Sashe 59
Kirjin Mai Hankali Part 2 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Zuciyarta ta yi nauyi da wani abu mai daɗi da ban tsoro a lokaci guda.
Shi kuwa ya gyara tsayuwa, yana kallonta cikin nutsuwa. "Ina so ki san cewa babu rana guda da zata wuce ba tare da na yi tunaninki ba."
Ta haɗiye yawu.
"Babu safiya da zata waye ba tare da zuciyata ta ambace ki ba."
Ta ƙura masa ido, zuciyarta na tafarfasa.
"Babu dare da zan kwanta ba tare da hotonki a cikin tunanina ba."
Ta numfasa, amma numfashin da bata san yana ɗauke da nauyi ba.
Shi kuwa, ya janye idonsa a hankali, yana duban sararin samaniya kamar yana magana da taurari.
"Idan har akwai soyayya da zata iya riƙe mutum gaba ɗaya, to ni na san cewa kin riga kin mallake ta a wajena."
Kallonta ya dawo kanta, cikin zurfin so da gaskiya.
"Nabeeha… ina son ki."
Hankalinta ya tsaya cak. Zuciyarta ta tsaya na ɗan lokaci, kafin ta cigaba da bugawa da wani irin yanayi da bata taɓa jin irinsa ba.
Fawaaz ya gyara tsayuwa, yana dubanta da kwanciyar hankali. "Kuma ba zan taɓa gajiya da faɗin hakan ba."
Ya numfasa a hankali, sannan ya ce, "Ko da baki ce komai ba… ko da kin ci gaba da ɓoye zuciyarki, zan tsaya har sai lokacin da kike da shirin bayyana min abinda take ji."
"Har abada, zan jira."
Shiru ya ratsa tsakaninsu. Amma shiru ne mai cike da nauyin soyayya da kalmomin da suka yi ƙaura a zuciya.
Nabeeha ta ji ƙafafunta sun gaza ɗaukar ta. Sai ta ɗauke idonta daga nasa, zuciyarta na tafasa da abu mai wuyar fassara.
Fawaaz kuwa, sai ya ja numfashi, sannan a hankali, ya matsa daga kusa da ita, yana kallonta da murmushi mai taushi.
"Zan wuce yanzu. Amma zan sake dawowa."
Ya juya a hankali, yana tafiya zuwa mota.
Daidai lokacin da ya shiga, sai ya sake kallonta, yana gyada kai. "Ki kula da kanki, Nabeeha."
Ya tada motarsa, ya fice a hankali, zuciyarsa na barin wani ɓangare a wajenta.
Ita kuwa, ta tsaya a wurin, har sai da sautin motarsa ya ɓace.
A hankali ta lumshe idonta, zuciyarta na tafasa da wani irin yanayi.
Bata san yaya zata yi da zuciyarta ba. Bata san wane mataki zata ɗauka ba.
Amma abu guda ta sani.
Soyayyar Fawaaz…
Tuni ta shiga jikinta, kuma bata san ko zata iya fita daga gare ta ba.
Nabeeha ta tsaya daram a wajen, zuciyarta na dokawa da wani irin sauti da bata taɓa ji ba. Hannunta ta ɗaura saman KIRJIN ta, tana jin yadda zuciyarta ke bugawa da sauri kamar zata tsinke.
Idanunta suka lumshe a hankali, kalmomin Fawaaz suna sake dawo mata a zuciya.
"Nabeeha… ina son ki."
Numfashinta ya ɗauke na wasu dakiku. Sai ta buɗe idanunta da sauri, ta ɗauke idonta daga inda motarsa ta ɓace.
Soyayya ce?
Zuciyarta ta ambace shi?
A hankali ta ɗaga hannunta, ta taɓa saitin zuciyarta da laushi. Ta girgiza kai da ƙyar, tana ƙoƙarin kawar da wannan tunanin.
Sai dai wani murya mai taushi ya faɗo mata a cikin zuciya.
"Har abada, zan jira."
Ta haɗiye yawu, zuciyarta na ƙoƙarin amincewa da wani abu da ita kanta bata gama fahimta ba.
Wani ganyen bishiya ya fado ya ratsa kusa da ita yana busa iska, sai ta dawo daga duniyar tunaninta. Ta sauke numfashi a hankali, sannan ta ɗaga ƙafafunta da ƙyar, ta juya zuwa cikin gida.
Tana jin kamar tana tafiya cikin wani sabon yanayi da bata taɓa sanin tana da shi ba.
Kuma a karo na farko…
Ta ji zuciyarta na yarda da abu guda.
Soyayyar Fawaaz…
Tuni ta fara ratsa tsokar zuciyarta, kuma bata da ikon tsayar da ita...
🎀🎀🎀
Gwaggo Hafsatu na zaune a kan gadonta, hannunta rike da carjib, tana jan karatu cikin nutsuwa. Hajiya Zaytunah ta shigo dakin a hankali, jikinta cike da lumana. Idanunta na bayyana natsuwa da shawara, duk da cewa zuciyarta tana bugawa da karfin gaske.
“Gwaggo…” Ta kira da murya kasa, tana durkusawa gabanta.
Gwaggo Hafsatu ta janye kallonta daga abunda take, ta kalli Zaytunah da idanu masu cike da hikima. “Na’am, Zaytunah.”
Ta dan numfasa, sannan ta lumshe ido na wasu dakiku kafin ta bude. “Na gama istikhara, Gwaggo. Na ji kwanciyar HANKALI a raina. Na yanke shawarar komawa gidan mijina.”
Shiru ya ratsa dakin na ‘yan dakiku. Gwaggo Hafsatu ta ajiye misbah dinta a hankali, tana nazarin fuskarta. Ta sauke ajiyar zuciya sannan ta yi murmushi mai cike da farin ciki.
“Alhamdulillah,” ta fada da sigar godiya. “Allah Ya tabbatar da alheri.”
Zaytunah ta gyada kai da girmamawa, zuciyarta tana karbar kalmomin da natsuwa.
Gwaggo Hafsatu ta kai hannu ta rike nata. “Zaytunah, komawar ki gidan Alhaji Uzairu ba matsala ba ce, amma ki tabbatar kin shiga da addu’a. Duk wanda ya dogara ga Allah, ba zai tozarta ba.”
Cikin sanyin murya, Zaytunah ta amsa, “Na yarda, Gwaggo. Da addu’a zan shiga.”
Gwaggo Hafsatu ta dafa hannunta cikin kulawa. “Allah Ya albarkaci zaman ki.”
....
Motar Fawaaz ta tsaya a gefen titi a gaban wani gida mai tsari. A cikin motar, shi da Nabeeha suna zaune, amma babu wanda ke magana. Sai shiru mai cike da nauyi.
A hankali ya juyo ya kalleta, idanunsa masu zurfi da kwarjini sun ratsa ta.
“Ki shigo ki gaisa da Humyrah, amma...” Ya dakata kadan, yana dauke kansa kamar ba ya so ya fadi abin da ke ransa. “Kada ki dade.” ya karasa fada ahankali..
Nabeeha ta dan saki murmushi, sai dai ba ta kalle shi ba. “Toh.”
Ta bude kofar motar ta fito. Duk da sanyin dare da ke tashi, tana jin zafin bugun zuciyarta. Fawaaz ya kara gyara zaman sa, amma bai dauke idanunsa daga kanta ba har sai da ta bace cikin gidan.
Humyrah ta karbi Nabeeha da murmushi mai cike da tsokana. Kafin ma su zauna da kyau, ta riga ta fara dariya.
“Nabeeha, kin san me?”
Ta dan dago ido tana kallonta. “Mene?”
Humyrah ta dan rankwafa kadan, tana kallonta da wani kallo na tsokana. “Tun shekarun baya nake tunanin cewa Yaya Fawaaz yana kaunarki.”
Nabeeha ta dan zaro ido da mamaki, sannan ta kada kai da sauri. “Ke dai Humyrah, me ya sa kike tunani haka?”
Humyrah ta tabe baki. “Ai yana bayyane! Yanda yake kula da ke, tsananin tsaro da yake bamu, yadda baya barin kowa ya shiga tsakaninku…” Ta ja numfashi, sannan ta dan yamutsa fuska. “Ko da yake, miskili ne, sai da wuya ya nuna abin da ke zuciyarsa.”
Nabeeha ta dan saki murmushi, zuciyarta na bugawa da sauri.
Suka zauna. Ta cika gaban Nabeeha da kayan kwalam. Kafin daga bisani ta fita da kanta da drinks da snacks ta kaiwa yayan nata suka gaysa. Sannan ta dawo wajen nabeeha suka cigaba da hirar su..
Fawaaz na tsaye a gefen motarsa, hannayensa a kugu. Fuskar sa kamar yadda aka saba—ba yabo ba fallasa. Amma idanunsa sun nuna yana cikin tunani mai zurfi.
A hankali, yaga Nabeeha ta fito daga gidan, tana tafiya cikin nutsuwa kamar yadda ya saba hangota.
Bai ce komai ba har sai da ta karasa kusa da shi. Ta tsaya, tana kallonsa da ido masu cike da tambayoyi.
Ya dan numfasa, sannan ya furta da murya mai kwarjini amma cike da saukin gaske.
“Nabeeha…”
Ta dago kai tana kallonsa, zuciyarta na bugawa da sauri.
Shiru ya ratsa tsakaninsu, sai sanyin iska da ke kadawa a hankali.
Daga nan sai ya matsa kusa da ita, yana kallon cikin idanunta kai tsaye.
“Kin san abin da ke cikin KIRJIN duk wani MAI HANKALI?”
Ta dan girgiza kai a hankali, idanunta na bayyana sha’awar jin amsar.
Ya lumshe ido na wasu dakiku, yana dauke numfashi, kafin ya bude su da wani yanayi na soyayya mai cike da natsuwa.
“AKWATIN SIRRIN SA ne,” ya furta da murya kasa kasa.
Hannunta ya dan motsa, kamar tana son rikewa da gaske. Amma sai ta tsaya, tana kallonsa da wata shaukin fuska.
Shi kuma ya ci gaba, “Kuma kinsan mene ne SIRRI na?”
Ta sake girgiza kai, zuciyarta na neman dukan kirjin ta.
Ya yi murmushin da ba kasafai ake ganinsa da shi ba. A hankali, ya rike hannunta, yana kallonta da wani yanayi na dabara.
“Ke ce, Nabeeha.”
ADVERT👇
YERWA INCENSE AND MORE
YERWA INCENSE AND MORE
YERWA INCENSE AND MORE
(THE SCENTS WITH DIFFERENT ESSENCE FOR YOU AND YOUR HOME)
(MASARAUTAR KAYAYYAKIN KAMSHI)
INA MA'ABOTA TURARE!
Shin kuna son gida mai ƙamshi da nutsuwa? Kaya masu ɗaukar hankalin kowa? YERWA INCENSE AND MORE ta kawo muku kayayyakin turaruka masu kyau, ingantattu, da tsada mai rahusa!
🌟 Mene ne za ku samu?
Turarukan wuta don gida, kaya, da tsugunno.
Khumrahs masu kamshi irin na Borno, Chadi, da Sudan.
Oil perfumes masu daɗin kamshi mai ɗorewa.
Turaren wanka, mopping, da wanki don dukkan sassan gida.
Man gashi mai gyara da fesa kamshi mai dadi.
Kayayyakin gyaran jiki na musamman don lafiya da ƙamshi mai ɗorewa.
📍 Adireshi:
Kano, amma muna tura kayayyakin mu duk fadin Najeriya da ƙetare.
📞 Tuntuɓe mu:
WhatsApp ko kira: 08095215215 / 09044191709 / 09134848107
Instagram: @yerwaincense_and_more
Facebook: @yerwacollection
Twitter:Hafsaaat00
🌐 Don ƙarin bayani da hotunan kayayyakin mu: Ku ziyarta mu a TikTok:
@besturarenwutainkano
https://www.tiktok.com/@besturarenwutainkano?_t=ZM-8s89xrbgS3x&_r=1
🎉 DON RAGI NA MUSAMMAN: Idan za ku siya, ku faɗi cewa daga ZAFAFA ne!
🌹 Ku more gida da jiki mai kamshi, nutsuwa, da farin ciki. Sai dai kayan turaren YERWA INCENSE AND MORE!
*KIRJIN MAI HANKALI*
_(Akwatin sirrin sa)_
_🧳👩❤️👨🌺_
*_The Vault Of His Secrets_*
_®️NANA HAFSATU (MX)_
_©️ZAFAFA BIYAR WRITERS_
*_BOOK TWO_*
_PAGE:53_
Nabeeha ta tsaya cak, idanunta sun kasa dauke wa daga nasa. Zuciyarta na bugawa da sauri fiye da kowane lokaci. Kalmar da ya fada ta ratsa ta, ta tsaya a zuciyarta kamar an rubuta da bakin zinariya.
"Ke ce, Nabeeha."
Ba ta san lokacin da ta dan saki numfashi ba. A karo na farko, ta fahimci cewa Fawaaz ba kawai mai kareta ba ne, zuciyarsa na tare da ita.
Fawaaz ya dan kalleta, sai kuma ya dauke kansa kamar ba shi da abin cewa. Amma hannunsa da ke rike da nata bai motsa ba. Sai ma ya kara matse shi a hankali, yana jin yadda tafin hannunta ke sanyi kamar yana jin bugun zuciyarta ta ratsa nashi.
“Nabeeha…” Ya kira sunanta cikin nutsuwa.
Shi kuwa ya gyara tsayuwa, yana kallonta cikin nutsuwa. "Ina so ki san cewa babu rana guda da zata wuce ba tare da na yi tunaninki ba."
Ta haɗiye yawu.
"Babu safiya da zata waye ba tare da zuciyata ta ambace ki ba."
Ta ƙura masa ido, zuciyarta na tafarfasa.
"Babu dare da zan kwanta ba tare da hotonki a cikin tunanina ba."
Ta numfasa, amma numfashin da bata san yana ɗauke da nauyi ba.
Shi kuwa, ya janye idonsa a hankali, yana duban sararin samaniya kamar yana magana da taurari.
"Idan har akwai soyayya da zata iya riƙe mutum gaba ɗaya, to ni na san cewa kin riga kin mallake ta a wajena."
Kallonta ya dawo kanta, cikin zurfin so da gaskiya.
"Nabeeha… ina son ki."
Hankalinta ya tsaya cak. Zuciyarta ta tsaya na ɗan lokaci, kafin ta cigaba da bugawa da wani irin yanayi da bata taɓa jin irinsa ba.
Fawaaz ya gyara tsayuwa, yana dubanta da kwanciyar hankali. "Kuma ba zan taɓa gajiya da faɗin hakan ba."
Ya numfasa a hankali, sannan ya ce, "Ko da baki ce komai ba… ko da kin ci gaba da ɓoye zuciyarki, zan tsaya har sai lokacin da kike da shirin bayyana min abinda take ji."
"Har abada, zan jira."
Shiru ya ratsa tsakaninsu. Amma shiru ne mai cike da nauyin soyayya da kalmomin da suka yi ƙaura a zuciya.
Nabeeha ta ji ƙafafunta sun gaza ɗaukar ta. Sai ta ɗauke idonta daga nasa, zuciyarta na tafasa da abu mai wuyar fassara.
Fawaaz kuwa, sai ya ja numfashi, sannan a hankali, ya matsa daga kusa da ita, yana kallonta da murmushi mai taushi.
"Zan wuce yanzu. Amma zan sake dawowa."
Ya juya a hankali, yana tafiya zuwa mota.
Daidai lokacin da ya shiga, sai ya sake kallonta, yana gyada kai. "Ki kula da kanki, Nabeeha."
Ya tada motarsa, ya fice a hankali, zuciyarsa na barin wani ɓangare a wajenta.
Ita kuwa, ta tsaya a wurin, har sai da sautin motarsa ya ɓace.
A hankali ta lumshe idonta, zuciyarta na tafasa da wani irin yanayi.
Bata san yaya zata yi da zuciyarta ba. Bata san wane mataki zata ɗauka ba.
Amma abu guda ta sani.
Soyayyar Fawaaz…
Tuni ta shiga jikinta, kuma bata san ko zata iya fita daga gare ta ba.
Nabeeha ta tsaya daram a wajen, zuciyarta na dokawa da wani irin sauti da bata taɓa ji ba. Hannunta ta ɗaura saman KIRJIN ta, tana jin yadda zuciyarta ke bugawa da sauri kamar zata tsinke.
Idanunta suka lumshe a hankali, kalmomin Fawaaz suna sake dawo mata a zuciya.
"Nabeeha… ina son ki."
Numfashinta ya ɗauke na wasu dakiku. Sai ta buɗe idanunta da sauri, ta ɗauke idonta daga inda motarsa ta ɓace.
Soyayya ce?
Zuciyarta ta ambace shi?
A hankali ta ɗaga hannunta, ta taɓa saitin zuciyarta da laushi. Ta girgiza kai da ƙyar, tana ƙoƙarin kawar da wannan tunanin.
Sai dai wani murya mai taushi ya faɗo mata a cikin zuciya.
"Har abada, zan jira."
Ta haɗiye yawu, zuciyarta na ƙoƙarin amincewa da wani abu da ita kanta bata gama fahimta ba.
Wani ganyen bishiya ya fado ya ratsa kusa da ita yana busa iska, sai ta dawo daga duniyar tunaninta. Ta sauke numfashi a hankali, sannan ta ɗaga ƙafafunta da ƙyar, ta juya zuwa cikin gida.
Tana jin kamar tana tafiya cikin wani sabon yanayi da bata taɓa sanin tana da shi ba.
Kuma a karo na farko…
Ta ji zuciyarta na yarda da abu guda.
Soyayyar Fawaaz…
Tuni ta fara ratsa tsokar zuciyarta, kuma bata da ikon tsayar da ita...
🎀🎀🎀
Gwaggo Hafsatu na zaune a kan gadonta, hannunta rike da carjib, tana jan karatu cikin nutsuwa. Hajiya Zaytunah ta shigo dakin a hankali, jikinta cike da lumana. Idanunta na bayyana natsuwa da shawara, duk da cewa zuciyarta tana bugawa da karfin gaske.
“Gwaggo…” Ta kira da murya kasa, tana durkusawa gabanta.
Gwaggo Hafsatu ta janye kallonta daga abunda take, ta kalli Zaytunah da idanu masu cike da hikima. “Na’am, Zaytunah.”
Ta dan numfasa, sannan ta lumshe ido na wasu dakiku kafin ta bude. “Na gama istikhara, Gwaggo. Na ji kwanciyar HANKALI a raina. Na yanke shawarar komawa gidan mijina.”
Shiru ya ratsa dakin na ‘yan dakiku. Gwaggo Hafsatu ta ajiye misbah dinta a hankali, tana nazarin fuskarta. Ta sauke ajiyar zuciya sannan ta yi murmushi mai cike da farin ciki.
“Alhamdulillah,” ta fada da sigar godiya. “Allah Ya tabbatar da alheri.”
Zaytunah ta gyada kai da girmamawa, zuciyarta tana karbar kalmomin da natsuwa.
Gwaggo Hafsatu ta kai hannu ta rike nata. “Zaytunah, komawar ki gidan Alhaji Uzairu ba matsala ba ce, amma ki tabbatar kin shiga da addu’a. Duk wanda ya dogara ga Allah, ba zai tozarta ba.”
Cikin sanyin murya, Zaytunah ta amsa, “Na yarda, Gwaggo. Da addu’a zan shiga.”
Gwaggo Hafsatu ta dafa hannunta cikin kulawa. “Allah Ya albarkaci zaman ki.”
....
Motar Fawaaz ta tsaya a gefen titi a gaban wani gida mai tsari. A cikin motar, shi da Nabeeha suna zaune, amma babu wanda ke magana. Sai shiru mai cike da nauyi.
A hankali ya juyo ya kalleta, idanunsa masu zurfi da kwarjini sun ratsa ta.
“Ki shigo ki gaisa da Humyrah, amma...” Ya dakata kadan, yana dauke kansa kamar ba ya so ya fadi abin da ke ransa. “Kada ki dade.” ya karasa fada ahankali..
Nabeeha ta dan saki murmushi, sai dai ba ta kalle shi ba. “Toh.”
Ta bude kofar motar ta fito. Duk da sanyin dare da ke tashi, tana jin zafin bugun zuciyarta. Fawaaz ya kara gyara zaman sa, amma bai dauke idanunsa daga kanta ba har sai da ta bace cikin gidan.
Humyrah ta karbi Nabeeha da murmushi mai cike da tsokana. Kafin ma su zauna da kyau, ta riga ta fara dariya.
“Nabeeha, kin san me?”
Ta dan dago ido tana kallonta. “Mene?”
Humyrah ta dan rankwafa kadan, tana kallonta da wani kallo na tsokana. “Tun shekarun baya nake tunanin cewa Yaya Fawaaz yana kaunarki.”
Nabeeha ta dan zaro ido da mamaki, sannan ta kada kai da sauri. “Ke dai Humyrah, me ya sa kike tunani haka?”
Humyrah ta tabe baki. “Ai yana bayyane! Yanda yake kula da ke, tsananin tsaro da yake bamu, yadda baya barin kowa ya shiga tsakaninku…” Ta ja numfashi, sannan ta dan yamutsa fuska. “Ko da yake, miskili ne, sai da wuya ya nuna abin da ke zuciyarsa.”
Nabeeha ta dan saki murmushi, zuciyarta na bugawa da sauri.
Suka zauna. Ta cika gaban Nabeeha da kayan kwalam. Kafin daga bisani ta fita da kanta da drinks da snacks ta kaiwa yayan nata suka gaysa. Sannan ta dawo wajen nabeeha suka cigaba da hirar su..
Fawaaz na tsaye a gefen motarsa, hannayensa a kugu. Fuskar sa kamar yadda aka saba—ba yabo ba fallasa. Amma idanunsa sun nuna yana cikin tunani mai zurfi.
A hankali, yaga Nabeeha ta fito daga gidan, tana tafiya cikin nutsuwa kamar yadda ya saba hangota.
Bai ce komai ba har sai da ta karasa kusa da shi. Ta tsaya, tana kallonsa da ido masu cike da tambayoyi.
Ya dan numfasa, sannan ya furta da murya mai kwarjini amma cike da saukin gaske.
“Nabeeha…”
Ta dago kai tana kallonsa, zuciyarta na bugawa da sauri.
Shiru ya ratsa tsakaninsu, sai sanyin iska da ke kadawa a hankali.
Daga nan sai ya matsa kusa da ita, yana kallon cikin idanunta kai tsaye.
“Kin san abin da ke cikin KIRJIN duk wani MAI HANKALI?”
Ta dan girgiza kai a hankali, idanunta na bayyana sha’awar jin amsar.
Ya lumshe ido na wasu dakiku, yana dauke numfashi, kafin ya bude su da wani yanayi na soyayya mai cike da natsuwa.
“AKWATIN SIRRIN SA ne,” ya furta da murya kasa kasa.
Hannunta ya dan motsa, kamar tana son rikewa da gaske. Amma sai ta tsaya, tana kallonsa da wata shaukin fuska.
Shi kuma ya ci gaba, “Kuma kinsan mene ne SIRRI na?”
Ta sake girgiza kai, zuciyarta na neman dukan kirjin ta.
Ya yi murmushin da ba kasafai ake ganinsa da shi ba. A hankali, ya rike hannunta, yana kallonta da wani yanayi na dabara.
“Ke ce, Nabeeha.”
ADVERT👇
YERWA INCENSE AND MORE
YERWA INCENSE AND MORE
YERWA INCENSE AND MORE
(THE SCENTS WITH DIFFERENT ESSENCE FOR YOU AND YOUR HOME)
(MASARAUTAR KAYAYYAKIN KAMSHI)
INA MA'ABOTA TURARE!
Shin kuna son gida mai ƙamshi da nutsuwa? Kaya masu ɗaukar hankalin kowa? YERWA INCENSE AND MORE ta kawo muku kayayyakin turaruka masu kyau, ingantattu, da tsada mai rahusa!
🌟 Mene ne za ku samu?
Turarukan wuta don gida, kaya, da tsugunno.
Khumrahs masu kamshi irin na Borno, Chadi, da Sudan.
Oil perfumes masu daɗin kamshi mai ɗorewa.
Turaren wanka, mopping, da wanki don dukkan sassan gida.
Man gashi mai gyara da fesa kamshi mai dadi.
Kayayyakin gyaran jiki na musamman don lafiya da ƙamshi mai ɗorewa.
📍 Adireshi:
Kano, amma muna tura kayayyakin mu duk fadin Najeriya da ƙetare.
📞 Tuntuɓe mu:
WhatsApp ko kira: 08095215215 / 09044191709 / 09134848107
Instagram: @yerwaincense_and_more
Facebook: @yerwacollection
Twitter:Hafsaaat00
🌐 Don ƙarin bayani da hotunan kayayyakin mu: Ku ziyarta mu a TikTok:
@besturarenwutainkano
https://www.tiktok.com/@besturarenwutainkano?_t=ZM-8s89xrbgS3x&_r=1
🎉 DON RAGI NA MUSAMMAN: Idan za ku siya, ku faɗi cewa daga ZAFAFA ne!
🌹 Ku more gida da jiki mai kamshi, nutsuwa, da farin ciki. Sai dai kayan turaren YERWA INCENSE AND MORE!
*KIRJIN MAI HANKALI*
_(Akwatin sirrin sa)_
_🧳👩❤️👨🌺_
*_The Vault Of His Secrets_*
_®️NANA HAFSATU (MX)_
_©️ZAFAFA BIYAR WRITERS_
*_BOOK TWO_*
_PAGE:53_
Nabeeha ta tsaya cak, idanunta sun kasa dauke wa daga nasa. Zuciyarta na bugawa da sauri fiye da kowane lokaci. Kalmar da ya fada ta ratsa ta, ta tsaya a zuciyarta kamar an rubuta da bakin zinariya.
"Ke ce, Nabeeha."
Ba ta san lokacin da ta dan saki numfashi ba. A karo na farko, ta fahimci cewa Fawaaz ba kawai mai kareta ba ne, zuciyarsa na tare da ita.
Fawaaz ya dan kalleta, sai kuma ya dauke kansa kamar ba shi da abin cewa. Amma hannunsa da ke rike da nata bai motsa ba. Sai ma ya kara matse shi a hankali, yana jin yadda tafin hannunta ke sanyi kamar yana jin bugun zuciyarta ta ratsa nashi.
“Nabeeha…” Ya kira sunanta cikin nutsuwa.