← Book details Yar Garuwa Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 44 OF 86

Sashe 44

Yar Garuwa Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Tun kafin ya k'arasa ta fashe da kuka tana fad'in
"Ni dama nasan hakan sai ya faru,wayyoo Allah MAMANA dan Allah kada ki mutu ki barni,wayyoo MAMA dan Allah ki tsaya"
Surutai iri-iri take wanda bata iya tantance kalmomin da bakinta ke furtawa..

A hankali BIGGY ya matso kusa da BABA yana tambayansa
"BABA wane asibiti ne aka kwantar da ita?"

"Ehhh tana asibitin MALAM AMINU KANO"
BABA ya bashi bayani hatta da d'akin da take a kwance sai da ya musu kwatance,cikin sauri ya figi hannun ASHNA da batama cikin nutsuwarta suka d'auki hanyan asibitin AKTH....

《《》》

Dai² lokacin da suke tsaka da murnan tashin MAMA cikin sauri KHALEEL da BB suka fice dan nemo likita.
Suna cikin d'akin duk sun baibayeta kowa nason ya mata magana,idanunta taketa juyawa tana kallonsu d'aya bayan d'aya.

K'ofar aka bud'e da k'arfi cikin sauri duk suka maida hankali gurin dan ganin waye haka ya dokota da k'arfi.
Abunda suka gani ne yasa su kowa ya bud'e baki da tsantsan mamaki shimfid'e a fuskokinsu...................

*~#TEAM KHUBRA.~*

*_#REAL SMASHER._*
💠

*Y'AR GARUWA......*
*(ɬɧɛ mơʂɬ ɧɛąrɬ ɬơųcɧıŋɠ ʂɬơrყ).*

🕊🕊🕊🕊
🌹🌹🌹

*©®2018*
*11/ʝųlყ,2018*

*ʂɬơrყ ąŋɖ wrıɬɛɛŋ*
*ცყ*
_HAWWA M.U {$мaѕнer}_
🕊🕊🕊🕊🕊
🌹🌹🌹🌹

_BISMILLAHIR-RAHMANIR-RAHEEM..._
*~________________________~*

*DEVOTED TO:*
_BILKISU M.ADAM (Y'AR ABBA)_

*BESTOWED TO:*
_MURJA SALIS (NA'IKKE)._

*AND*

_FATIMA ABUBAKAR (FATEEY AFIRST)._

*4⃣2⃣*

*'D* akin ya afka ba tare da yayi sallama ba yana muzurai had'e da dubawa ko zai ganota cikin d'akin,amma babu kowa ciki sai LADIYO data mik'e saman gado tana faman shirgar bacci uwa wacce ta sha wani abun.
Wata irin tsanarta ce ta dirarwa MALAM BUBA take ya juya ba tare da yayi magana ba,ficewa yayi daga gidan yana ta taraddadin ina yarinyar tasa ta shiga haka.
Abubuwa da dama yake tunani akansu da suka faru dashi a y'an watannin da suka wuce wad'anda basu da dad'in ji bare a fad'esu.
Dai² bakin wata makarantar primary dake k'auyen ya nemi guri ya zauna nan ya shiga tunanin inda ta shiga da halin da take ciki.
Rana ta k'arshe da suka rabu ta fad'o masa da abunda ya janyo rabuwar tasu,kuka ya fashe da shi yana tausaya mata yasan wahala kam da tsanani tana cikinsu a dai² lokacin.
Babu mai rarrashinsa sai da yayi mai isarsa sannan ya tsagaita shi kad'ai yake magana da kansa
"Allah kaga halin da bayinka suka tsinci kawunansu ya Allah kaine gatanmu bamu da kowa idan ba kaiba,gareka muke neman taimako ya Allah ka k'ara tsaremu a duk inda muka tsinci kawunanmu,Allah ina rok'onka daka tsaremin yarinyata a duk inda take a kuma kowane hali take ciki"
Ya jima yana addu'a har sai da yaji zuciyarsa tayi sanyi daga mugun zafin da take masa sannan yayi shiru na wasu y'an mintuna bakinsa kuma har lokacin yana motsawa babu abunda da ke fitowa daga bakinsa face
"Astagfirullah wa'atubu ilaih,astagfirullahal azeeym"
A dai² lokacin ba komai MALAM BUBA yake tunawa ba sai wani al'amari daya tab'a faruwa shekaru sha tara da suka wuce wanda sune dalilin da yasa yaketa neman gafara,a zuciyarsa yake fad'in
"Lallai ya zamemin wajibi na nemeki ko dan neman gafara,a yau Allah ya nunamin abunda ko a mafarki banyi tsammaniba tare da LADIYO,lallai wannan ya tabbatarmin da *BA LAIFINKI BANE"*
Wuni guda yana zaune a gurin sallah kad'ai ke tada shi shima da yayi alwala a bakin tap en dake farfajiyar makarantar zai dawo saman varenda a nan zaiyi sallah sannan yaci gaba da zama yana dad'a neman gafarar mahalicci visa kuskuren da yayi shekaru da dama....

《《》》

K'ofar da aka doko ne da k'arfi yaja hankulansu suka kai dubansu ga k'ofan dan ganin waye haka,kallon ASHNA sukayi wacce idanunta suka gama rinewa saboda tsabar kukan da tayi kafin su iso.
Mik'ewa sukayi bakin kowanne na rawa gurin furta sunanta,MAMA dake kwance tsawon kwanaki ko kanta bata san inda yakeba,ganin ASHNA a gabanta dai² lokacin ta mik'e zaune had'e da zare abunda ke bakinta cikin murya k'asa-k'asa ta furta
"ASHNA kece zo nan y'ata naji d'umin jikinki kinji y'ata zo maza"

Gaba d'ayansu suka kuma juyawa jin maganar MAMA,zaune suka ganta saman gadon da suka barta a kwance,mamaki fal cikin zuk'atansu had'e da farin ciki mara misaltuwa.
Da gudu ASHNA ta k'arasa kusa da MAMA,fad'awa tayi jikinta ta saki wani kuka mai ban tausayi kowa sai matse ido yake,hannu MAMA tayiwa KHUBRA alama da tazo kusa da ita,babu musu kuwa ta isa kusa da ita,kamata tayi ta rungume idanun MAMA na fidda hawaye,abun ba k'aramin mamaki ya bawa UMMI,ZUHRA,FATAHIYYA da suke cikin d'akinba farin ciki mara misaltuwa a tare da su,a hankali ZUHRA ta isa kusa dasu tasa hannunta a bayansu itama ta kwantar da kanta bayan ASHNA da KHUBRA tana fidda hawayen jin dad'i.
Muryan MAMA ya katse musu kukan da suke
"Ku yafe min yarana dan Allah badan ni ba,nasan na cutar da ku na kuma b'ata muku rayuwa ban bi nasiha da kuma burin mahaifinkuba kamar yadda ya barmin wasiyyar kula da kuba,kuyimin aikin gafara in sha Allah haka bazai k'ara faruwaba...
KHUBRA ki gafartamin cutar dake da nayi,sanadin haka abubuwa suka sake cukurkud'ewa idan har baki yafemin ba ni kaina bazan tab'a yafewa kainaba"..
Kuka ne yaci k'arfin maganar MAMA,inda kafin taci gaba da magana DR ya shigo had'e da sallama bayansa kuma BB ne da KHALEEL,tun kafin DR en yayi magana wasu dattijai suka shigo,nanfa aka fara kallon-kallo tsakaninsu da MAMA dake zaune gefenta kuma ASHNA da KHUBRA ne sai ZUHRA dake kusa da k'afafuwanta.
Shi kansa DR en ganinta a zaune sai da abun ya matuk'ar bashi mamaki,baiyi tsammanin ganin hakan a tare da itaba amma sai ya bar hakan a ransa
Wayansa ya shiga pressing sannan ya d'orata a kunnensa
"Hello DR LEEMA idan babu abunda kike yi ina son ganinki yanzun"
Abunda ya fad'a kenan sai number room en da ya shaida mata,cikin y'an mintuna akayi knocking door en,izinin shigowa aka bata ta shigo d'akin dake cike da mutane,nan DR en ya basu umarnin su basu guri yana son ya duba jikin nata.
Ficewa sukayi gaba d'aya ya rage daga shi sai DR da kuma MAMA dake zaune har lokacin,da taimakon DR LEEMA suka duba jikin nata inda suka tarar da komai normal,bayan sun gama suka fice,a k'ofan d'akin ya tarar da su nan ya buk'aci ganinsu.

"BABA ina ganin ku yafi kamata da ku je don ganawa da likita dan dama ya buk'aci hakan tun kwanakin da suka gabata"

"A'a KHALEEL ku en dai kuje tunda kun san dalilin faruwar rashin lafiyar tata,kuma kune y'an boko saboda haka ina ganin zaku fimu fuskantar abunda zai fad'a"

'Dan murmushi yayi had'e da fad'in
"To shi kenan BABA amma tunda Allah yasa abun yazo da haka me zai hana muje gaba d'aya,daga nan maji koma mene ya faru da dalilin afkuwar hakan"

'Dan murmushin shima OLD KHALEED yayi sannan ya kama hannun BB yana fad'in
"Takwara muje ko?"
Wucewa sukayi zuwa office en inda da shigarsu suka nemi guri suka zauna suna masu sauraron abunda zai fito daga bakin DR.
Shiru ne ya biyo baya na tsawon wasu mintuna,kafin DR ya sanar musu da yadda jikin nata yake a halin da ake ciki
"To yanzu DR nan da zuwa wane lokaci zaku sallameta?"
KHALEEL ya tambaya
"Ehh to duk da jikin nata sa sauk'i sosai a yanzun zamu rik'eta a nan har nan da tsawon kwanaki biyu zuwa uku".

《《》》

Likkafa taci uban na da a gurin MA'U dan ko tun bayan da likita ya tabbatar mata da babu matsala ta sake kafa sabon kasuwanci da yafi na da a yanzu MA'U da mutane suka sani a baya wannan har ta dame waccen a rashin mutunci da duniyanci,idan abun nata ya motsa mata kwana biyu sai ta haukace yini take tana kan network babu sassauci,su da kansu mazajen nata suna mamakin wannan sauyi nata a y'an kwanakin da hakan ya faru....

Mu dai sai muce Allah ya kyauta na gaba...

《《》》

Kwanaki sun dad'a tafiya inda zuwa yanzun MAMA ta dawo gida kamar ba itace tayi jinyan da bata iya sanin duk wanda ke kantaba.
Yau ta kama kowa da kowa yana gida hatta da su BABA KHALEED da suka zo daga JIHAR JIGAWA,gaba d'aya suna zaune bayan gaishe-gaishe da akayi da tsokanar juna,MAMA ta kalli duka jama'ar gurin sannan ta fara magana wanda sai da taja hankulan jama'ar dake gurin gaba d'aya
"Da farko kafin na fara cewa komai ina buk'atar neman yafiyarku saboda wasu abubuwa da suka faru wanda a dai² wannan lokaci nake mai burin sanar daku GASKIYAR AL'AMARI'N da ya faru shekaru bakwai da suka faru"
Labarin yadda suka rabu da ABBA'NSU BB ta shiga badawa tun daga lokacin da suka fara samun sab'ani har zuwa lokacin da ya bar garin,da yadda suka had'a baki ita da HAJIYA LAURA kan cewa da mutane mutuwa yayi,duk dan gudun kada duniya ta zagesu,gaba d'ayan parlor'n sunyi shiru kowa da abunda ke damunsa da jin wannan al'amari mai matuk'ar rikitarwa da d'aure kai musammanma su BABA KHALEED da basu san da wannan labarinba,shiru mutanen parlor'n sukayi suna jiran jin me kuma zai dad'a fitowa daga bakin wani a gurin.

Shiru zuwa tsayin lokaci da haka taron ranar ya watse ba tare da wani ko wata sun sake furta wani abuba saboda zuciyoyinsu na cike da alhini.

Bayan tashinsu daga gurin BB tare da KHALEEL suka fice,basu zame ko inaba sai guarding inda suka zauna saman kujerun dake gurin,shiru na d'an lokaci sukama juna kowa na tunani duk da a gurinsu wannan maganar ta MAMA bata wani sasu jin shock kamar sauran mutanen dake parlor'nba kasancewar sun riga da sun san da ita,sai dai a wannan karon suna tunanin mafitane.

Bayan shud'ewar mintuna arba'in suna zaman kurame ba tare da wani yayi magana ba da sauri BB ya kalli KHALEEL
"Heyyy!MAN ka san me nake tunani kuwa?"

Kai KHALEEL ya kad'a masa

"Ina tunani ne akan b'acewar ABBANMU gaskiya inaji a jikina babu wanda yasan inda ABBA yake face ABBANKA"
Shiru duka sukayi suna kallon juna da sauri sukayi ihu had'e da k'ank'ame juna
"Tabbas!kayi gaskiya duk duniya ABBANA ne kad'ai zai iya sanin inda yake,amma me yasa bamu yi wannan tunaninba tun farko sai yanzun???"

"Wallahi dai kam MAN na manta ne tun farko,kuma kaima bakayi tunanin hakaba ko?"
Chapter 44 · 0% Book details