Sashe 6
Kirjin Mai Hankali Part 2 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Bayan ɗan lokaci, Ya ɗan gyara zamansa, yana kallon Gwaggo Zainabu da sauran bakin da ke falon, yana jiran jin dalilin zuwansu da abinda suke da bukatar tattaunawa a kai.
"Ranka ya dade... Nasan wata kila chief judge ya sanar maka da zuwan mu ko?"
"Eh anyi haka. Yace zaku zo da yardar Allah..Dazu ma ya kirawo ni yake duba jikin mahaifiyata yake kuma sheda mun cewar shugaban kasa yana neman su kan wata shariah da.. yace idan ya dawo daga tafiyar zai shigo inshaa Allah"
"Allah sarki. Shi yasa nayita kiran wayar sa bata shiga?" Cewar Alhaji Amiru
"Zai iya yiwuwa kam. Kila suna cikin meeting. Allah yasa adace"
"Aameen Yaa Rabbi. Ya jikin Hajian? "
Suka shiga tanbayar jikin Gwaggo Hafsatu
"Da sauki Alhamdulillah.... Zata karaso nan din yanzu Inshaa Allah.." major general ya fada yana murmushi.
Bai rufe baki ba kuwa... Gwaggo Hafsatu ta shiga parlorn. Hajia Hauwa tana biye da ita a baya. Bakunan su dauke da sallama suka karasa shiga
Suka amsa sallamar ta su... Gwaggo Hafsatu ta zauna akan kujera yayinda hajia Hauwa take daga kasanta.
Gaisuwa suka farayi. Gwaggo Hafsatu da gwaggo zainabu sun gaysa sosai. Har suna tuno abubuwan da suka faru a baya lokacin da suka fara haduwa a asibitin dake birnin mawii.
Alhaji Uzairu ya zauna cikin kamewa da dattako, ya gyara zamansa sannan ya fara magana da ladabi,
"Assalamu alaikum wa rahmatullahi wa barakatuhu. Yan uwa da iyayena mun zo gare ku ne a yau da farin ciki da girmamawa, domin mu gabatar da bukatar mu ta musamman. Da farko, muna mika gaisuwa da fatan alheri gare ku baki daya. Mun zo ne domin neman izinin ku da yardar ku, wajen neman auren 'yar ku, Nabeeha, ga ɗan mu, Muhammad. Mun yi imani cewa wannan haɗin zai kawo farin ciki da ɗorewar zumunci tsakanin iyalanmu.
"Muhammad, ɗanmu, matashi ne mai tarbiyya da kyawawan halaye. Ya kammala karatunsa tare da samun nasarori masu yawa, kuma yana da kyakkyawan aiki da ke ba shi damar kula da iyali yadda ya kamata. Wato matukin jirgin sama ne, Air captain Muhammad, Har ila yau, yana da kyakkyawar mu'amala da mutane, kuma yana da kishi da kishin al'umma. Mun yi imani cewa zai zama miji nagari ga 'yar ku, Kuma yar mu, Nabeeha.
"Mun kuma ji labarin kyawawan halayen Nabeeha, Mun yaba kwarai matuka, Yadda take da ilimi, Tana karatun likita, Ga tarbiyya, da kuma kwarewa a fannoni daban-daban. Mun yi imani cewa tare da Muhammad, za su kafa gida nagari mai cike da soyayya, fahimta, da kuma goyon bayan juna.
"Muna fatan Allah ya sa wannan haɗin ya zama alheri ga dukkanmu, ya kuma ba mu ikon cika dukkan hakkokin da ke kanmu wajen wannan aure. Muna kuma fatan za mu ci gaba da ƙarfafa zumunci da haɗin kai tsakanin iyalanmu, domin amfaninmu da kuma al'ummar da muke ciki.
"Aameen" suka amsa baki daya...
Bayan Alhaji Uzairu ya kammala bayani, Gwaggo Zainabu ta gyara zamanta cikin nutsuwa, ta kalli iyayen Nabeeha da murmushi, sannan ta fara magana,
"Assalamu alaikum.... Masha Allah, Ya gama fadan kusan daya daga cikin abunda ya kawo mu...Na zo tare da su ne domin nuna goyon baya ga wannan kyakkyawar manufa. Ina fatan wannan ziyara za ta taimaka wajen ƙara sanin juna, ƙarfafa zumunci, da gina kyakkyawar alaƙa tsakanin iyalanmu. Har ila yau, ina son in ga yarinyar da jikata, Muhammad, yake so ya aura. Wato kishiyata Nabeeha, don in fara Shirin damarar zama da wadda zaa kawo"
Suka Saka dariya baki daya... na Jin gwaggo zainabu tana wasan kaka da jika.. Gwaggo zainabu ta dan murmusa sannan ta cigaba da cewa,
"Ina fatan Allah ya sa wannan haɗin ya zama sanadin samun zaman lafiya, farin ciki, da ci gaba ga iyalanmu baki ɗaya.muna fatan za mu yi aiki tare wajen shirye-shiryen wannan aure, idan har an amince mana, tare da yin duk mai yiwuwa domin ganin an gudanar da komai cikin nasara da yardar Allah. Allah ya sa a yi aure lafiya, ya ba su zuri'a dayyiba, ya kuma sa zaman aurensu ya kasance cike da farin ciki da albarka.
"Da fatan za mu ci gaba da haɗin kai da fahimtar juna a duk matakan da za a bi domin cimma wannan manufa ta alheri. Muna godiya da lokacinku da kuma karɓar mu da kuka yi da hannu biyu. Wassalamu alaikum wa rahmatullahi wa barakatuhu."
"Wa'alaykumm Salam Wa rahamatullahi Wa barakatuh. Sannu ku da kokari Gwaggo. Muna godia kwarai da gaske. Hadi da kambamawa da wannan dattako irin naku. Harda wahala. Ga kayanan fal? Mungode Allah ya Saka da alkhairi " major general ya fada yana nuni da kayayyakin da suka kawo..
"Sai yanzu na lura da su... Aa harda kokari haka? Toh Allah ya Saka da alkhairi ya bar zumunci har gaban abadan. Sai dai ban sheda ka sosai ba" gwaggo Hafsatu ta karasa magana tana duban Alhaji Uzairu.
Alhaji Uzairu ya dubi Gwaggo Hafsatu da murmushi a kwance a fuskar sa yace,
"Laa Gwaggo kin manta uzairu? Ni ne ke zama da gwaggo a asibiti da safe zuwa da yamma kafin a kawo abinci."
"Oh haka haka. Allah sarki ai dake shekarun da yawa. Jikin tsufa. Toh Allah yayi muku albarka"
"Aameen gwaggo Aameen"
"Alhaji Uzairu ne. Kani ga Alhaji Amiru " major general ya dubi gwaggo Hafsatu yana gaya mata.. gabansa na bugawa..
Gwaggo Hafsatu mahaifiyar sa ta lura ta dube shi cikin idanu tana murmushin da zai kwantar masa da hankali.
Gwaggo zainabu ta dan numfasa tana kurbar ruwan gorar da ke hannunta tache,
Bayan Gwaggo Zainabu ta kammala jawabin ta na farko, ta ɗan yi shiru na ɗan lokaci, sannan ta numfasa cikin nutsuwa, ta kalli Major General Dawud da iyalansa, ta ci gaba da magana cikin tausayawa,
"Abin da ya sa na zo tare da su a yau, ba wai kawai don neman auren Nabeeha ga Muhammad ba ne, har ila yau akwai wata muhimmiyar magana da take damuna sosai. Na san cewa kai, Major General Dawud, kana iyaka ƙoƙarinka wajen ganin an samu nasara a dukkan al'amuran tsaro da suka shafi ƙasarmu. Amma ina roƙonka da Allah, a sake tsananta bincike domin gano halin da Zaytunah da 'ya'yanta biyu suke ciki..shekaru matukar yawa bamu sake Saka su a idanun mu ba. Ko suna raye ko kuma sun rasu.
"Zaytunah tana da matuƙar muhimmanci a gare mu. Matar da na ce uzairu gashi nan., kuma tun lokacin da muka rasa labarinta tare da 'ya'yanta biyu, Zainab da Muhammad . Wanda suna daya suka ci da wannan manemun Nabeeha. zuciyata tana cikin tsananin damuwa da rashin tabbas. Mun yi ƙoƙari da dama wajen gano inda suke, amma har yanzu ba mu sami wani sahihin labari ba. Na san cewa kana da damar da za ta iya taimaka mana wajen gano gaskiyar al'amarin. Don Allah, ka taimaka mana a wannan lamari, ka yi duk mai yiwuwa wajen ganin an gano ko suna raye ko kuma sun rasu, domin mu samu nutsuwar zuciya.
"Rashin sanin halin da suke ciki ya kasance wani babban ƙunci a zuciyarmu. Idan har suna raye, muna fatan Allah ya sa mu sake haɗuwa da su cikin koshin lafiya. Idan kuma akasin haka ne, to muna so mu san gaskiya domin mu yi musu addu'a yadda ya kamata, kuma mu ci gaba da rayuwarmu tare da karɓar ƙaddara. Amma wannan rashin tabbas yana ci gaba da damunmu, kuma muna fatan za ka taimaka mana wajen kawo ƙarshen wannan yanayi.
"Na san cewa kana da nauyi mai yawa a kan ka, kuma kana aiki tukuru wajen tabbatar da tsaron ƙasa da walwalar jama'a. Amma ina roƙonka da ka ɗauki wannan lamari a matsayin wani abu na musamman, ka ba shi muhimmanci, domin taimaka mana mu samu kwanciyar hankali. Ina fatan Allah ya taimaka maka a aikinka, ya ba ka nasara a dukkan al'amuranka, ya kuma saka maka da alheri bisa taimakon da za ka yi mana.
"Muna godiya sosai da lokacinka da kuma kulawarka. Allah ya saka da alheri, ya kuma sa mu ji labari mai daɗi nan ba da jimawa ba."
Bayan ta kammala wannan jawabi, Gwaggo Zainabu ta share hawaye daga idonta, tana fatan cewa wannan roƙo nata zai samu karɓuwa, kuma za a ɗauki matakan da suka dace wajen gano halin da Zaytunah da 'ya'yanta suke ciki.
Duk jikin su sai yayi sanyi gaba ki dayan su. Musanman yadda kalaman gwaggo suke futa daga bakinta da tausayawa matuka...
_1-KALBIM:MAMUH GEE_
_2-KIRJIN MAI HANKALI (AKWATIN SIRRIN SA):MSS XOXO_
_3-ADUNIYATAH :HUGUMAH_
_4-AJIYA A DUHU: BILYN ABDULL_
°°
_1-BOOK DAYA:DARI BIYAR_
_2-BOOKS BIYU:DUBU DAYA_
_3-BOOKS UKU: DUBU DAYA DA DARI BIYAR_
_4-BOOKS HUDU :DUBU BIYU_
_5_YAN NIJAR: 1000CF: 89825722 NOUSAIBA LAWALI MARADI_
_ku tura receipt zuwa ga 09033181070_
*IDAN KATI NE A TURO TA WANNAN NUMBER:*
*09032345899.. SHEDAR KATIN MA NAN ZAA TURA. KATIN MTN!!MTN!!*
____
*KIRJIN MAI HANKALI*
_(Akwatin sirrin sa)_
_🧳👩❤️👨🌺_
*_The Vault Of His Secrets_*
_®️NANA HAFSATU (MX)_
_©️ZAFAFA BIYAR WRITERS_
*_BOOK TWO_*
_PAGE:7_
Bayan Gwaggo Zainabu ta kammala bayani kan bukatar a tsananta bincike don gano halin da Zaytunah da 'ya'yanta biyu suke ciki, Major General Dawud ya gyara zamansa cikin tawali'u, ya dubi Gwaggo Zainabu da kulawa, sannan ya fara magana cikin nutsuwa,
"Gaskiya, Gwaggo Zainabu, na yi matukar jin dadin zuwanku da kuma wannan muhimmiyar bukata da kuka gabatar. Ina mai tabbatar muku cewa muna daukar wannan al'amari da matukar muhimmanci, kuma za mu ci gaba da yin duk mai yiwuwa wajen ganin an gano halin da Zaytunah da 'ya'yanta suke ciki. Za mu kara kaimi wajen bincike, tare da amfani da dukkan hanyoyin da suka dace domin samun bayanai masu inganci kan wannan batu...." Ya numfasa ainun yana jujjuya yadda zai furta zancen. Don a zahirin gaskiya a halin da suke ciki shi kansa ba shida masaniyar inda su hajia zaytunahh suke a yanzu kenan. A baya suna gidansa ne tabbas. Amma yanzu an sace su bai san inda suke ba. Yanadai iya kokarin wajen gano inda suke don haka ya dubi gwaggo Hafsatu cikin kwarin gwiwa hadi da mayarda dubansa ga Gwaggo zainabu ya cigaba da cewa,
"Ranka ya dade... Nasan wata kila chief judge ya sanar maka da zuwan mu ko?"
"Eh anyi haka. Yace zaku zo da yardar Allah..Dazu ma ya kirawo ni yake duba jikin mahaifiyata yake kuma sheda mun cewar shugaban kasa yana neman su kan wata shariah da.. yace idan ya dawo daga tafiyar zai shigo inshaa Allah"
"Allah sarki. Shi yasa nayita kiran wayar sa bata shiga?" Cewar Alhaji Amiru
"Zai iya yiwuwa kam. Kila suna cikin meeting. Allah yasa adace"
"Aameen Yaa Rabbi. Ya jikin Hajian? "
Suka shiga tanbayar jikin Gwaggo Hafsatu
"Da sauki Alhamdulillah.... Zata karaso nan din yanzu Inshaa Allah.." major general ya fada yana murmushi.
Bai rufe baki ba kuwa... Gwaggo Hafsatu ta shiga parlorn. Hajia Hauwa tana biye da ita a baya. Bakunan su dauke da sallama suka karasa shiga
Suka amsa sallamar ta su... Gwaggo Hafsatu ta zauna akan kujera yayinda hajia Hauwa take daga kasanta.
Gaisuwa suka farayi. Gwaggo Hafsatu da gwaggo zainabu sun gaysa sosai. Har suna tuno abubuwan da suka faru a baya lokacin da suka fara haduwa a asibitin dake birnin mawii.
Alhaji Uzairu ya zauna cikin kamewa da dattako, ya gyara zamansa sannan ya fara magana da ladabi,
"Assalamu alaikum wa rahmatullahi wa barakatuhu. Yan uwa da iyayena mun zo gare ku ne a yau da farin ciki da girmamawa, domin mu gabatar da bukatar mu ta musamman. Da farko, muna mika gaisuwa da fatan alheri gare ku baki daya. Mun zo ne domin neman izinin ku da yardar ku, wajen neman auren 'yar ku, Nabeeha, ga ɗan mu, Muhammad. Mun yi imani cewa wannan haɗin zai kawo farin ciki da ɗorewar zumunci tsakanin iyalanmu.
"Muhammad, ɗanmu, matashi ne mai tarbiyya da kyawawan halaye. Ya kammala karatunsa tare da samun nasarori masu yawa, kuma yana da kyakkyawan aiki da ke ba shi damar kula da iyali yadda ya kamata. Wato matukin jirgin sama ne, Air captain Muhammad, Har ila yau, yana da kyakkyawar mu'amala da mutane, kuma yana da kishi da kishin al'umma. Mun yi imani cewa zai zama miji nagari ga 'yar ku, Kuma yar mu, Nabeeha.
"Mun kuma ji labarin kyawawan halayen Nabeeha, Mun yaba kwarai matuka, Yadda take da ilimi, Tana karatun likita, Ga tarbiyya, da kuma kwarewa a fannoni daban-daban. Mun yi imani cewa tare da Muhammad, za su kafa gida nagari mai cike da soyayya, fahimta, da kuma goyon bayan juna.
"Muna fatan Allah ya sa wannan haɗin ya zama alheri ga dukkanmu, ya kuma ba mu ikon cika dukkan hakkokin da ke kanmu wajen wannan aure. Muna kuma fatan za mu ci gaba da ƙarfafa zumunci da haɗin kai tsakanin iyalanmu, domin amfaninmu da kuma al'ummar da muke ciki.
"Aameen" suka amsa baki daya...
Bayan Alhaji Uzairu ya kammala bayani, Gwaggo Zainabu ta gyara zamanta cikin nutsuwa, ta kalli iyayen Nabeeha da murmushi, sannan ta fara magana,
"Assalamu alaikum.... Masha Allah, Ya gama fadan kusan daya daga cikin abunda ya kawo mu...Na zo tare da su ne domin nuna goyon baya ga wannan kyakkyawar manufa. Ina fatan wannan ziyara za ta taimaka wajen ƙara sanin juna, ƙarfafa zumunci, da gina kyakkyawar alaƙa tsakanin iyalanmu. Har ila yau, ina son in ga yarinyar da jikata, Muhammad, yake so ya aura. Wato kishiyata Nabeeha, don in fara Shirin damarar zama da wadda zaa kawo"
Suka Saka dariya baki daya... na Jin gwaggo zainabu tana wasan kaka da jika.. Gwaggo zainabu ta dan murmusa sannan ta cigaba da cewa,
"Ina fatan Allah ya sa wannan haɗin ya zama sanadin samun zaman lafiya, farin ciki, da ci gaba ga iyalanmu baki ɗaya.muna fatan za mu yi aiki tare wajen shirye-shiryen wannan aure, idan har an amince mana, tare da yin duk mai yiwuwa domin ganin an gudanar da komai cikin nasara da yardar Allah. Allah ya sa a yi aure lafiya, ya ba su zuri'a dayyiba, ya kuma sa zaman aurensu ya kasance cike da farin ciki da albarka.
"Da fatan za mu ci gaba da haɗin kai da fahimtar juna a duk matakan da za a bi domin cimma wannan manufa ta alheri. Muna godiya da lokacinku da kuma karɓar mu da kuka yi da hannu biyu. Wassalamu alaikum wa rahmatullahi wa barakatuhu."
"Wa'alaykumm Salam Wa rahamatullahi Wa barakatuh. Sannu ku da kokari Gwaggo. Muna godia kwarai da gaske. Hadi da kambamawa da wannan dattako irin naku. Harda wahala. Ga kayanan fal? Mungode Allah ya Saka da alkhairi " major general ya fada yana nuni da kayayyakin da suka kawo..
"Sai yanzu na lura da su... Aa harda kokari haka? Toh Allah ya Saka da alkhairi ya bar zumunci har gaban abadan. Sai dai ban sheda ka sosai ba" gwaggo Hafsatu ta karasa magana tana duban Alhaji Uzairu.
Alhaji Uzairu ya dubi Gwaggo Hafsatu da murmushi a kwance a fuskar sa yace,
"Laa Gwaggo kin manta uzairu? Ni ne ke zama da gwaggo a asibiti da safe zuwa da yamma kafin a kawo abinci."
"Oh haka haka. Allah sarki ai dake shekarun da yawa. Jikin tsufa. Toh Allah yayi muku albarka"
"Aameen gwaggo Aameen"
"Alhaji Uzairu ne. Kani ga Alhaji Amiru " major general ya dubi gwaggo Hafsatu yana gaya mata.. gabansa na bugawa..
Gwaggo Hafsatu mahaifiyar sa ta lura ta dube shi cikin idanu tana murmushin da zai kwantar masa da hankali.
Gwaggo zainabu ta dan numfasa tana kurbar ruwan gorar da ke hannunta tache,
Bayan Gwaggo Zainabu ta kammala jawabin ta na farko, ta ɗan yi shiru na ɗan lokaci, sannan ta numfasa cikin nutsuwa, ta kalli Major General Dawud da iyalansa, ta ci gaba da magana cikin tausayawa,
"Abin da ya sa na zo tare da su a yau, ba wai kawai don neman auren Nabeeha ga Muhammad ba ne, har ila yau akwai wata muhimmiyar magana da take damuna sosai. Na san cewa kai, Major General Dawud, kana iyaka ƙoƙarinka wajen ganin an samu nasara a dukkan al'amuran tsaro da suka shafi ƙasarmu. Amma ina roƙonka da Allah, a sake tsananta bincike domin gano halin da Zaytunah da 'ya'yanta biyu suke ciki..shekaru matukar yawa bamu sake Saka su a idanun mu ba. Ko suna raye ko kuma sun rasu.
"Zaytunah tana da matuƙar muhimmanci a gare mu. Matar da na ce uzairu gashi nan., kuma tun lokacin da muka rasa labarinta tare da 'ya'yanta biyu, Zainab da Muhammad . Wanda suna daya suka ci da wannan manemun Nabeeha. zuciyata tana cikin tsananin damuwa da rashin tabbas. Mun yi ƙoƙari da dama wajen gano inda suke, amma har yanzu ba mu sami wani sahihin labari ba. Na san cewa kana da damar da za ta iya taimaka mana wajen gano gaskiyar al'amarin. Don Allah, ka taimaka mana a wannan lamari, ka yi duk mai yiwuwa wajen ganin an gano ko suna raye ko kuma sun rasu, domin mu samu nutsuwar zuciya.
"Rashin sanin halin da suke ciki ya kasance wani babban ƙunci a zuciyarmu. Idan har suna raye, muna fatan Allah ya sa mu sake haɗuwa da su cikin koshin lafiya. Idan kuma akasin haka ne, to muna so mu san gaskiya domin mu yi musu addu'a yadda ya kamata, kuma mu ci gaba da rayuwarmu tare da karɓar ƙaddara. Amma wannan rashin tabbas yana ci gaba da damunmu, kuma muna fatan za ka taimaka mana wajen kawo ƙarshen wannan yanayi.
"Na san cewa kana da nauyi mai yawa a kan ka, kuma kana aiki tukuru wajen tabbatar da tsaron ƙasa da walwalar jama'a. Amma ina roƙonka da ka ɗauki wannan lamari a matsayin wani abu na musamman, ka ba shi muhimmanci, domin taimaka mana mu samu kwanciyar hankali. Ina fatan Allah ya taimaka maka a aikinka, ya ba ka nasara a dukkan al'amuranka, ya kuma saka maka da alheri bisa taimakon da za ka yi mana.
"Muna godiya sosai da lokacinka da kuma kulawarka. Allah ya saka da alheri, ya kuma sa mu ji labari mai daɗi nan ba da jimawa ba."
Bayan ta kammala wannan jawabi, Gwaggo Zainabu ta share hawaye daga idonta, tana fatan cewa wannan roƙo nata zai samu karɓuwa, kuma za a ɗauki matakan da suka dace wajen gano halin da Zaytunah da 'ya'yanta suke ciki.
Duk jikin su sai yayi sanyi gaba ki dayan su. Musanman yadda kalaman gwaggo suke futa daga bakinta da tausayawa matuka...
_1-KALBIM:MAMUH GEE_
_2-KIRJIN MAI HANKALI (AKWATIN SIRRIN SA):MSS XOXO_
_3-ADUNIYATAH :HUGUMAH_
_4-AJIYA A DUHU: BILYN ABDULL_
°°
_1-BOOK DAYA:DARI BIYAR_
_2-BOOKS BIYU:DUBU DAYA_
_3-BOOKS UKU: DUBU DAYA DA DARI BIYAR_
_4-BOOKS HUDU :DUBU BIYU_
_5_YAN NIJAR: 1000CF: 89825722 NOUSAIBA LAWALI MARADI_
_ku tura receipt zuwa ga 09033181070_
*IDAN KATI NE A TURO TA WANNAN NUMBER:*
*09032345899.. SHEDAR KATIN MA NAN ZAA TURA. KATIN MTN!!MTN!!*
____
*KIRJIN MAI HANKALI*
_(Akwatin sirrin sa)_
_🧳👩❤️👨🌺_
*_The Vault Of His Secrets_*
_®️NANA HAFSATU (MX)_
_©️ZAFAFA BIYAR WRITERS_
*_BOOK TWO_*
_PAGE:7_
Bayan Gwaggo Zainabu ta kammala bayani kan bukatar a tsananta bincike don gano halin da Zaytunah da 'ya'yanta biyu suke ciki, Major General Dawud ya gyara zamansa cikin tawali'u, ya dubi Gwaggo Zainabu da kulawa, sannan ya fara magana cikin nutsuwa,
"Gaskiya, Gwaggo Zainabu, na yi matukar jin dadin zuwanku da kuma wannan muhimmiyar bukata da kuka gabatar. Ina mai tabbatar muku cewa muna daukar wannan al'amari da matukar muhimmanci, kuma za mu ci gaba da yin duk mai yiwuwa wajen ganin an gano halin da Zaytunah da 'ya'yanta suke ciki. Za mu kara kaimi wajen bincike, tare da amfani da dukkan hanyoyin da suka dace domin samun bayanai masu inganci kan wannan batu...." Ya numfasa ainun yana jujjuya yadda zai furta zancen. Don a zahirin gaskiya a halin da suke ciki shi kansa ba shida masaniyar inda su hajia zaytunahh suke a yanzu kenan. A baya suna gidansa ne tabbas. Amma yanzu an sace su bai san inda suke ba. Yanadai iya kokarin wajen gano inda suke don haka ya dubi gwaggo Hafsatu cikin kwarin gwiwa hadi da mayarda dubansa ga Gwaggo zainabu ya cigaba da cewa,