Sashe 27
Kirjin Mai Hankali Part 2 Complete Hausa Novel · about 8 min read
"Kullum dada kewarki. Nake, tamkar na janyo ranar bikin mu haka nakeji, Ban san me yasa ba, amma tun farkon haduwarmu, na ji wani abu na daban a kanki. Ina son ki, Nabeeha, da gaske nake."
Shiru ta yi, ba ta ce komai ba. A zahiri, ta ji kalmomin Muhammad, amma ba su shiga zuciyarta ba. Tunani kawai take—da ace Fawaaz ne ke furta mata hakan a baki, ba kawai a rubuce ba…
Yar wahalaaaaa🤭😏
Muhammad ya dan yi murmushi. "Kin yi shiru?"
Ta numfasa. "Ba komai."
"Ba ki ce komai ba akan abin da na fada."
Ta dafa goshinta. "Muhammad… Kai na ke ciwo. Yi.hakuri"
Ya yi shiru na wani lokaci. "Babu matsala. Amma a kalla ki san cewa na fadi abin da zuciyata ke ji. Kuma ba zan yi nadamar fada ba...Allah yakara miki lafiya da nisan kwana mai albarka amin"
Ta dan yi murmushi kadan. "Nagode."
Sun dan kara hira kadan, sannan suka yi sallama. Ta mika wa Humayrah wayarta, sannan ta koma ta kwanta, zuciyarta na kara cike da tunanin Fawaaz.
"Me yasa ya kasa furtawa a baki?"
"Me yasa ya ke boye abin da yake ji?"
"Ko kuwa yana fargabar abinda zai biyo baya?"
Watan wata rana… wata rana zai iya furtawa?
Bayan tattaunawarta da Muhammad, Nabeeha ta ajiye mikawa humyrah wayarta,. Sai dai, ko da suka yi sallama, ba kalmomin Muhammad take tunani ba—sai Fawaaz.
"Me yasa ya kasa furtawa a baki?"
Tana kwance kan gadonta, hannayenta sun dunkule a kirjinta, zuciyarta tana gudu da sauri. Ta rufe idanuwanta da karfi, tana kokarin korar tunanin da ya mamaye ta. Amma hakan bai yiwu ba.
Tunanin Fawaaz ya ci gaba da dawowa. Idanunta na kulle, ta fara tuno lokacin da ta fara lura da sauyin da ya faru da shi—lokacin da ya fara kallonta da wata irin kallo mai nauyi, lokacin da ta fara samun sakonninsa masu dauke da kalmomin da suka fi yadda yake iya furtawa.
"Ba zan iya furtawa a baki ba… amma ki sani, zuciyata ta yarda da ke."
"Ke ce abin da nake bukata, ko da kuwa duniya ba ta fahimta."
Tana da tabbacin cewa Fawaaz yana da wata irin soyayya a gare ta, amma ya kasa furtawa a fili. Me yasa? Shin miskilancinsa ne ke hana shi? Ko kuwa wani abu ne da ba ta sani ba?
Ta bude idonta, tana duban rufin dakin. "Idan har yana sona da gaske, me zai hana ya fada?"
Tana cikin wannan tunani ne sai aka turo kofar dakin.
"Nabeeha!"
Ta dago da sauri. Humayrah ce ke kokarin shigowa, fuskarta cike da murmushi.
"Mene ne kuma?" Nabeeha ta tambaya, tana zuba mata harara.
Humayrah ta zauna a gefen gadon, tana yatsina fuska. "Haba dai, ke kam. Me yasa kika yi kamar ba kya son magana da Muhammad?"
"Ban ce ba na son magana da shi ba."
"Amma ba ki nuna sha'awar tattaunawar ba."
Nabeeha ta dube ta da murmushin gefen baki. "Ke dai bari kawai, ina cikin tunani ne."
Humayrah ta mike tana kallonta. "Tunanin wani kike ko?"
Nabeeha ta zabura. "Me yasa kika ce haka?"
Humayrah ta harare ta. "Ai a yanzu haka, koda ace wani zai baka labari mai dadi, amma kana da wani abu a zuciyarka, ba za ka ji dadin labarin ba."
Ta yi shiru, tana nazarin maganar Humayrah. Ko da yake ba ta son yarda da hakan, amma akwai gaskiya a ciki.
"Ke dai bari kawai," ta ce, tana kokarin kawar da batun.
Humayrah ta yi dariya. "To Allah ya kyauta. Amma dai Muhammad na nan, yana jiranki ki yanke hukunci."
____
A gefe guda, Fawaaz yana zaune a kofar falonsa, cikin duhun dare. Ya jingina da kujerar da yake zaune a kai, hannunsa rike da wayarsa. Ya kafe screen din wayar da idanu, yana nazarin sakonnin da ya tura wa Nabeeha.
Ya sani. Ya sani cewa bai dace ya ci gaba da boye soyayyarsa ba. Ya sani cewa ba zai iya ci gaba da kamewa ba, amma me zai yi?
Zuciyarsa na cike da tsoro. Ba tsoron soyayya ba—tsoron abin da zai biyo baya.
Yana jin zuciyarsa na dukan abu guda. Idanunsa sun kada kadan saboda tunani da damuwa.
A can can, zuciyarsa na tambayarsa,
"Za ka ci gaba da ɓoye gaskiyar zuciyarka?"
"Ko kuwa lokaci ya yi da za ka bayyana?"
Ya sauke ajiyar zuciya, yana jin daren yana yi masa nauyi.
Numfashin Nabeeha ya tsaya cak. "Yaa Fawaaz?"
Muryarta ta fita da sanyi, tamkar ba ita ta yi magana ba.
A daya bangaren, shiru ne. Sai daga baya ta ji numfashinsa ya sauka kadan. "Eh, .. Zan iya ganinki?"
Wata irin kasala ta shige ta. Hannunta ya yi sanyi, zuciyarta na bugawa kamar zata fado daga kirjinta.
Me zai fada mata?
Meyasa yake neman ganinta a wannan dare ta intercom din dakin ta?
Tayi shiru, zuciyarta na kokarin tattaro amsar da zata bashi.
"Ina kusa da balcony. Idan har ba damuwa, ki fito."
Zuciyarta ta tsananta bugawa.
Shin ta fita?
Shin da gaske zai iya furtawa a yau?
Tana cikin wannan tunani ne sai aka turo kofar dakin. Humayrah ce.
"Ke! Waye haka yake magana da ke da daddare?" Ta tambaya, tana kokarin karbar wayar.
Da sauri Nabeeha ta kashe kiran, zuciyarta na harbawa. "Ba kowa."
Humayrah ta kalle ta da mamaki. "Ba kowa kuma? To me yasa kika kashe wayar da sauri?"
Nabeeha ta girgiza kai, tana kokarin boye rikicin zuciyarta. "Ki daina bincike mana."
Humayrah ta tabe baki. "To ai da gani akwai abu. Ko dai Muhammad ne ya kira?"
"A'a kuma ta intercom? ." Nabeeha ta fada da sauri, tana jin yadda zuciyarta ke ci gaba da dukan abu guda.
Humayrah ta yi shiru, sannan ta kalli gefenta. "Da gaske dai babu matsala?"
Nabeeha ta yi kokarin murmushi. "Eh, ki kwantar da hankalinki."
Amma ita kanta ta san cewa hankalinta ya tashi.
Ta mike daga gadon, zuciyarta na tafasa. Shin ta fita ta hadu da Fawaaz?
Ko kuwa ta share shi kamar yadda yake son boye soyayyarsa?
Fawaaz yana tsaye a jikin motarsa, hannayensa a cikin aljihu. Zuciyarsa na tafasa, yana jiran amsar Nabeeha.
Me zai ce idan ta fito?
Meyasa bai iya furtawa a da ba?
Ya sauke numfashi. "Yau, dole zan fada."
Idan har ba zai iya furtawa a yau ba, to zai iya rasa ta har abada.
_1-KALBIM:MAMUH GEE_
_2-KIRJIN MAI HANKALI (AKWATIN SIRRIN SA):MSS XOXO_
_3-ADUNIYATAH :HUGUMAH_
_4-AJIYA A DUHU: BILYN ABDULL_
°°
_1-BOOK DAYA:DARI BIYAR_
_2-BOOKS BIYU:DUBU DAYA_
_3-BOOKS UKU: DUBU DAYA DA DARI BIYAR_
_4-BOOKS HUDU :DUBU BIYU_
_5_YAN NIJAR: 1000CF: 89825722 NOUSAIBA LAWALI MARADI_
_ku tura receipt zuwa ga 09033181070_
*IDAN KATI NE A TURO TA WANNAN NUMBER:*
*09032345899.. SHEDAR KATIN MA NAN ZAA TURA. KATIN MTN!!MTN!!*
____
**KIRJIN MAI HANKALI*
_(AKWATIN SIRRIN SA)_
🧳➿💞
*PG :23*
*AREWABOOKS VVIP:👇*
https://www.arewabooks.com/book?id=670bd07e35879b101764c0eb
__
A tsakar dare, Fawaaz yana zaune a kan kujerar barandar gidan, hannunsa na jingine da gefen kujera, yana kallon sararin samaniya. Hasken wata yana haska filin gidan, yana ba da nutsuwa, amma zuciyarsa ba ta da nutsuwa ko kadan.
Me yake yi da zuciyarsa haka?
Ya rike goshinsa a hankali. Duk yadda ya so ya boye abin da ke ransa, ya kasa.
Yana son Nabeeha.
Bai san yadda zai iya rayuwa ba tare da ita ba.
Yana shakar numfashinta idan tana kusa.
Idan ta wuce ta gefensa, wani kamshi na musamman ke ratsa shi. Bai san ko menene ba, amma yana tabbatar da cewa ko a cikin taron mutane dari, zai iya gane Nabeeha.
Komai nata daban ne.
Tana da nutsuwa, tana da sanin ya kamata, tana da ilimi, tana da hankali fiye da yadda yawancin mata ke da shi.
Ba kawai kyawunta ba ne ya ke ja shi gare ta, dabi'arta ce, hankalinta, tausasawarta.
Ya yi murmushi a hankali. Ta na da tausayi.
Yana iya tuna yadda take tausaya wa kowa, har da wadanda ba su san tausayin wasu ba.
Ya kan ga yadda take rike da addininta, yadda take nisantar abin da bai dace ba. Ba wai tana takura wa kanta ba, amma tana da tsoron Allah.
Wacce mace ce kamar haka?
Duk da cewa tana da karancin shekaru, ta fi kowace mace da ya sani.
Yana sonta. Yana son ta fiye da yadda ya taba son wani abu a rayuwarsa.🥹
Amma yana tsoron furtawa.
Ya jima yana tunanin hakan. Idan ya fada mata, me zai faru?
Shin zata karba?
Shin zata fahimce shi?
Shin zata yi dariya kawai ta bar shi yana jin zuciyarsa na kuncewa?
Ya sauke ajiyar zuciya, yana jin bugun zuciyarsa na tsananta.
Nabeeha tana zaune a gefen gadonta, tana rike da wayar Humayrah da ta ajiye a gefenta. Hannunta da sanyi, zuciyarta na bugawa da sauri.
"Ya fawaaz..."
Shin da gaske yana son ganinta?
Me zai ce?
Meyasa yake ta ɓoye abu a zuciyarsa?
Tun da ya fara turo mata sakonni a rubuce, zuciyarta ta daina samun sukuni.
Tana son sanin dalilin da yasa yake haka.
Idan har yana da abin da yake ji a zuciyarsa, me zai hana ya fada?
Tayi shiru, tana jin zuciyarta na kokarin bata amsa,
"Ko kuwa miskilancinsa ne ke hana shi furtawa?"
Ta rike hannunta da hannu guda, tana jin yadda jikinta ke daukar zafi. Tana jin dadin yadda Fawaaz yake kula da ita, duk da cewa bai taba cewa tana da muhimmanci a gare shi ba.
Sai dai zuciyarta tana jin hakan.
Tana jin yadda idanunsa ke magana idan suka hada ido.
Tana jin yadda shiru yake da ma'ana idan suna tare.
Tana jin yadda kalmominsa ke bayyana da sauri a rubuce, amma ba zai iya fada da baki ba.
Tana jin yadda yake tsoron furta abu a bakinsa.
Tana jin yadda ya rasa yadda zai fada mata abin da zuciyarsa ke rayawa..
Ta lumshe idonta a hankali. Ta fahimci abu daya.
Fawaaz yana sonta.
Amma ya kasa furtawa.
Fawaaz ya tsaya yana kallon wayar da ke hannunsa. Sabuwar waya ce mai kyau da tsada, kirar zamani, wadda ya siya da sabon SIM a ciki. Tun kafin ya karɓi wannan matsaya, ya sha gwagwarmaya da zuciyarsa. Ya dade yana tunani, yana shan shakkar ko hakan daidai ne. Amma a ƙarshe, ya yanke shawara, yanzu lokaci ne na aikatawa, ba tunani ba.
Shiru ta yi, ba ta ce komai ba. A zahiri, ta ji kalmomin Muhammad, amma ba su shiga zuciyarta ba. Tunani kawai take—da ace Fawaaz ne ke furta mata hakan a baki, ba kawai a rubuce ba…
Yar wahalaaaaa🤭😏
Muhammad ya dan yi murmushi. "Kin yi shiru?"
Ta numfasa. "Ba komai."
"Ba ki ce komai ba akan abin da na fada."
Ta dafa goshinta. "Muhammad… Kai na ke ciwo. Yi.hakuri"
Ya yi shiru na wani lokaci. "Babu matsala. Amma a kalla ki san cewa na fadi abin da zuciyata ke ji. Kuma ba zan yi nadamar fada ba...Allah yakara miki lafiya da nisan kwana mai albarka amin"
Ta dan yi murmushi kadan. "Nagode."
Sun dan kara hira kadan, sannan suka yi sallama. Ta mika wa Humayrah wayarta, sannan ta koma ta kwanta, zuciyarta na kara cike da tunanin Fawaaz.
"Me yasa ya kasa furtawa a baki?"
"Me yasa ya ke boye abin da yake ji?"
"Ko kuwa yana fargabar abinda zai biyo baya?"
Watan wata rana… wata rana zai iya furtawa?
Bayan tattaunawarta da Muhammad, Nabeeha ta ajiye mikawa humyrah wayarta,. Sai dai, ko da suka yi sallama, ba kalmomin Muhammad take tunani ba—sai Fawaaz.
"Me yasa ya kasa furtawa a baki?"
Tana kwance kan gadonta, hannayenta sun dunkule a kirjinta, zuciyarta tana gudu da sauri. Ta rufe idanuwanta da karfi, tana kokarin korar tunanin da ya mamaye ta. Amma hakan bai yiwu ba.
Tunanin Fawaaz ya ci gaba da dawowa. Idanunta na kulle, ta fara tuno lokacin da ta fara lura da sauyin da ya faru da shi—lokacin da ya fara kallonta da wata irin kallo mai nauyi, lokacin da ta fara samun sakonninsa masu dauke da kalmomin da suka fi yadda yake iya furtawa.
"Ba zan iya furtawa a baki ba… amma ki sani, zuciyata ta yarda da ke."
"Ke ce abin da nake bukata, ko da kuwa duniya ba ta fahimta."
Tana da tabbacin cewa Fawaaz yana da wata irin soyayya a gare ta, amma ya kasa furtawa a fili. Me yasa? Shin miskilancinsa ne ke hana shi? Ko kuwa wani abu ne da ba ta sani ba?
Ta bude idonta, tana duban rufin dakin. "Idan har yana sona da gaske, me zai hana ya fada?"
Tana cikin wannan tunani ne sai aka turo kofar dakin.
"Nabeeha!"
Ta dago da sauri. Humayrah ce ke kokarin shigowa, fuskarta cike da murmushi.
"Mene ne kuma?" Nabeeha ta tambaya, tana zuba mata harara.
Humayrah ta zauna a gefen gadon, tana yatsina fuska. "Haba dai, ke kam. Me yasa kika yi kamar ba kya son magana da Muhammad?"
"Ban ce ba na son magana da shi ba."
"Amma ba ki nuna sha'awar tattaunawar ba."
Nabeeha ta dube ta da murmushin gefen baki. "Ke dai bari kawai, ina cikin tunani ne."
Humayrah ta mike tana kallonta. "Tunanin wani kike ko?"
Nabeeha ta zabura. "Me yasa kika ce haka?"
Humayrah ta harare ta. "Ai a yanzu haka, koda ace wani zai baka labari mai dadi, amma kana da wani abu a zuciyarka, ba za ka ji dadin labarin ba."
Ta yi shiru, tana nazarin maganar Humayrah. Ko da yake ba ta son yarda da hakan, amma akwai gaskiya a ciki.
"Ke dai bari kawai," ta ce, tana kokarin kawar da batun.
Humayrah ta yi dariya. "To Allah ya kyauta. Amma dai Muhammad na nan, yana jiranki ki yanke hukunci."
____
A gefe guda, Fawaaz yana zaune a kofar falonsa, cikin duhun dare. Ya jingina da kujerar da yake zaune a kai, hannunsa rike da wayarsa. Ya kafe screen din wayar da idanu, yana nazarin sakonnin da ya tura wa Nabeeha.
Ya sani. Ya sani cewa bai dace ya ci gaba da boye soyayyarsa ba. Ya sani cewa ba zai iya ci gaba da kamewa ba, amma me zai yi?
Zuciyarsa na cike da tsoro. Ba tsoron soyayya ba—tsoron abin da zai biyo baya.
Yana jin zuciyarsa na dukan abu guda. Idanunsa sun kada kadan saboda tunani da damuwa.
A can can, zuciyarsa na tambayarsa,
"Za ka ci gaba da ɓoye gaskiyar zuciyarka?"
"Ko kuwa lokaci ya yi da za ka bayyana?"
Ya sauke ajiyar zuciya, yana jin daren yana yi masa nauyi.
Numfashin Nabeeha ya tsaya cak. "Yaa Fawaaz?"
Muryarta ta fita da sanyi, tamkar ba ita ta yi magana ba.
A daya bangaren, shiru ne. Sai daga baya ta ji numfashinsa ya sauka kadan. "Eh, .. Zan iya ganinki?"
Wata irin kasala ta shige ta. Hannunta ya yi sanyi, zuciyarta na bugawa kamar zata fado daga kirjinta.
Me zai fada mata?
Meyasa yake neman ganinta a wannan dare ta intercom din dakin ta?
Tayi shiru, zuciyarta na kokarin tattaro amsar da zata bashi.
"Ina kusa da balcony. Idan har ba damuwa, ki fito."
Zuciyarta ta tsananta bugawa.
Shin ta fita?
Shin da gaske zai iya furtawa a yau?
Tana cikin wannan tunani ne sai aka turo kofar dakin. Humayrah ce.
"Ke! Waye haka yake magana da ke da daddare?" Ta tambaya, tana kokarin karbar wayar.
Da sauri Nabeeha ta kashe kiran, zuciyarta na harbawa. "Ba kowa."
Humayrah ta kalle ta da mamaki. "Ba kowa kuma? To me yasa kika kashe wayar da sauri?"
Nabeeha ta girgiza kai, tana kokarin boye rikicin zuciyarta. "Ki daina bincike mana."
Humayrah ta tabe baki. "To ai da gani akwai abu. Ko dai Muhammad ne ya kira?"
"A'a kuma ta intercom? ." Nabeeha ta fada da sauri, tana jin yadda zuciyarta ke ci gaba da dukan abu guda.
Humayrah ta yi shiru, sannan ta kalli gefenta. "Da gaske dai babu matsala?"
Nabeeha ta yi kokarin murmushi. "Eh, ki kwantar da hankalinki."
Amma ita kanta ta san cewa hankalinta ya tashi.
Ta mike daga gadon, zuciyarta na tafasa. Shin ta fita ta hadu da Fawaaz?
Ko kuwa ta share shi kamar yadda yake son boye soyayyarsa?
Fawaaz yana tsaye a jikin motarsa, hannayensa a cikin aljihu. Zuciyarsa na tafasa, yana jiran amsar Nabeeha.
Me zai ce idan ta fito?
Meyasa bai iya furtawa a da ba?
Ya sauke numfashi. "Yau, dole zan fada."
Idan har ba zai iya furtawa a yau ba, to zai iya rasa ta har abada.
_1-KALBIM:MAMUH GEE_
_2-KIRJIN MAI HANKALI (AKWATIN SIRRIN SA):MSS XOXO_
_3-ADUNIYATAH :HUGUMAH_
_4-AJIYA A DUHU: BILYN ABDULL_
°°
_1-BOOK DAYA:DARI BIYAR_
_2-BOOKS BIYU:DUBU DAYA_
_3-BOOKS UKU: DUBU DAYA DA DARI BIYAR_
_4-BOOKS HUDU :DUBU BIYU_
_5_YAN NIJAR: 1000CF: 89825722 NOUSAIBA LAWALI MARADI_
_ku tura receipt zuwa ga 09033181070_
*IDAN KATI NE A TURO TA WANNAN NUMBER:*
*09032345899.. SHEDAR KATIN MA NAN ZAA TURA. KATIN MTN!!MTN!!*
____
**KIRJIN MAI HANKALI*
_(AKWATIN SIRRIN SA)_
🧳➿💞
*PG :23*
*AREWABOOKS VVIP:👇*
https://www.arewabooks.com/book?id=670bd07e35879b101764c0eb
__
A tsakar dare, Fawaaz yana zaune a kan kujerar barandar gidan, hannunsa na jingine da gefen kujera, yana kallon sararin samaniya. Hasken wata yana haska filin gidan, yana ba da nutsuwa, amma zuciyarsa ba ta da nutsuwa ko kadan.
Me yake yi da zuciyarsa haka?
Ya rike goshinsa a hankali. Duk yadda ya so ya boye abin da ke ransa, ya kasa.
Yana son Nabeeha.
Bai san yadda zai iya rayuwa ba tare da ita ba.
Yana shakar numfashinta idan tana kusa.
Idan ta wuce ta gefensa, wani kamshi na musamman ke ratsa shi. Bai san ko menene ba, amma yana tabbatar da cewa ko a cikin taron mutane dari, zai iya gane Nabeeha.
Komai nata daban ne.
Tana da nutsuwa, tana da sanin ya kamata, tana da ilimi, tana da hankali fiye da yadda yawancin mata ke da shi.
Ba kawai kyawunta ba ne ya ke ja shi gare ta, dabi'arta ce, hankalinta, tausasawarta.
Ya yi murmushi a hankali. Ta na da tausayi.
Yana iya tuna yadda take tausaya wa kowa, har da wadanda ba su san tausayin wasu ba.
Ya kan ga yadda take rike da addininta, yadda take nisantar abin da bai dace ba. Ba wai tana takura wa kanta ba, amma tana da tsoron Allah.
Wacce mace ce kamar haka?
Duk da cewa tana da karancin shekaru, ta fi kowace mace da ya sani.
Yana sonta. Yana son ta fiye da yadda ya taba son wani abu a rayuwarsa.🥹
Amma yana tsoron furtawa.
Ya jima yana tunanin hakan. Idan ya fada mata, me zai faru?
Shin zata karba?
Shin zata fahimce shi?
Shin zata yi dariya kawai ta bar shi yana jin zuciyarsa na kuncewa?
Ya sauke ajiyar zuciya, yana jin bugun zuciyarsa na tsananta.
Nabeeha tana zaune a gefen gadonta, tana rike da wayar Humayrah da ta ajiye a gefenta. Hannunta da sanyi, zuciyarta na bugawa da sauri.
"Ya fawaaz..."
Shin da gaske yana son ganinta?
Me zai ce?
Meyasa yake ta ɓoye abu a zuciyarsa?
Tun da ya fara turo mata sakonni a rubuce, zuciyarta ta daina samun sukuni.
Tana son sanin dalilin da yasa yake haka.
Idan har yana da abin da yake ji a zuciyarsa, me zai hana ya fada?
Tayi shiru, tana jin zuciyarta na kokarin bata amsa,
"Ko kuwa miskilancinsa ne ke hana shi furtawa?"
Ta rike hannunta da hannu guda, tana jin yadda jikinta ke daukar zafi. Tana jin dadin yadda Fawaaz yake kula da ita, duk da cewa bai taba cewa tana da muhimmanci a gare shi ba.
Sai dai zuciyarta tana jin hakan.
Tana jin yadda idanunsa ke magana idan suka hada ido.
Tana jin yadda shiru yake da ma'ana idan suna tare.
Tana jin yadda kalmominsa ke bayyana da sauri a rubuce, amma ba zai iya fada da baki ba.
Tana jin yadda yake tsoron furta abu a bakinsa.
Tana jin yadda ya rasa yadda zai fada mata abin da zuciyarsa ke rayawa..
Ta lumshe idonta a hankali. Ta fahimci abu daya.
Fawaaz yana sonta.
Amma ya kasa furtawa.
Fawaaz ya tsaya yana kallon wayar da ke hannunsa. Sabuwar waya ce mai kyau da tsada, kirar zamani, wadda ya siya da sabon SIM a ciki. Tun kafin ya karɓi wannan matsaya, ya sha gwagwarmaya da zuciyarsa. Ya dade yana tunani, yana shan shakkar ko hakan daidai ne. Amma a ƙarshe, ya yanke shawara, yanzu lokaci ne na aikatawa, ba tunani ba.