik'i"
'Dan murmushi yayi daga nan ya bar gurin yayi hanyan bedroom,abunda yasan yana da muhimmanci na daga documents ensa da visa en da yayi na barin k'asan ya d'iba ya gama sasu a envelop yana gama had'a kayan ya maida car keys ensa cikin drawer daga haka ya fito yana kulle d'akin....

Bedroom enta ta shiga da yake sauri take ta shirya time en tafiyansu school ya k'arato ne yasa ko bud'e ledan bata tsaya yiba ta sa cikin closet enta ta rufe....

MAMA na zaune cikin parlor su ASHNA suka fito cikin shiri zasu tafi school,lokacin suna mata sallama,daga haka suka fice cikin sauri dan time en suna gaf da makara...

Duk da ba flight en safe zaibi ba,yana son fita ya je gurin KHALEEL daga nan yake son wucewa,a tunanin BB yin hakan kad'ai shi ne mafita a tare da shi...
Da sauri shima ya fita lokacin har sun kaiga mota da driver zai kaisu,sai dai me suna zuwa driver'n yake shaida musu motan yayi faci kuma yanzun masu faci basu fitoba...

Yana gama maganan su ASHNA suka fice ita da ZUHRA,FATAHIYYA da KHALEEFA....
Ganin sauri suke ne yasa ZUHRA maida HANEEF ya sanar da MAMA abunda ke faruwa,komawa cikin gidan yayi da gudunsa ya fad'awa MAMA matsalan da aka samu,kamar yadda ZUHRA ta fad'a masa..

"Toh ai kuwa idan haka ne sai dai kuyi saurin tafiya ku samu NAPEP dan kada ku k'ara makara"...
Chapter 30 · 0% Book details