Sashe 30
Kirjin Mai Hankali Part 2 Complete Hausa Novel · about 8 min read
"Uzairu, lokaci ya yi da za ka tsayu ka fuskanci gaskiya," ta fada cikin nutsuwa. "Idan ka yi sakaci, abin da zai biyo baya ka iya zama mafi muni fiye da yadda kake tunani."
Alhaji Uzairu ya bude ido, yana kallonta. Har yanzu zuciyarsa ba ta gama karbar gaskiyar abin da ake fada masa ba. Sai dai yana jin nauyinsa sosai.
Alhaji Amiru ya yi gyaran murya.
"Maganar gaskiya, ba zamu jira har su sake kokarin cutar da Zaytunah ba," ya ce da kwarin gwiwa. "Dole ne mu kai rahoto wajen Major General Dawud. Shi ne kadai zai iya magance wannan matsala cikin gaggawa."
Gwaggo Zainabu ta jinjina kai.
"Hakan daidai ne," ta ce. "Amma kada mu manta cewa idan suka fahimci cewa an gano su, to ba abin da ba za su iya aikatawa ba domin su kare kansu."
Haruna ya gyada kai.
"Tabbas, su Karama da kishiyoyinta ba za su yi kasa a gwiwa ba idan suka ji cewa an bankado SIRRIN su," ya ce. "Wannan shine dalilin da ya sa dole a yi komai a hankali, ba tare da sun fahimta ba."
Alhaji Uzairu ya gyara zamansa, ya dubi Alhaji Amiru da Gwaggo Zainabu.
"To yanzu, ya za ayi?" ya tambaya cikin damuwa.
Alhaji Amiru ya yi shiru na dan lokaci, kafin ya kalli Haruna.
"Ka shirya ka sake tafiya wajen boka?" ya tambaya.
Haruna ya yi ajiyar zuciya, ya kalli su duka.
"Idan hakan zai tabbatar da cewa muna da cikakken shaida, zan sake komawa," ya ce cikin karfin hali. "Sai dai, dole a yi HANKALI kada su fahimci cewa ana bincikensu."
Gwaggo Zainabu ta dubi Alhaji Uzairu.
"Uzairu, kana da tabbacin cewa za ka iya hada kai da mu wajen ganin an yi adalci?"
Alhaji Uzairu ya dago idanuwansa, yana kallon kowa daya bayan daya. A zuciyarsa, yana jin radadin cewa iyalinsa sun fi kowa cutar da shi. Bai taba tunanin cewa akwai wata rana da za a gaya masa irin wannan abu ba.
Ya numfasa, sannan ya gyada kai.
"Na amince," ya ce a hankali. "Ba zan bari su kashe min iyali ba."
Alhaji Amiru ya sauke ajiyar zuciya mai nauyi.
"To, lokaci bai yi ba da za mu tafi wajen Major General Dawud ba?"
Gwaggo Zainabu ta gyada kai.
"Yanzu ne lokaci. Ba za mu jira har sai wani abu ya faru ba."
Alhaji Amiru ya mike tsaye.
A nan suka yanke shawarar tafiya wajen Major General Dawud, don a dauki matakin kare Zaytunah daga mummunar makarkashiya da kishiyoyinta suka kitsa...
Suna fitowa daga falon, kowanne daga cikinsu zuciyarsa cike da tunani. Alhaji Uzairu yana bin su da baya, har yanzu kansa a kulle yake da abubuwan da suka faru. Bai taba tunanin cewa wata rana zai fuskanci wannan matsala daga matansa ba.
Haruna ne ya dauki nauyin tukin motar, yayin da Alhaji Amiru da Alhaji Uzairu suka zauna a bayan mota, kowanne cikin nitsuwa. A lokacin da motar ta bar harabar sashen Gwaggo Zainabu, shiru ya ratsa cikin su.
Alhaji Uzairu ya lumshe idanu, yana jin yadda zuciyarsa ke bugawa da karfi. Abin da ke faruwa ya girgiza shi matuka.
“Uzairu, ka tabbatar cewa kana da ƙarfin zuciyar fuskantar abin da zai biyo baya?” Alhaji Amiru ya tambaya, yana dubansa.
Alhaji Uzairu ya bude idanu, ya dubi dan uwansa. “Dole na yi hakan, Yaya Amiru,” ya ce da karfin hali. “Ba zan iya bari su hallaka min ‘ya’ya ba.”
Haruna ya cigaba da tuƙi cikin nutsuwa, yana bin titin da zai kaisu gidan Major General Dawud.
MAJOR GENERAL DAWUD MAFIA RES:
A lokacin da suka isa, an shigo da su kai tsaye zuwa falon ba tare da wata matsala ba. Major General Dawud yana sanye da kayan gida, yana zaune bisa kujerar da ke gefen babban falonsa. Da gani, yana cikin shirin hutawa ne kafin su shigo.
Ya kalli su daya bayan daya, kafin ya maida kallonsa ga Alhaji Amiru.
“Kun zo da gaggawa, Amiru,” ya fada a hankali. “Ina sauraronku.”
Alhaji Amiru ya sauke ajiyar zuciya, sannan ya fara bayanin komai dalla-dalla. Ya fada masa yadda Haruna ya bi matan Alhaji Uzairu har wajen boka, yadda ya ji su da kunnuwansa suna tsara kashe Zaytunah, da yadda Alhaji Uzairu ya kasa yarda da hakan har sai an kawo hujja mai karfi.
A lokacin da Alhaji Amiru ya kai karshe, fuskar Major General Dawud ta nuna tsananin ɓacin rai.
“Kun tabbatar da cewa wannan maganar gaskiya ce?” ya tambaya, yana duban Haruna da tsananin ido.
Haruna ya gyada kai. “Wallahi, babu shakka akan haka, ranka ya dade,” ya ce da tabbaci.
Major General Dawud ya jingina da kujera, yana tunani na wani lokaci.
“Idan haka ne, lamarin yana bukatar gaggawa,” ya ce a hankali. “Ba zan bari komai ya same su Zaytunah ba. Fata dai a same sun..”
Ya dubi Alhaji Uzairu da kyau. “Uzairu,” ya kira sunansa da kakkausar murya. “Kana da tabbacin cewa ba za ka yi wata-wata wajen daukar mataki akan wannan lamari ba?”
Alhaji Uzairu ya lumshe ido, yana jin nauyin kalmomin Major General Dawud. Da farko, yana jin kamar abin kamar mafarki ne, amma yanzu ya san babu gudu ba ja da baya.
“Na tabbatar,” ya amsa cikin muryar da ke nuna yanke shawara.
Major General Dawud ya mike tsaye. “To, ku jira ni,” ya fada.
Ya yi gaba zuwa wani daki, sannan ya fito cikin uniform dinsa, yana daure da damara. Fuskar sa a daure take, alamun ya gama yanke shawara akan abin da zai yi.
“Za a tsaurara tsaro Inn shaa' Allah"
Ya kalli su duka, sannan ya dauki wayarsa. “Kuma ba zan tsaya nan ba. Sai mun tabbatar da cewa an hukunta duk wanda ke da hannu a wannan makirci.”
Alhaji Uzairu ya runtse ido, zuciyarsa cike da nauyi. Ya san cewa daga wannan rana, rayuwar sa ba za ta kara zama kamar yadda take a da ba...
_1-KALBIM:MAMUH GEE_
_2-KIRJIN MAI HANKALI (AKWATIN SIRRIN SA):MSS XOXO_
_3-ADUNIYATAH :HUGUMAH_
_4-AJIYA A DUHU: BILYN ABDULL_
°°
_1-BOOK DAYA:DARI BIYAR_
_2-BOOKS BIYU:DUBU DAYA_
_3-BOOKS UKU: DUBU DAYA DA DARI BIYAR_
_4-BOOKS HUDU :DUBU BIYU_
_5_YAN NIJAR: 1000CF: 89825722 NOUSAIBA LAWALI MARADI_
_ku tura receipt zuwa ga 09033181070_
*IDAN KATI NE A TURO TA WANNAN NUMBER:*
*09032345899.. SHEDAR KATIN MA NAN ZAA TURA. KATIN MTN!!MTN!!*
____
*KIRJIN MAI HANKALI*
_(Akwatin sirrin sa)_
_🧳👩❤️👨🌺_
*_The Vault Of His Secrets_*
_®️NANA HAFSATU (MX)_
_©️ZAFAFA BIYAR WRITERS_
*_BOOK TWO_*
_PAGE:26_
Da Alhaji Uzairu ya iso gida, bai wuce kai tsaye zuwa dakinsa ba. Maimakon haka, ya tsaya a babban falon gida inda matansa, Hajiya da Hajiya Karama, suke zaune suna tattauna wasu batutuwa a tsakaninsu. A ganinsa, kamar dai suna magana ne da nutsuwa, amma da zarar suka hango shi, sai suka yi shiru tamkar wadanda aka kama da laifi.
Ya zuba musu ido na dan lokaci ba tare da ya ce komai ba. Sai da ya zauna a kujera ya dora kafa daya kan daya, sannan ya gyara zama, yana jin nauyin da ke cikin zuciyarsa.
"Hajiya," ya kira sunan matar sa ta farko, "yau na wuni a gidan Ya Amiru."
Hajiya ta kalle shi cikin kulawa. "Lafiya dai? Ka dawo da wuri yau."
"Eh, ai ba wani abu," ya fada, yana juyawa zuwa ga Hajiya Karama.
"Mun yi doguwar hira da Alhaji Amiru da Gwaggo Zainabu. Sun yi tambayoyi da yawa game da rayuwar mu."
A take, Hajiya Karama ta hadiye yawu. "Tambayoyi irin na menene kuma?"
Alhaji Uzairu ya girgiza kai. "Kawai dai wasu tsofaffin batutuwa ne… da kuma wasu abubuwan da suka shafi rayuwar mu a baya."
Hajiya ta dube shi da dan tsoro. "Rayuwa ta baya fa?"
Sai ya gyada kai a hankali, yana kallonsu dukkansu. "Kusan shekara goma kenan da wasu abubuwa suka faru… kuma sai yanzu suke tambayata su kansu. Abin mamaki, ko ba haka ba?"
Hajiya Karama ta shiga girgiza kai. "To, me ya sa sai yanzu suka tuna? Ai da ace wani abu ne mai muhimmanci, da tuni sun yi magana da kai a baya."
Alhaji Uzairu ya dan saki murmushi mara dadi. "Hakan nake tunani. Amma kin san wani abu? Na fara jin kamar akwai wani abu da ba a gaya min ba. Kuma hakan yana bani mamaki sosai."
Hajiya karama ta dan yi dariya. "Me kake nufi da wani abu da ba a gaya maka ba? Me ya sa kake tunanin haka?"
Sai ya jingina da kujera, yana dubansu dukkansu da idon bincike...
"Hakane," ya ce yana kallonsu da ido mai zurfi, "amma abin da ya faru bai shuɗe haka kawai ba. Ko dai wani ne ya sa hannu, ko kuma akwai wani SIRRI da ake boyewa."
Hajiya da Hajiya Karama suka kalli juna a lokaci guda, tamkar suna kokarin jin wace za ta fara magana. Sai dai dukkansu sun kasa cewa komai nan take.
Alhaji Uzairu ya gyara zama, yana nazarinsu. "Kun san abinda ya fi bani mamaki?"
Hajiya Karama ta yi saurin girgiza kai. "A’a."
Ya sake dubansu duka, sannan ya furta a hankali: "Yadda duk sanda aka ambaci sunan Zaytunah, sai ku dinga kokarin gujewa maganar."
A take, Hajiya ta ɗan ja numfashi. "Ba haka bane, Alhaji. Ai ba wai muna gujewa bane, kawai dai... ba mu ga amfanin tada wannan batu ba."
"Ba ku ga amfaninsa ba?" Ya jinjina kansa, yana kallonsu da kyau. "Matar aure ce, Mahaifiya ga yayanta. Yara biyu. , baƙar rana daya ta ɓace, har yau ba a san inda take ba da iyalanta, ba a san ko tana raye ba ko kuma..." Ya dan dakata, yana son ganin yadda za su karɓi kalmomin nasa.
Hajiya Karama ta sake gyara zama, ta lumshe ido na ɗan lokaci, kamar tana tunanin wani abu. Da ta buɗe su, sai ta ce da ƙasa-ƙasa: "Ai Allah kadai yasan inda take, Alhaji."
Alhaji Uzairu ya haɗiye yawu. Yanzu ya fara jin wata irin hujja a cikin muryarta. "Kun tabbata?" Ya tambaya, yana jefa musu wani irin kallo da ya sa dukansu suka rasa yadda za su mayar masa da martani.
Hajiya ta ɗauke kanta gefe, yayin da Hajiya Karama ta sunkuyar da kai. Wannan ne karon farko da ya tabbatar da cewa akwai wani abu da suke ɓoyewa. SIRRI ne da suka daɗe suna rufewa, amma yanzu lokaci ya kusa da za a tona komai.
Alhaji Uzairu ya bude ido, yana kallonta. Har yanzu zuciyarsa ba ta gama karbar gaskiyar abin da ake fada masa ba. Sai dai yana jin nauyinsa sosai.
Alhaji Amiru ya yi gyaran murya.
"Maganar gaskiya, ba zamu jira har su sake kokarin cutar da Zaytunah ba," ya ce da kwarin gwiwa. "Dole ne mu kai rahoto wajen Major General Dawud. Shi ne kadai zai iya magance wannan matsala cikin gaggawa."
Gwaggo Zainabu ta jinjina kai.
"Hakan daidai ne," ta ce. "Amma kada mu manta cewa idan suka fahimci cewa an gano su, to ba abin da ba za su iya aikatawa ba domin su kare kansu."
Haruna ya gyada kai.
"Tabbas, su Karama da kishiyoyinta ba za su yi kasa a gwiwa ba idan suka ji cewa an bankado SIRRIN su," ya ce. "Wannan shine dalilin da ya sa dole a yi komai a hankali, ba tare da sun fahimta ba."
Alhaji Uzairu ya gyara zamansa, ya dubi Alhaji Amiru da Gwaggo Zainabu.
"To yanzu, ya za ayi?" ya tambaya cikin damuwa.
Alhaji Amiru ya yi shiru na dan lokaci, kafin ya kalli Haruna.
"Ka shirya ka sake tafiya wajen boka?" ya tambaya.
Haruna ya yi ajiyar zuciya, ya kalli su duka.
"Idan hakan zai tabbatar da cewa muna da cikakken shaida, zan sake komawa," ya ce cikin karfin hali. "Sai dai, dole a yi HANKALI kada su fahimci cewa ana bincikensu."
Gwaggo Zainabu ta dubi Alhaji Uzairu.
"Uzairu, kana da tabbacin cewa za ka iya hada kai da mu wajen ganin an yi adalci?"
Alhaji Uzairu ya dago idanuwansa, yana kallon kowa daya bayan daya. A zuciyarsa, yana jin radadin cewa iyalinsa sun fi kowa cutar da shi. Bai taba tunanin cewa akwai wata rana da za a gaya masa irin wannan abu ba.
Ya numfasa, sannan ya gyada kai.
"Na amince," ya ce a hankali. "Ba zan bari su kashe min iyali ba."
Alhaji Amiru ya sauke ajiyar zuciya mai nauyi.
"To, lokaci bai yi ba da za mu tafi wajen Major General Dawud ba?"
Gwaggo Zainabu ta gyada kai.
"Yanzu ne lokaci. Ba za mu jira har sai wani abu ya faru ba."
Alhaji Amiru ya mike tsaye.
A nan suka yanke shawarar tafiya wajen Major General Dawud, don a dauki matakin kare Zaytunah daga mummunar makarkashiya da kishiyoyinta suka kitsa...
Suna fitowa daga falon, kowanne daga cikinsu zuciyarsa cike da tunani. Alhaji Uzairu yana bin su da baya, har yanzu kansa a kulle yake da abubuwan da suka faru. Bai taba tunanin cewa wata rana zai fuskanci wannan matsala daga matansa ba.
Haruna ne ya dauki nauyin tukin motar, yayin da Alhaji Amiru da Alhaji Uzairu suka zauna a bayan mota, kowanne cikin nitsuwa. A lokacin da motar ta bar harabar sashen Gwaggo Zainabu, shiru ya ratsa cikin su.
Alhaji Uzairu ya lumshe idanu, yana jin yadda zuciyarsa ke bugawa da karfi. Abin da ke faruwa ya girgiza shi matuka.
“Uzairu, ka tabbatar cewa kana da ƙarfin zuciyar fuskantar abin da zai biyo baya?” Alhaji Amiru ya tambaya, yana dubansa.
Alhaji Uzairu ya bude idanu, ya dubi dan uwansa. “Dole na yi hakan, Yaya Amiru,” ya ce da karfin hali. “Ba zan iya bari su hallaka min ‘ya’ya ba.”
Haruna ya cigaba da tuƙi cikin nutsuwa, yana bin titin da zai kaisu gidan Major General Dawud.
MAJOR GENERAL DAWUD MAFIA RES:
A lokacin da suka isa, an shigo da su kai tsaye zuwa falon ba tare da wata matsala ba. Major General Dawud yana sanye da kayan gida, yana zaune bisa kujerar da ke gefen babban falonsa. Da gani, yana cikin shirin hutawa ne kafin su shigo.
Ya kalli su daya bayan daya, kafin ya maida kallonsa ga Alhaji Amiru.
“Kun zo da gaggawa, Amiru,” ya fada a hankali. “Ina sauraronku.”
Alhaji Amiru ya sauke ajiyar zuciya, sannan ya fara bayanin komai dalla-dalla. Ya fada masa yadda Haruna ya bi matan Alhaji Uzairu har wajen boka, yadda ya ji su da kunnuwansa suna tsara kashe Zaytunah, da yadda Alhaji Uzairu ya kasa yarda da hakan har sai an kawo hujja mai karfi.
A lokacin da Alhaji Amiru ya kai karshe, fuskar Major General Dawud ta nuna tsananin ɓacin rai.
“Kun tabbatar da cewa wannan maganar gaskiya ce?” ya tambaya, yana duban Haruna da tsananin ido.
Haruna ya gyada kai. “Wallahi, babu shakka akan haka, ranka ya dade,” ya ce da tabbaci.
Major General Dawud ya jingina da kujera, yana tunani na wani lokaci.
“Idan haka ne, lamarin yana bukatar gaggawa,” ya ce a hankali. “Ba zan bari komai ya same su Zaytunah ba. Fata dai a same sun..”
Ya dubi Alhaji Uzairu da kyau. “Uzairu,” ya kira sunansa da kakkausar murya. “Kana da tabbacin cewa ba za ka yi wata-wata wajen daukar mataki akan wannan lamari ba?”
Alhaji Uzairu ya lumshe ido, yana jin nauyin kalmomin Major General Dawud. Da farko, yana jin kamar abin kamar mafarki ne, amma yanzu ya san babu gudu ba ja da baya.
“Na tabbatar,” ya amsa cikin muryar da ke nuna yanke shawara.
Major General Dawud ya mike tsaye. “To, ku jira ni,” ya fada.
Ya yi gaba zuwa wani daki, sannan ya fito cikin uniform dinsa, yana daure da damara. Fuskar sa a daure take, alamun ya gama yanke shawara akan abin da zai yi.
“Za a tsaurara tsaro Inn shaa' Allah"
Ya kalli su duka, sannan ya dauki wayarsa. “Kuma ba zan tsaya nan ba. Sai mun tabbatar da cewa an hukunta duk wanda ke da hannu a wannan makirci.”
Alhaji Uzairu ya runtse ido, zuciyarsa cike da nauyi. Ya san cewa daga wannan rana, rayuwar sa ba za ta kara zama kamar yadda take a da ba...
_1-KALBIM:MAMUH GEE_
_2-KIRJIN MAI HANKALI (AKWATIN SIRRIN SA):MSS XOXO_
_3-ADUNIYATAH :HUGUMAH_
_4-AJIYA A DUHU: BILYN ABDULL_
°°
_1-BOOK DAYA:DARI BIYAR_
_2-BOOKS BIYU:DUBU DAYA_
_3-BOOKS UKU: DUBU DAYA DA DARI BIYAR_
_4-BOOKS HUDU :DUBU BIYU_
_5_YAN NIJAR: 1000CF: 89825722 NOUSAIBA LAWALI MARADI_
_ku tura receipt zuwa ga 09033181070_
*IDAN KATI NE A TURO TA WANNAN NUMBER:*
*09032345899.. SHEDAR KATIN MA NAN ZAA TURA. KATIN MTN!!MTN!!*
____
*KIRJIN MAI HANKALI*
_(Akwatin sirrin sa)_
_🧳👩❤️👨🌺_
*_The Vault Of His Secrets_*
_®️NANA HAFSATU (MX)_
_©️ZAFAFA BIYAR WRITERS_
*_BOOK TWO_*
_PAGE:26_
Da Alhaji Uzairu ya iso gida, bai wuce kai tsaye zuwa dakinsa ba. Maimakon haka, ya tsaya a babban falon gida inda matansa, Hajiya da Hajiya Karama, suke zaune suna tattauna wasu batutuwa a tsakaninsu. A ganinsa, kamar dai suna magana ne da nutsuwa, amma da zarar suka hango shi, sai suka yi shiru tamkar wadanda aka kama da laifi.
Ya zuba musu ido na dan lokaci ba tare da ya ce komai ba. Sai da ya zauna a kujera ya dora kafa daya kan daya, sannan ya gyara zama, yana jin nauyin da ke cikin zuciyarsa.
"Hajiya," ya kira sunan matar sa ta farko, "yau na wuni a gidan Ya Amiru."
Hajiya ta kalle shi cikin kulawa. "Lafiya dai? Ka dawo da wuri yau."
"Eh, ai ba wani abu," ya fada, yana juyawa zuwa ga Hajiya Karama.
"Mun yi doguwar hira da Alhaji Amiru da Gwaggo Zainabu. Sun yi tambayoyi da yawa game da rayuwar mu."
A take, Hajiya Karama ta hadiye yawu. "Tambayoyi irin na menene kuma?"
Alhaji Uzairu ya girgiza kai. "Kawai dai wasu tsofaffin batutuwa ne… da kuma wasu abubuwan da suka shafi rayuwar mu a baya."
Hajiya ta dube shi da dan tsoro. "Rayuwa ta baya fa?"
Sai ya gyada kai a hankali, yana kallonsu dukkansu. "Kusan shekara goma kenan da wasu abubuwa suka faru… kuma sai yanzu suke tambayata su kansu. Abin mamaki, ko ba haka ba?"
Hajiya Karama ta shiga girgiza kai. "To, me ya sa sai yanzu suka tuna? Ai da ace wani abu ne mai muhimmanci, da tuni sun yi magana da kai a baya."
Alhaji Uzairu ya dan saki murmushi mara dadi. "Hakan nake tunani. Amma kin san wani abu? Na fara jin kamar akwai wani abu da ba a gaya min ba. Kuma hakan yana bani mamaki sosai."
Hajiya karama ta dan yi dariya. "Me kake nufi da wani abu da ba a gaya maka ba? Me ya sa kake tunanin haka?"
Sai ya jingina da kujera, yana dubansu dukkansu da idon bincike...
"Hakane," ya ce yana kallonsu da ido mai zurfi, "amma abin da ya faru bai shuɗe haka kawai ba. Ko dai wani ne ya sa hannu, ko kuma akwai wani SIRRI da ake boyewa."
Hajiya da Hajiya Karama suka kalli juna a lokaci guda, tamkar suna kokarin jin wace za ta fara magana. Sai dai dukkansu sun kasa cewa komai nan take.
Alhaji Uzairu ya gyara zama, yana nazarinsu. "Kun san abinda ya fi bani mamaki?"
Hajiya Karama ta yi saurin girgiza kai. "A’a."
Ya sake dubansu duka, sannan ya furta a hankali: "Yadda duk sanda aka ambaci sunan Zaytunah, sai ku dinga kokarin gujewa maganar."
A take, Hajiya ta ɗan ja numfashi. "Ba haka bane, Alhaji. Ai ba wai muna gujewa bane, kawai dai... ba mu ga amfanin tada wannan batu ba."
"Ba ku ga amfaninsa ba?" Ya jinjina kansa, yana kallonsu da kyau. "Matar aure ce, Mahaifiya ga yayanta. Yara biyu. , baƙar rana daya ta ɓace, har yau ba a san inda take ba da iyalanta, ba a san ko tana raye ba ko kuma..." Ya dan dakata, yana son ganin yadda za su karɓi kalmomin nasa.
Hajiya Karama ta sake gyara zama, ta lumshe ido na ɗan lokaci, kamar tana tunanin wani abu. Da ta buɗe su, sai ta ce da ƙasa-ƙasa: "Ai Allah kadai yasan inda take, Alhaji."
Alhaji Uzairu ya haɗiye yawu. Yanzu ya fara jin wata irin hujja a cikin muryarta. "Kun tabbata?" Ya tambaya, yana jefa musu wani irin kallo da ya sa dukansu suka rasa yadda za su mayar masa da martani.
Hajiya ta ɗauke kanta gefe, yayin da Hajiya Karama ta sunkuyar da kai. Wannan ne karon farko da ya tabbatar da cewa akwai wani abu da suke ɓoyewa. SIRRI ne da suka daɗe suna rufewa, amma yanzu lokaci ya kusa da za a tona komai.