Sashe 8
Kirjin Mai Hankali Part 2 Complete Hausa Novel · about 8 min read
"Toh Alhamdulillah... Allah abun godiya. Ubangiji Allah Kuma ya bayyana su zaytunah yasa suna cikin koshin lafiya. Komai yazo ya wuce. Dukkanin abunda akayi mata da yaranta Allah yasa ya karye. Suma su waiwayi yan uwa. Allah ya datar damu"
"Aameen Gwaggo. Allah bakiji gabana yadda yake faduwa ba. Amman yadda komai ya wuce na yau da mike tunanin zai faru komai yazo da sauki. Sai na samu nutsuwa da kwanciyar hankali. Ina Kuma fatan Allah ya bayyana su zaytunah da gaggawa yasa suna cikin aminci. Wannan munafiki ko munafaka da suke turawa Alhaji Amiru wannan Sako Kuma Allah ya bayyana mana su. Ya tarwatsa Shirin su duk me hannu aciki"
"Aameen Yaa Rabbi dawuda, Allah yayi maka albarka, Allah yayi maka albarka , Allah ya maka albarka"
"Aameen gwaggo na.. Ubangiji Allah ya Kara miki tsawon kwana da yalwar afuwa, lafiya mai inganci, ya yi riko da hannuwan ki. Yasa ki gama da duniya lafiya"
"Aameen dawuda. Tare da Kai da sauran musulmai baki daya"
Da wannan suka koma cikin gidah su na kambama mutunci da dattako na zuriyar gwaggo zainabu da gwaggo zainabun kan ta...
_1-KALBIM:MAMUH GEE_
_2-KIRJIN MAI HANKALI (AKWATIN SIRRIN SA):MSS XOXO_
_3-ADUNIYATAH :HUGUMAH_
_4-AJIYA A DUHU: BILYN ABDULL_
°°
_1-BOOK DAYA:DARI BIYAR_
_2-BOOKS BIYU:DUBU DAYA_
_3-BOOKS UKU: DUBU DAYA DA DARI BIYAR_
_4-BOOKS HUDU :DUBU BIYU_
_5_YAN NIJAR: 1000CF: 89825722 NOUSAIBA LAWALI MARADI_
_ku tura receipt zuwa ga 09033181070_
*IDAN KATI NE A TURO TA WANNAN NUMBER:*
*09032345899.. SHEDAR KATIN MA NAN ZAA TURA. KATIN MTN!!MTN!!*
____
*KIRJIN MAI HANKALI*
_(Akwatin sirrin sa)_
_🧳👩❤️👨🌺_
*_The Vault Of His Secrets_*
_®️NANA HAFSATU (MX)_
_©️ZAFAFA BIYAR WRITERS_
*_BOOK TWO_*
_PAGE:8_
Hajiya Rumanah ta jingina da kujerarta, zuciyarta na bugawa da sauri. Idanunta sun kada, cikinta kamar yana kuna da wutar da ba ta da iyaka. Tunani ne ya cika zuciyarta, yana tsunduma ta cikin rudani mai tsanani. Shin da gaske Muhammad yaron nan yana son auren Nabeeha? Kuma wai ita Nabeeha ‘yar waye a hakikanin gaskiya?
Ta saki numfashi a hankali, sannan ta mika hannu ta dauki wayarta daga gefenta. Ta dade tana kallon fuskar wayar kamar wacce ke shirin daukar matakin da ba ta da tabbas a kansa. Sai kuma ta bude sabon sakon rubutu, ta danna lambar da take bukata. Hannunta yana kadawa yayin da take danna rubutun,
“Muhammad dan wajen Amiru, wacece yarinyar da yake son aura dagaske? Nabeeha ce?”
Ta yi shiru na dan lokaci, tana kallon sakon da ta rubuta. Sai ta kara danna wasu kalmomi,
“Kuma ina so na tabbatar, wacece ita a hakikanin gaskiya? Ita ‘yar Major General Dawud ce?”
Bayan ta gama, ta danna send. Wayarta ta koma hannunta, amma zuciyarta ta kasa samun kwanciyar hankali. Bata dade da aika sakon ba, sai ga amsa ta shigo. Ta yi saurin dannawa, zuciyarta na bugawa da sauri.
"Nabeeha 'yar Hajiya Zaytunah ce, dake gidan Major General Dawud. Amma ba 'yar Major General Dawud bace."
Hajiya Rumanah ta zaro ido, wani irin jiri ya kwasheta. Gabanta ya fadi, hannunta ya soma rawa, ta saki wayar tana duban su Hajiya Karama da Hajiya Ladi da ido waje.
“Subhanallah! Kenan…” Ta kasa karasawa, sai ta dafe kanta, zuciyarta kamar zata faso kirjinta ta fito.
Hajiya Karama ta matso kusa da ita, tana kokarin lallashinta.
“Rumanah, ki kwantar da hankalinki. Me ya faru? Me suka ce?”
Hajiya Ladi ta dan matsa kusa da ita itama, fuskarta dauke da damuwa.
“Ki fada mana! Me ya sa kike cikin wannan tashin hankalin?”
Hajiya Rumanah ta runtse idanu, ta dafe goshinta da hannu daya, sannan ta furta da kyar,
“Nabeeha ba ‘yar Major General Dawud bace…”
Hajiya Karama da Hajiya Ladi suka zaro ido a tare.
"Me kike nufi?"
Hajiya Rumanah ta bude idanu, tana kallon su da tsananin firgici.
“’Yar Hajiya Zaytunah ce! Kuma tana gidan Major General Dawud ne… Amma ba ‘yar sa bace!”
Shiru ya biyo baya. Zuciyoyinsu sun cika da mamaki da firgici. Hajiya Ladi ta yi saurin fadin:
“Haba Rumanah! Wannan ba zai yiwu ba. Kin tabbata? Wannan bayanin ba kuskure bane?”
Hajiya Rumanah ta kada kai, hawaye na taruwa a idonta. "Ban san me ke faruwa ba… Amma idan haka ne, to lamarin ya fi yadda muke tunani. Wannan matsala ce babba!"
Hajiya Karama ta dafe kirjinta, tana kokarin kwantar da nutsuwarta. “Dole ne mu samo mafita da wuri. Kada mu bari wannan ya bata mana shiri.”
Amma Hajiya Rumanah ta kasa samun nutsuwa. Duk yadda suka so su lallasheta, tunaninta ya tafi nesa. Idan har Nabeeha ba ‘yar Major General Dawud bace, Toh ta tabbata yar Hajiya Zaytunah ce kenan... Zuciyarta ta sake harbawa da karfi…
Hajiya Rumanah ta kasa zama. Ta tashi tsaye, tana safa da marwa a cikin dakin, zuciyarta tana tafasa kamar ruwan dafawa. Idanunta sun kada, tana huci kamar wacce aka yi wa dukan tsiya.
"Wannan ba zai yiwu ba! Nabeeha 'yar Zaytunah ce? Amma me hakan ke nufi? Me yasa take gidan Major General Dawud? Yaki ya fito da ita. Shine gaskiar lamarin ne ko kuwa?"
Hajiya Ladi ta gyara zaman mayafinta, ta dubi Hajiya Karama da fuskar da ke bayyana damuwa.
"Yanzu, Rumanah, yaya za a yi?" Ta tambaya da karyayyen murya.
Hajiya Karama ta numfasa, ta saki wani murmushin dole.
"Ba mu da wata mafita illa mu sake duba lamarin da kyau. Mu tabbatar da gaskiyar al’amarin kafin mu dauki wani mataki."
Amma Hajiya Rumanah ta juyo da sauri, ta daga murya.
"Karama! Da me za mu sake duba lamarin? Ai an riga an tabbatar! Idan har Nabeeha 'yar Zaytunah ce, to tabbas muna cikin matsala! Me ya sa ba wanda ya gaya mana? Me yasa har yanzu Muhammad yake bibiyarta?"
Ta dafe goshinta da hannu daya, tana girgiza kai.
"Haka kawai na ji ba dadi! Na ji kamar muna cin amanar kanmu! Don kuwa lamarin backfiring zeyi. Komai tsawon lokaci sai gaskia ta fito mun kwashi kashin mu a hannu"
Hajiya Ladi ta yi gyaran murya, tana kokarin dan shawo kanta.
"Rumanah, ki kwantar da hankalinki. Muna da damar da za mu iya gyara komai."
"Yaya?" Hajiya Rumanah ta yi tsawa.
"Za mu ci gaba da bincike. Sai mun tabbatar da komai kafin mu dauki mataki."
Hajiya Karama ta jinjina kai.
"Eh, dole ne wannan"
Shiru ya ratsa dakin na wasu ‘yan dakiku. Sai dai zuciyar Hajiya Rumanah ta kasa samun natsuwa. Ta sake kallon wayarta, zuciyarta na bugawa da sauri.
"Dole in sake aika sakon tambaya! Ina so in tabbatar da abu daya..."
"To me yasa Muhammad ke son aurenta. Bashi ita akai ko ganinta yayi yana so?"
Hajiya Rumanah ta danna sakon cikin sauri, zuciyarta na dokawa da karfi. Hannunta na rawa, ta zuba ido kan wayar tana jiran amsa.
Hajiya Ladi ta lura da hakan, ta kalli Karama kafin ta dubi Rumanah da kulawa.
"Rumanah, ki kwantar da hankalinki. Kina acting kamar kin san komai, alhali ba mu gama fahimtar lamarin ba."
Hajiya Rumanah ta juyo, idonta cike da bacin rai.
"Ladi, wannan ai ba wasa ba ne! Idan har Nabeeha 'yar Zaytunah ce, kuma take tare da Major General Dawud, muna cikin matsala!"
Hajiya Karama ta yi ajiyar zuciya, ta gyara zaman hijabinta.
"Kin ce haka, amma har yanzu ba ki tabbatar da komai ba. Idan har Muhammad ita din yake so Kuma an tabbatar , ya kamata mu gano me yasa."
Hajiya Rumanah ta sake duban wayarta, tana huci. Kafin su samu damar ci gaba da tattaunawa, amsar sakon ya shigo.
"Nabeeha ba 'yar Major General Dawud bace. 'Yar Hajiya Zaytunah ce, wadda ke zaune a gidan Major General Dawud."
Wayar ta sulale daga hannun Hajiya Rumanah, zuciyarta ta buga da karfi. Kamar an tsikare ta, ta dafe kirjinta, zuciyarta na bugawa da mugun sauri.
"Innalillahi wa inna ilaihi raji’un!"
Hajiya Ladi da Hajiya Karama suka matso da sauri, suka tsare ta da ido.
"Me ya faru?" Karama ta tambaya da damuwa.
Hajiya Rumanah ta nuna wayar da yatsa, idanunta sun ciko da matsanancin tashin hankali.
"Kun ga? Nabeeha 'yar Zaytunah ce! Kuma suna gidan major general dagaske"
Shiru ya ratsa tsakani na wasu dakiku, kowacce daga cikinsu tana kokarin fahimtar wannan ruɗanin da ya kunno kai.
"Ko dai akwai wani abu da ba mu sani ba?" Hajiya Ladi ta furta a hankali, tana mai jin gabanta yana faɗuwa.
Hajiya Karama ta share gumin da ya keto mata.
"Rumanah, muna bukatar karin bayani! Me yasa take a gidan Major General Dawud? Kuma me yasa har yanzu ba mu san hakan ba. Shin su alhaji sunada masaniya ko kuwa?"
Hajiya Rumanah ta jingina jikin kujera, zuciyarta tana ci gaba da tafasa. Wannan batu ya fi ƙarfin yadda take zato!
Tana jin kamar zuciyarta zata tarwatse. Abin da ta fi tsoro yana kokarin zama gaskiya!..
🎀🎀🎀🎀
A cikin wani tsohon gida da ke tsakiyar daji, an ajiye su Hajiya Zaytunah, Nabeeha, da Hammad a ɗaki mai duhu. Hannayensu da ƙafafunsu an ɗaure su da igiya mai ƙarfi, yayin da wasu daga cikin yan fashin suka tsaya a bakin ƙofa suna gadinsu.
Nabeeha ta kalli mahaifiyarta da damuwa, hawaye na kokarin cika idanunta. “Ammi, su wanene waɗannan mutanen? Me su ke so da mu?”
Hajia Zaytunah ta sauke ajiyar zuciya, tana kallon ɗiyarta da ƙoƙarin kwantar mata da hankali.
"Ban sani ba, amma abin da na sani shi ne dole mu ci gaba da yin addu’a.”
Hammad ya runtse idanu, zuciyarsa na tafasa da takaici. Bai iya jure ganin mahaifiyarsa da yayar sa cikin wannan hali ba. Ya ce da ƙasa da murya,
"Su wane ne suka aikosu? Wane irin mugunta ce wannan?”
A dai-dai lokacin, kofar ɗakin ta bude da karfi, daya daga cikin yan fashin ya shigo. Fuskar sa a tamke, idonsa na cike da ƙeta. Ya kalli su hajia zaytunah da wani irin murmushin mugunta.
“Kuna bukatar ruwa ko abinci?” Ya tambaya da wata murya mai cike da zolaya.
Hajiya Zaytunah ta ɗago idonta, tana kallon sa da tsananin tsoro amma ba tare da ta nuna rauni ba. Ta ce da ƙarfi,
“Me kuka ke so da mu? Ku gaya mana, me muka muku?”
Dan fashin ya bushe da dariya.
"Ba ke ce matsalar ba. Amma fa idan ba a bi umarnin mu ba, sai mun koya muku darasi.”
"Aameen Gwaggo. Allah bakiji gabana yadda yake faduwa ba. Amman yadda komai ya wuce na yau da mike tunanin zai faru komai yazo da sauki. Sai na samu nutsuwa da kwanciyar hankali. Ina Kuma fatan Allah ya bayyana su zaytunah da gaggawa yasa suna cikin aminci. Wannan munafiki ko munafaka da suke turawa Alhaji Amiru wannan Sako Kuma Allah ya bayyana mana su. Ya tarwatsa Shirin su duk me hannu aciki"
"Aameen Yaa Rabbi dawuda, Allah yayi maka albarka, Allah yayi maka albarka , Allah ya maka albarka"
"Aameen gwaggo na.. Ubangiji Allah ya Kara miki tsawon kwana da yalwar afuwa, lafiya mai inganci, ya yi riko da hannuwan ki. Yasa ki gama da duniya lafiya"
"Aameen dawuda. Tare da Kai da sauran musulmai baki daya"
Da wannan suka koma cikin gidah su na kambama mutunci da dattako na zuriyar gwaggo zainabu da gwaggo zainabun kan ta...
_1-KALBIM:MAMUH GEE_
_2-KIRJIN MAI HANKALI (AKWATIN SIRRIN SA):MSS XOXO_
_3-ADUNIYATAH :HUGUMAH_
_4-AJIYA A DUHU: BILYN ABDULL_
°°
_1-BOOK DAYA:DARI BIYAR_
_2-BOOKS BIYU:DUBU DAYA_
_3-BOOKS UKU: DUBU DAYA DA DARI BIYAR_
_4-BOOKS HUDU :DUBU BIYU_
_5_YAN NIJAR: 1000CF: 89825722 NOUSAIBA LAWALI MARADI_
_ku tura receipt zuwa ga 09033181070_
*IDAN KATI NE A TURO TA WANNAN NUMBER:*
*09032345899.. SHEDAR KATIN MA NAN ZAA TURA. KATIN MTN!!MTN!!*
____
*KIRJIN MAI HANKALI*
_(Akwatin sirrin sa)_
_🧳👩❤️👨🌺_
*_The Vault Of His Secrets_*
_®️NANA HAFSATU (MX)_
_©️ZAFAFA BIYAR WRITERS_
*_BOOK TWO_*
_PAGE:8_
Hajiya Rumanah ta jingina da kujerarta, zuciyarta na bugawa da sauri. Idanunta sun kada, cikinta kamar yana kuna da wutar da ba ta da iyaka. Tunani ne ya cika zuciyarta, yana tsunduma ta cikin rudani mai tsanani. Shin da gaske Muhammad yaron nan yana son auren Nabeeha? Kuma wai ita Nabeeha ‘yar waye a hakikanin gaskiya?
Ta saki numfashi a hankali, sannan ta mika hannu ta dauki wayarta daga gefenta. Ta dade tana kallon fuskar wayar kamar wacce ke shirin daukar matakin da ba ta da tabbas a kansa. Sai kuma ta bude sabon sakon rubutu, ta danna lambar da take bukata. Hannunta yana kadawa yayin da take danna rubutun,
“Muhammad dan wajen Amiru, wacece yarinyar da yake son aura dagaske? Nabeeha ce?”
Ta yi shiru na dan lokaci, tana kallon sakon da ta rubuta. Sai ta kara danna wasu kalmomi,
“Kuma ina so na tabbatar, wacece ita a hakikanin gaskiya? Ita ‘yar Major General Dawud ce?”
Bayan ta gama, ta danna send. Wayarta ta koma hannunta, amma zuciyarta ta kasa samun kwanciyar hankali. Bata dade da aika sakon ba, sai ga amsa ta shigo. Ta yi saurin dannawa, zuciyarta na bugawa da sauri.
"Nabeeha 'yar Hajiya Zaytunah ce, dake gidan Major General Dawud. Amma ba 'yar Major General Dawud bace."
Hajiya Rumanah ta zaro ido, wani irin jiri ya kwasheta. Gabanta ya fadi, hannunta ya soma rawa, ta saki wayar tana duban su Hajiya Karama da Hajiya Ladi da ido waje.
“Subhanallah! Kenan…” Ta kasa karasawa, sai ta dafe kanta, zuciyarta kamar zata faso kirjinta ta fito.
Hajiya Karama ta matso kusa da ita, tana kokarin lallashinta.
“Rumanah, ki kwantar da hankalinki. Me ya faru? Me suka ce?”
Hajiya Ladi ta dan matsa kusa da ita itama, fuskarta dauke da damuwa.
“Ki fada mana! Me ya sa kike cikin wannan tashin hankalin?”
Hajiya Rumanah ta runtse idanu, ta dafe goshinta da hannu daya, sannan ta furta da kyar,
“Nabeeha ba ‘yar Major General Dawud bace…”
Hajiya Karama da Hajiya Ladi suka zaro ido a tare.
"Me kike nufi?"
Hajiya Rumanah ta bude idanu, tana kallon su da tsananin firgici.
“’Yar Hajiya Zaytunah ce! Kuma tana gidan Major General Dawud ne… Amma ba ‘yar sa bace!”
Shiru ya biyo baya. Zuciyoyinsu sun cika da mamaki da firgici. Hajiya Ladi ta yi saurin fadin:
“Haba Rumanah! Wannan ba zai yiwu ba. Kin tabbata? Wannan bayanin ba kuskure bane?”
Hajiya Rumanah ta kada kai, hawaye na taruwa a idonta. "Ban san me ke faruwa ba… Amma idan haka ne, to lamarin ya fi yadda muke tunani. Wannan matsala ce babba!"
Hajiya Karama ta dafe kirjinta, tana kokarin kwantar da nutsuwarta. “Dole ne mu samo mafita da wuri. Kada mu bari wannan ya bata mana shiri.”
Amma Hajiya Rumanah ta kasa samun nutsuwa. Duk yadda suka so su lallasheta, tunaninta ya tafi nesa. Idan har Nabeeha ba ‘yar Major General Dawud bace, Toh ta tabbata yar Hajiya Zaytunah ce kenan... Zuciyarta ta sake harbawa da karfi…
Hajiya Rumanah ta kasa zama. Ta tashi tsaye, tana safa da marwa a cikin dakin, zuciyarta tana tafasa kamar ruwan dafawa. Idanunta sun kada, tana huci kamar wacce aka yi wa dukan tsiya.
"Wannan ba zai yiwu ba! Nabeeha 'yar Zaytunah ce? Amma me hakan ke nufi? Me yasa take gidan Major General Dawud? Yaki ya fito da ita. Shine gaskiar lamarin ne ko kuwa?"
Hajiya Ladi ta gyara zaman mayafinta, ta dubi Hajiya Karama da fuskar da ke bayyana damuwa.
"Yanzu, Rumanah, yaya za a yi?" Ta tambaya da karyayyen murya.
Hajiya Karama ta numfasa, ta saki wani murmushin dole.
"Ba mu da wata mafita illa mu sake duba lamarin da kyau. Mu tabbatar da gaskiyar al’amarin kafin mu dauki wani mataki."
Amma Hajiya Rumanah ta juyo da sauri, ta daga murya.
"Karama! Da me za mu sake duba lamarin? Ai an riga an tabbatar! Idan har Nabeeha 'yar Zaytunah ce, to tabbas muna cikin matsala! Me ya sa ba wanda ya gaya mana? Me yasa har yanzu Muhammad yake bibiyarta?"
Ta dafe goshinta da hannu daya, tana girgiza kai.
"Haka kawai na ji ba dadi! Na ji kamar muna cin amanar kanmu! Don kuwa lamarin backfiring zeyi. Komai tsawon lokaci sai gaskia ta fito mun kwashi kashin mu a hannu"
Hajiya Ladi ta yi gyaran murya, tana kokarin dan shawo kanta.
"Rumanah, ki kwantar da hankalinki. Muna da damar da za mu iya gyara komai."
"Yaya?" Hajiya Rumanah ta yi tsawa.
"Za mu ci gaba da bincike. Sai mun tabbatar da komai kafin mu dauki mataki."
Hajiya Karama ta jinjina kai.
"Eh, dole ne wannan"
Shiru ya ratsa dakin na wasu ‘yan dakiku. Sai dai zuciyar Hajiya Rumanah ta kasa samun natsuwa. Ta sake kallon wayarta, zuciyarta na bugawa da sauri.
"Dole in sake aika sakon tambaya! Ina so in tabbatar da abu daya..."
"To me yasa Muhammad ke son aurenta. Bashi ita akai ko ganinta yayi yana so?"
Hajiya Rumanah ta danna sakon cikin sauri, zuciyarta na dokawa da karfi. Hannunta na rawa, ta zuba ido kan wayar tana jiran amsa.
Hajiya Ladi ta lura da hakan, ta kalli Karama kafin ta dubi Rumanah da kulawa.
"Rumanah, ki kwantar da hankalinki. Kina acting kamar kin san komai, alhali ba mu gama fahimtar lamarin ba."
Hajiya Rumanah ta juyo, idonta cike da bacin rai.
"Ladi, wannan ai ba wasa ba ne! Idan har Nabeeha 'yar Zaytunah ce, kuma take tare da Major General Dawud, muna cikin matsala!"
Hajiya Karama ta yi ajiyar zuciya, ta gyara zaman hijabinta.
"Kin ce haka, amma har yanzu ba ki tabbatar da komai ba. Idan har Muhammad ita din yake so Kuma an tabbatar , ya kamata mu gano me yasa."
Hajiya Rumanah ta sake duban wayarta, tana huci. Kafin su samu damar ci gaba da tattaunawa, amsar sakon ya shigo.
"Nabeeha ba 'yar Major General Dawud bace. 'Yar Hajiya Zaytunah ce, wadda ke zaune a gidan Major General Dawud."
Wayar ta sulale daga hannun Hajiya Rumanah, zuciyarta ta buga da karfi. Kamar an tsikare ta, ta dafe kirjinta, zuciyarta na bugawa da mugun sauri.
"Innalillahi wa inna ilaihi raji’un!"
Hajiya Ladi da Hajiya Karama suka matso da sauri, suka tsare ta da ido.
"Me ya faru?" Karama ta tambaya da damuwa.
Hajiya Rumanah ta nuna wayar da yatsa, idanunta sun ciko da matsanancin tashin hankali.
"Kun ga? Nabeeha 'yar Zaytunah ce! Kuma suna gidan major general dagaske"
Shiru ya ratsa tsakani na wasu dakiku, kowacce daga cikinsu tana kokarin fahimtar wannan ruɗanin da ya kunno kai.
"Ko dai akwai wani abu da ba mu sani ba?" Hajiya Ladi ta furta a hankali, tana mai jin gabanta yana faɗuwa.
Hajiya Karama ta share gumin da ya keto mata.
"Rumanah, muna bukatar karin bayani! Me yasa take a gidan Major General Dawud? Kuma me yasa har yanzu ba mu san hakan ba. Shin su alhaji sunada masaniya ko kuwa?"
Hajiya Rumanah ta jingina jikin kujera, zuciyarta tana ci gaba da tafasa. Wannan batu ya fi ƙarfin yadda take zato!
Tana jin kamar zuciyarta zata tarwatse. Abin da ta fi tsoro yana kokarin zama gaskiya!..
🎀🎀🎀🎀
A cikin wani tsohon gida da ke tsakiyar daji, an ajiye su Hajiya Zaytunah, Nabeeha, da Hammad a ɗaki mai duhu. Hannayensu da ƙafafunsu an ɗaure su da igiya mai ƙarfi, yayin da wasu daga cikin yan fashin suka tsaya a bakin ƙofa suna gadinsu.
Nabeeha ta kalli mahaifiyarta da damuwa, hawaye na kokarin cika idanunta. “Ammi, su wanene waɗannan mutanen? Me su ke so da mu?”
Hajia Zaytunah ta sauke ajiyar zuciya, tana kallon ɗiyarta da ƙoƙarin kwantar mata da hankali.
"Ban sani ba, amma abin da na sani shi ne dole mu ci gaba da yin addu’a.”
Hammad ya runtse idanu, zuciyarsa na tafasa da takaici. Bai iya jure ganin mahaifiyarsa da yayar sa cikin wannan hali ba. Ya ce da ƙasa da murya,
"Su wane ne suka aikosu? Wane irin mugunta ce wannan?”
A dai-dai lokacin, kofar ɗakin ta bude da karfi, daya daga cikin yan fashin ya shigo. Fuskar sa a tamke, idonsa na cike da ƙeta. Ya kalli su hajia zaytunah da wani irin murmushin mugunta.
“Kuna bukatar ruwa ko abinci?” Ya tambaya da wata murya mai cike da zolaya.
Hajiya Zaytunah ta ɗago idonta, tana kallon sa da tsananin tsoro amma ba tare da ta nuna rauni ba. Ta ce da ƙarfi,
“Me kuka ke so da mu? Ku gaya mana, me muka muku?”
Dan fashin ya bushe da dariya.
"Ba ke ce matsalar ba. Amma fa idan ba a bi umarnin mu ba, sai mun koya muku darasi.”