Sashe 34
Kirjin Mai Hankali Part 2 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Sai dai, shin yana yiwuwa?
Wakar dake fitowa daga motar ta sake mamaye zuciyarsu:
"Take my hand… take my whole life too… for I can’t help falling in love with you."
Fawaaz ya lumshe ido a hankali.
Nabeeha, me kike so na yi?
Ina jin ki. Ina jin ki fiye da yadda na zata. Amma ba zan iya furtawa ba.
Ya gyara zaman hularsa ta soja (Beret/Military cap), yana jin yadda soyayyar ke kara cika zuciyarsa da nauyi.
Nabeeha ta dago da sauri, tana kallon sa.
Shigarsa ta kara burgeta fiye da yadda take zato.
Ba ta san lokacin da murmushi ya subuce mata ba.
Fawaaz kuwa, ya lura da murmushin, amma sai ya dauke kai.
Idan ya ci gaba da kallo, zai iya furta abin da zuciyarsa take fada.
Sai dai a zuciyarsa, yana jin kamar yana makara.
Yana makara kafin soyayyarsa ta fishe shi, har ta gagara ɓoyuwa.
Fawaaz ya kafe idanunsa a kan titin da ke gabansa, hannayensa na riƙe da sitiyari da cikakken iko. Motar na tafiya cikin nutsuwa, iska na tashi daga A.C, tana ratsa su da sanyin da bai iya kashe wutar zuciyarsu ba..
Yana sanye da kayan sojoji—khaki mai kyau da tsari, da hular soja (beret) da ya gyara a gefen kansa. Dogon hannun rigarsa ya bayyana ƙwarewa da ƙa’ida irin ta sojoji, lambar sunansa ta manne a gefen ƙirjinsa.
Nabeeha ta ji zuciyarta ta buga da sauri da ta sake kallonsa. Yana da kyau sosai a haka…
Amma hakan bai dame shi ba.
Yana tukinsa cikin shiru, fuska a daure kamar yadda ya saba. Sai dai ta lura da yadda jaw-line dinsa ke motsi—alamar yana taƙure wani abu da bai so ya bayyana ba.
Shiru ya fi magana sau dubu.
Sai dai ita kanta tana cikin tunani. Ba ta san me yasa zuciyarta ke dukan wata irin guda ba.
Ba ta son ya fahimta.
Sai dai, shin yana yiwuwa ya riga ya fahimta?
Wakar da ke tashi a hankali daga motar (Slow Love Song) ta cika zuciyarta da wani irin nutsuwa mai sanyi, amma da sauƙin da ke ɗauke da nauyi..
"I don’t wanna say goodbye…
Even when the night is over…
I just wanna hold you close…
Even if we’re lost forever…"
Ta dan lumshe idanu a hankali.
Tana jin shaukinsa na ratsa ta.
Hankalinsa na kan titi, amma zuciyarsa na wani wuri daban. Wurin da aka kulle shi da soyayyar da ba zai iya furta wa ba.
Fawaaz ya gyara zamansa a kujerar direba, yana matsa yatsunsa a kan sitiyari. Numfashinsa na fita a hankali, amma zuciyarsa na tafasa.
A gefensa, Nabeeha ta sake gyara zaman mayafinta, tana ƙoƙarin kwantar da zuciyarta. Sai dai hakan ya gagara.
Kafin ta fito daga gida, ta yanke shawarar cewa ba za ta sake kallonsa da wani irin kallo ba. Ba za ta bari zuciyarta ta bayyana abin da take ji ba.
Amma yanzu…
Yana da kyau…
Yadda kayan sojoji suka zauna masa daidai, sun bayyana cikakken ƙuruciya da ƙwarewarsa. Beret ɗinsa na gefen kansa, yana ƙara masa kwarjini. Idanunsa kuwa, ko da bai kalleta kai tsaye ba, akwai wani irin zurfi da take ji idan ta kalle su.
Zuciyarta ta ja da baya da sauri.
Wani sanyi ne ya ratsa ta lokacin da ta sake jin wakar da ke tashi a hankali daga speakers ɗin motar.
"I will always, always love you…"
Wata irin zufa ta keto mata a goshinta.
Ta san cewa ba kawai kalmomin waka ba ne ke ratsa ta.
Soyayyar da take jin yana ɓoye wa ne ke ratsata.
Fawaaz ya juyo da dan kallo, a hankali. Bai yi magana ba, amma idanunsa sun fada mata duk abin da bakinsa ya gaza furtawa.
Ta yi saurin dauke kai.
Zuciyarta na tsalle tamkar za ta fito waje.
Me yasa ba zai yi magana ba?
Me yasa ba zai furta abin da yake ji ba?
Ya jima da sanin cewa soyayyarta ta mamaye shi.
Ya jima da sanin cewa yana cikin matsala idan bai gaggauta daukar mataki ba.
Sai dai… yana jin tsoron furta hakan.
Hannunsa na dama ya dan dunkule sama da sitiyari, yana jin wani irin nauyi a KIRJI.
Fawaaz, kai soja ne.
Kai namiji ne.
Amma kuma me yasa soyayyarta ke galaba da kai?
Sai ya sake kallonta da gefen ido.
Sai dai ta kau da kanta, kamar yadda shima yake ƙoƙarin kau da zuciyarsa daga shaukinta.
Zuciyarta ta furta abu guda.
Duk da shiru ya yi yawa, zuciyoyinsu sun san gaskiya.
A haka ya karasar da ita zuwa inda zasuyi aikin... Ya jirata har suka kammala sannan ya dakkota suka koma hanyar gidah..
Motar ta tsaya a harabar gidan a hankali, amma babu wanda ya yi yunƙurin fita daga ciki.
Shiru ya ratsa tsakanin su, sai dai sautin numfashinsu da aka kasa ɓoyewa.🤭
Fawaaz ya kafe idanunsa a kan gaban motar, amma zuciyarsa na wani wuri. A zuciyarsa, yana jin tamkar bai so su koma gida ba. In da za a ce lokacin zai tsaya cak, ya kasance tare da ita har abada, babu shakka da ya yi hakan.
Sai dai rayuwa ba haka take ba.
Ya juyo a hankali, idanunsa suka sauka a kanta.
Nabeeha tana zaune da mayafinta da ya zame a gefe, yana bayyana fuskar da ya daɗe yana gujewa kallon kai tsaye. Amma yau…
Yau zuciyarsa ba ta iya daurewa ba.
“Nabeeha.”
Muryarsa ta fito a kasalance, amma cike da nauyin da bai saba da shi ba.
Ta dago idanunta a hankali, idanunta masu launin hazel sun ratsa nasa. Duk wani ƙoƙarin da take yi na guje wa kallonsa ya gagara, saboda yadda idanunsa suka kulle nata gaba ɗaya.
Fawaaz ya dan matsa, yana jin wani abu na fisgarsa da ƙarfi.
Bai san lokacin da hannunsa ya kai ya riƙo nata ba. Hannunta ƙanƙani ne cikin nasa, amma dumin da ya ji ya fi duka sojojinsa cusa masa jini a cikin gangar jikinsa.
Nabeeha ta runtse ido. Ta san cewa idan har ta sake kallonsa, tabbas za ta nutse a cikin abin da take ƙoƙarin guje wa.
Sai dai hakan bai hana ta jin yadda zuciyarta ke bugu da sauri ba.
A hankali, Fawaaz ya ɗago da ɗayan hannunsa, ya sanya yatsansa a gefen fuskarta. Bai sani ba, amma yana jin tamkar zuciyarsa ta ɓarke da wani irin shauƙi da bai taɓa fuskanta a rayuwa ba.
Ta buɗe idanunta a hankali.
Idanunsu sun haɗu, zuciyoyinsu suka yi shiru, amma jikin nasu na furta dukkan abin da suke ji.
Fawaaz ya saki ajiyar zuciya mai nauyi.
Ina ma ita ce tasa.
Ina ma yana da ita tamkar yadda yake buƙatar ta.
A hankali ya matsa, yana jin yadda numfashinta ke gauraya da nasa. Yana jin yadda idanunta ke kiran nasa, ba tare da wata kalma ba.
Labbanta sun jike da ɗan sauƙin numfashi. Suka kasance jajaye kamar furannin wardi, suna kiran nasa da wani irin nutsuwa da tsoron zuciya.
Tamkar Ya kai karamin sumba a hankali.
Sai da ya ji yadda duk wani zafin da zuciyarsa ke ji ya narke a take.
Nabeeha ta lumshe ido. Bai da ƙarfin ja da baya. Bai da ƙarfin barin abin da zuciyarsa ta riga ta aminta da shi.
Fawaaz yaji tamkar ya jingina goshinsa da nata, yana mai jin tamkar wannan ne farkon tafiyar da bai san inda za ta tsaya ba.
Yana jin zuciyarsa na bugawa, amma ba da tsoron soja ba—da tsoron so.
Soyayyar da ba zai iya furtawa ba.
Fawaaz ya kashe motar, amma bai yi yunƙurin buɗe ƙofa ba. Hannayensa suna kan sitiyari, amma zuciyarsa tana wani wuri.
Zuciyarsa tana tare da ita.
Nabeeha tana gefensa, zaune kamar yadda ta kasance tun farkon tafiyar. Sai dai yanzu, shiru ya mamaye tsakanin su.
Wani irin sanyi ya ratsashi. Bai san dalili ba, amma zuciyarsa na faɗin abu ɗaya,
"Ina ma halaliyata ce, inama tawa ce mallaki na ce.."
"Ina ma zan iya riƙe ta cikin kaina, ba tare da wata shakka ba.inama ace matata ce"
Ya dan juyo, idanunsa suka sauka a kanta.
Ta daɗe da sunkuyar da kai, tana wasa da yatsunta cikin nutsuwa.
Fawaaz ya kafe ta da ido, yana jin wani nauyi a zuciyarsa. Wani ƙarfi ne ya lulluɓe shi, yana ƙoƙarin fisgarsa.
Ya ma rasa dalilin da ya sa hakan ke faruwa.
Hannunsa ya dan motsa, yana so ya kai ga nata. Amma ya dakata.
Ba ta tashi ba.
Ba ta yi magana ba.
Haka shima bai ce komai ba.
Bai san yaushe ya juyo da fuskar sa sosai ba, yana kallon yadda hasken fitilar gidan ke sauka saman fuskarta.
Ta haɗiye yawu a hankali, tana jin idonsa akan ta kamar wuta.
Fawaaz ya sake numfasa, yana jin yadda zuciyarsa ke faɗin abu ɗaya,
"Ina ma zan iya rungumarta a kaina."
"Ina ma zata iya jin yadda zuciyata ke bugawa saboda ita."
Sai dai…
Ba halaliyar sa bace.
Ba mallakinsa ba ce.
Zuciyarsa ta amince da hakan, amma gangar jikinsa ta ƙi.
Ya lumshe ido, yana mai jin yadda wannan tunanin ke ƙara masa raɗaɗi.
Ya ɗauki lokaci kafin ya matsa baya kadan, ya jingina da kujera, yana mai kakkabe duk wani tunani da ke ransa.
Soja ne shi.
Dole ne ya riƙe kansa.
A hankali ya ce,
“Mun iso.”
Muryarsa ta fita da sanyi, ba tare da ƙarfin da ya saba da shi ba.
Nabeeha ta daga kai a hankali, suka yi ido biyu. Sai dai kafin ta samu damar cewa komai, ya riga ya buɗe ƙofar motar ya fita.
Ya riga ya rufe komai cikin zuciyarsa....
Dan wahala 😂🤭🧑🦯
MX🧕
*KIRJIN MAI HANKALI*
_(Akwatin sirrin sa)_
_🧳👩❤️👨🌺_
*_The Vault Of His Secrets_*
_®️NANA HAFSATU (MX)_
_©️ZAFAFA BIYAR WRITERS_
*_BOOK TWO_*
_PAGE:31_
A cikin babban falon gidan Major General Dawud, kowa ya hallara. Gwaggo Hafsatu na zaune a tsakiyar kujerar da take da alfarma, tana daura tafukan hannunta a saman cinyoyinta. Fuskar ta na bayyana alamar tunani mai zurfi, tamkar tana jin nauyin wani babban yanke hukunci.
Major general dawud mafia na daga gefen ta yana kallon kasa da shiru. Duk da cewa shi mutum ne da ke da karfi da iko, yau ya kasa daukar mataki ba tare da jin ra’ayin Gwaggo Hafsatu ba. Yana jin nauyin amanar da ta rataya a wuyansa—amanar Zaytunah da ‘ya’yanta.
Wakar dake fitowa daga motar ta sake mamaye zuciyarsu:
"Take my hand… take my whole life too… for I can’t help falling in love with you."
Fawaaz ya lumshe ido a hankali.
Nabeeha, me kike so na yi?
Ina jin ki. Ina jin ki fiye da yadda na zata. Amma ba zan iya furtawa ba.
Ya gyara zaman hularsa ta soja (Beret/Military cap), yana jin yadda soyayyar ke kara cika zuciyarsa da nauyi.
Nabeeha ta dago da sauri, tana kallon sa.
Shigarsa ta kara burgeta fiye da yadda take zato.
Ba ta san lokacin da murmushi ya subuce mata ba.
Fawaaz kuwa, ya lura da murmushin, amma sai ya dauke kai.
Idan ya ci gaba da kallo, zai iya furta abin da zuciyarsa take fada.
Sai dai a zuciyarsa, yana jin kamar yana makara.
Yana makara kafin soyayyarsa ta fishe shi, har ta gagara ɓoyuwa.
Fawaaz ya kafe idanunsa a kan titin da ke gabansa, hannayensa na riƙe da sitiyari da cikakken iko. Motar na tafiya cikin nutsuwa, iska na tashi daga A.C, tana ratsa su da sanyin da bai iya kashe wutar zuciyarsu ba..
Yana sanye da kayan sojoji—khaki mai kyau da tsari, da hular soja (beret) da ya gyara a gefen kansa. Dogon hannun rigarsa ya bayyana ƙwarewa da ƙa’ida irin ta sojoji, lambar sunansa ta manne a gefen ƙirjinsa.
Nabeeha ta ji zuciyarta ta buga da sauri da ta sake kallonsa. Yana da kyau sosai a haka…
Amma hakan bai dame shi ba.
Yana tukinsa cikin shiru, fuska a daure kamar yadda ya saba. Sai dai ta lura da yadda jaw-line dinsa ke motsi—alamar yana taƙure wani abu da bai so ya bayyana ba.
Shiru ya fi magana sau dubu.
Sai dai ita kanta tana cikin tunani. Ba ta san me yasa zuciyarta ke dukan wata irin guda ba.
Ba ta son ya fahimta.
Sai dai, shin yana yiwuwa ya riga ya fahimta?
Wakar da ke tashi a hankali daga motar (Slow Love Song) ta cika zuciyarta da wani irin nutsuwa mai sanyi, amma da sauƙin da ke ɗauke da nauyi..
"I don’t wanna say goodbye…
Even when the night is over…
I just wanna hold you close…
Even if we’re lost forever…"
Ta dan lumshe idanu a hankali.
Tana jin shaukinsa na ratsa ta.
Hankalinsa na kan titi, amma zuciyarsa na wani wuri daban. Wurin da aka kulle shi da soyayyar da ba zai iya furta wa ba.
Fawaaz ya gyara zamansa a kujerar direba, yana matsa yatsunsa a kan sitiyari. Numfashinsa na fita a hankali, amma zuciyarsa na tafasa.
A gefensa, Nabeeha ta sake gyara zaman mayafinta, tana ƙoƙarin kwantar da zuciyarta. Sai dai hakan ya gagara.
Kafin ta fito daga gida, ta yanke shawarar cewa ba za ta sake kallonsa da wani irin kallo ba. Ba za ta bari zuciyarta ta bayyana abin da take ji ba.
Amma yanzu…
Yana da kyau…
Yadda kayan sojoji suka zauna masa daidai, sun bayyana cikakken ƙuruciya da ƙwarewarsa. Beret ɗinsa na gefen kansa, yana ƙara masa kwarjini. Idanunsa kuwa, ko da bai kalleta kai tsaye ba, akwai wani irin zurfi da take ji idan ta kalle su.
Zuciyarta ta ja da baya da sauri.
Wani sanyi ne ya ratsa ta lokacin da ta sake jin wakar da ke tashi a hankali daga speakers ɗin motar.
"I will always, always love you…"
Wata irin zufa ta keto mata a goshinta.
Ta san cewa ba kawai kalmomin waka ba ne ke ratsa ta.
Soyayyar da take jin yana ɓoye wa ne ke ratsata.
Fawaaz ya juyo da dan kallo, a hankali. Bai yi magana ba, amma idanunsa sun fada mata duk abin da bakinsa ya gaza furtawa.
Ta yi saurin dauke kai.
Zuciyarta na tsalle tamkar za ta fito waje.
Me yasa ba zai yi magana ba?
Me yasa ba zai furta abin da yake ji ba?
Ya jima da sanin cewa soyayyarta ta mamaye shi.
Ya jima da sanin cewa yana cikin matsala idan bai gaggauta daukar mataki ba.
Sai dai… yana jin tsoron furta hakan.
Hannunsa na dama ya dan dunkule sama da sitiyari, yana jin wani irin nauyi a KIRJI.
Fawaaz, kai soja ne.
Kai namiji ne.
Amma kuma me yasa soyayyarta ke galaba da kai?
Sai ya sake kallonta da gefen ido.
Sai dai ta kau da kanta, kamar yadda shima yake ƙoƙarin kau da zuciyarsa daga shaukinta.
Zuciyarta ta furta abu guda.
Duk da shiru ya yi yawa, zuciyoyinsu sun san gaskiya.
A haka ya karasar da ita zuwa inda zasuyi aikin... Ya jirata har suka kammala sannan ya dakkota suka koma hanyar gidah..
Motar ta tsaya a harabar gidan a hankali, amma babu wanda ya yi yunƙurin fita daga ciki.
Shiru ya ratsa tsakanin su, sai dai sautin numfashinsu da aka kasa ɓoyewa.🤭
Fawaaz ya kafe idanunsa a kan gaban motar, amma zuciyarsa na wani wuri. A zuciyarsa, yana jin tamkar bai so su koma gida ba. In da za a ce lokacin zai tsaya cak, ya kasance tare da ita har abada, babu shakka da ya yi hakan.
Sai dai rayuwa ba haka take ba.
Ya juyo a hankali, idanunsa suka sauka a kanta.
Nabeeha tana zaune da mayafinta da ya zame a gefe, yana bayyana fuskar da ya daɗe yana gujewa kallon kai tsaye. Amma yau…
Yau zuciyarsa ba ta iya daurewa ba.
“Nabeeha.”
Muryarsa ta fito a kasalance, amma cike da nauyin da bai saba da shi ba.
Ta dago idanunta a hankali, idanunta masu launin hazel sun ratsa nasa. Duk wani ƙoƙarin da take yi na guje wa kallonsa ya gagara, saboda yadda idanunsa suka kulle nata gaba ɗaya.
Fawaaz ya dan matsa, yana jin wani abu na fisgarsa da ƙarfi.
Bai san lokacin da hannunsa ya kai ya riƙo nata ba. Hannunta ƙanƙani ne cikin nasa, amma dumin da ya ji ya fi duka sojojinsa cusa masa jini a cikin gangar jikinsa.
Nabeeha ta runtse ido. Ta san cewa idan har ta sake kallonsa, tabbas za ta nutse a cikin abin da take ƙoƙarin guje wa.
Sai dai hakan bai hana ta jin yadda zuciyarta ke bugu da sauri ba.
A hankali, Fawaaz ya ɗago da ɗayan hannunsa, ya sanya yatsansa a gefen fuskarta. Bai sani ba, amma yana jin tamkar zuciyarsa ta ɓarke da wani irin shauƙi da bai taɓa fuskanta a rayuwa ba.
Ta buɗe idanunta a hankali.
Idanunsu sun haɗu, zuciyoyinsu suka yi shiru, amma jikin nasu na furta dukkan abin da suke ji.
Fawaaz ya saki ajiyar zuciya mai nauyi.
Ina ma ita ce tasa.
Ina ma yana da ita tamkar yadda yake buƙatar ta.
A hankali ya matsa, yana jin yadda numfashinta ke gauraya da nasa. Yana jin yadda idanunta ke kiran nasa, ba tare da wata kalma ba.
Labbanta sun jike da ɗan sauƙin numfashi. Suka kasance jajaye kamar furannin wardi, suna kiran nasa da wani irin nutsuwa da tsoron zuciya.
Tamkar Ya kai karamin sumba a hankali.
Sai da ya ji yadda duk wani zafin da zuciyarsa ke ji ya narke a take.
Nabeeha ta lumshe ido. Bai da ƙarfin ja da baya. Bai da ƙarfin barin abin da zuciyarsa ta riga ta aminta da shi.
Fawaaz yaji tamkar ya jingina goshinsa da nata, yana mai jin tamkar wannan ne farkon tafiyar da bai san inda za ta tsaya ba.
Yana jin zuciyarsa na bugawa, amma ba da tsoron soja ba—da tsoron so.
Soyayyar da ba zai iya furtawa ba.
Fawaaz ya kashe motar, amma bai yi yunƙurin buɗe ƙofa ba. Hannayensa suna kan sitiyari, amma zuciyarsa tana wani wuri.
Zuciyarsa tana tare da ita.
Nabeeha tana gefensa, zaune kamar yadda ta kasance tun farkon tafiyar. Sai dai yanzu, shiru ya mamaye tsakanin su.
Wani irin sanyi ya ratsashi. Bai san dalili ba, amma zuciyarsa na faɗin abu ɗaya,
"Ina ma halaliyata ce, inama tawa ce mallaki na ce.."
"Ina ma zan iya riƙe ta cikin kaina, ba tare da wata shakka ba.inama ace matata ce"
Ya dan juyo, idanunsa suka sauka a kanta.
Ta daɗe da sunkuyar da kai, tana wasa da yatsunta cikin nutsuwa.
Fawaaz ya kafe ta da ido, yana jin wani nauyi a zuciyarsa. Wani ƙarfi ne ya lulluɓe shi, yana ƙoƙarin fisgarsa.
Ya ma rasa dalilin da ya sa hakan ke faruwa.
Hannunsa ya dan motsa, yana so ya kai ga nata. Amma ya dakata.
Ba ta tashi ba.
Ba ta yi magana ba.
Haka shima bai ce komai ba.
Bai san yaushe ya juyo da fuskar sa sosai ba, yana kallon yadda hasken fitilar gidan ke sauka saman fuskarta.
Ta haɗiye yawu a hankali, tana jin idonsa akan ta kamar wuta.
Fawaaz ya sake numfasa, yana jin yadda zuciyarsa ke faɗin abu ɗaya,
"Ina ma zan iya rungumarta a kaina."
"Ina ma zata iya jin yadda zuciyata ke bugawa saboda ita."
Sai dai…
Ba halaliyar sa bace.
Ba mallakinsa ba ce.
Zuciyarsa ta amince da hakan, amma gangar jikinsa ta ƙi.
Ya lumshe ido, yana mai jin yadda wannan tunanin ke ƙara masa raɗaɗi.
Ya ɗauki lokaci kafin ya matsa baya kadan, ya jingina da kujera, yana mai kakkabe duk wani tunani da ke ransa.
Soja ne shi.
Dole ne ya riƙe kansa.
A hankali ya ce,
“Mun iso.”
Muryarsa ta fita da sanyi, ba tare da ƙarfin da ya saba da shi ba.
Nabeeha ta daga kai a hankali, suka yi ido biyu. Sai dai kafin ta samu damar cewa komai, ya riga ya buɗe ƙofar motar ya fita.
Ya riga ya rufe komai cikin zuciyarsa....
Dan wahala 😂🤭🧑🦯
MX🧕
*KIRJIN MAI HANKALI*
_(Akwatin sirrin sa)_
_🧳👩❤️👨🌺_
*_The Vault Of His Secrets_*
_®️NANA HAFSATU (MX)_
_©️ZAFAFA BIYAR WRITERS_
*_BOOK TWO_*
_PAGE:31_
A cikin babban falon gidan Major General Dawud, kowa ya hallara. Gwaggo Hafsatu na zaune a tsakiyar kujerar da take da alfarma, tana daura tafukan hannunta a saman cinyoyinta. Fuskar ta na bayyana alamar tunani mai zurfi, tamkar tana jin nauyin wani babban yanke hukunci.
Major general dawud mafia na daga gefen ta yana kallon kasa da shiru. Duk da cewa shi mutum ne da ke da karfi da iko, yau ya kasa daukar mataki ba tare da jin ra’ayin Gwaggo Hafsatu ba. Yana jin nauyin amanar da ta rataya a wuyansa—amanar Zaytunah da ‘ya’yanta.