Sashe 28
Kirjin Mai Hankali Part 2 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Ya ɗan gyara zaman rigarsa, ya kalli agogo. Wajibi ne ya kammala wannan lamari cikin nutsuwa, batare da wani yayi tunanin akwai wani abu daban ba.
A hankali ya kira Nabeeha, murya a daidai misali.
"Ina son ganinki a waje," kawai ya ce mata, ba tare da wata sharhi ba.
**A lokacin da ta fito, ya jingina da motarsa, hannayensa a cikin aljihu, idanunsa na kallon gefe tamkar ba shi ya kira ta ba. Nabeeha ta dan yi jinkiri tana nazarinsa, sannan ta karasa kusa da shi. Tana gayshe da shi..
"Ga wannan."
Bai iya kallonta ba yayin da ya miƙa mata wayar. Murya a dakile, kamar yana bayar da wani abu mara muhimmanci.😂
Nabeeha ta kalli wayar da mamaki. Idanunta sun cika da alamar tambaya.
"Wannan fa?"
Fawaaz bai amsa ba. Ya ɗan juya gefen fuskarsa, yana kallon wata hanya kamar wanda ba ruwansa da abin da ke faruwa.
"Ta waye.. ko tawa ce?" Ta tambaya a hankali, tana jin kamar mafarki take yi.
Ya numfasa kadan, yana cigaba da kallon gefe. "Ee."
Shiru ya biyo baya na ƴan dakiku. Sai da zuciyarta ta harba da wani yanayi mai rikitarwa.
"Nagode Allah ya Saka maka da alkhairi amin," ta ce cikin sanyin murya.
Bai amsa ba. Bai ce komai ba. Kawai ya jinjina kai kaɗan, sannan ya juya ya buɗe motarsa ya shiga fice daga gidan.
Yana barin wajen, zuciyarsa na bugawa da karfi. Bai ce mata komai ba. Bai iya furtawa ba. Amma ya san, daga yanzu, zai iya jin ta kusa da shi... ko da kuwa ta hanyar sakonni ne kawai.
Nabeeha ta tsaya a wajen, hannunta rike da wayar da ya bata. Kamar mafarki ne, kamar ba gaske ba. Idanunta sun cika da tambayoyi, amma wanda ya dace ya amsa su, tuni ya tafi.
Ta lumshe idanu, zuciyarta na harbawa. Ba wai sayen wayar bane matsalar amma yadda ya bayar. Yadda bai ce komai ba, yadda ko murmushi bai yi ba, yadda ya maze kamar ba wani abu mai muhimmanci ya aikata ba.
Wayar ta rike a tafin hannunta, tana jin nauyinta fiye da yadda ta kamata. A hankali ta shaka iska, sannan ta juya zuwa cikin gida, zuciyarta na ji kamar tana tafiya da wani SIRRI.
***
Fawaaz yana tuƙi, amma hankalinsa ba a kan titi yake ba. Bai masan dalilin futar sa daga gida ba, Ba don yana da horo ba, da tuni ya samu matsala. Yana ta kici-kicin tunanin abinda ya aikata.
Me yasa bai iya cewa komai ba?
Me yasa ba zai iya cewa "na siya miki ne domin dubun kaunar ki danake da tsananin kwadaituwa da son jin muryar ki.." ba?
Bai gama amsa wa kansa wadannan tambayoyin ba, sai wayarsa ta fara ƙara. Ya duba—Dr. Nabeeha Uzairu Muhammad.
Zuciyarsa ta harba. Sai dai ko da haka, ya tsare fuska kamar ba komai.
A hankali ya ɗaga, yana kokarin tabbatar da cewa muryarsa ba zata nuna wani motsin rai ba.
"Hello," ya ce a dakile.
Shiru daga dayan bangaren.
"Yaa Fawaaz..." Ta ambaci sunansa a hankali, kamar mai jin nauyin magana.
"Na'am," ya amsa, har yanzu ba tare da ya nuna wata alama ba.
"Ba ka gaya min me yasa ka siya min waya ba."
Sai da ya lumshe idanu kafin ya bude su a hankali. Bai san me zai ce ba.
"Saboda ina so ki dinga samun damar magana da kowa cikin sauki," ya ce, ba tare da ya yi tunani sosai ba.
Shiru.
"Yaa Fawaaz," ta sake kiran sunansa, murya a kasalance.
Ya ji kamar tana son tace wani abu. Kawai sai ya danyi ajiyar zuciya. "Nabeeha, ki yi amfani da ita. Hakanan."
Daga nan ya katse kiran.
Ya ajiye wayarsa a gefen kujera, ya dan tsare numfashinsa na ƴan dakiku. Bai san dalili ba, amma zuciyarsa na bugawa da wani iri.
Ya riga ya aikata. Kuma ko da kuwa bai fadi ba, ya san zata fahimta... ko ba yanzu ba, wata rana.
_1-KALBIM:MAMUH GEE_
_2-KIRJIN MAI HANKALI (AKWATIN SIRRIN SA):MSS XOXO_
_3-ADUNIYATAH :HUGUMAH_
_4-AJIYA A DUHU: BILYN ABDULL_
°°
_1-BOOK DAYA:DARI BIYAR_
_2-BOOKS BIYU:DUBU DAYA_
_3-BOOKS UKU: DUBU DAYA DA DARI BIYAR_
_4-BOOKS HUDU :DUBU BIYU_
_5_YAN NIJAR: 1000CF: 89825722 NOUSAIBA LAWALI MARADI_
_ku tura receipt zuwa ga 09033181070_
*IDAN KATI NE A TURO TA WANNAN NUMBER:*
*09032345899.. SHEDAR KATIN MA NAN ZAA TURA. KATIN MTN!!MTN!!*
____
*
*KIRJIN MAI HANKALI*
_(AKWATIN SIRRIN SA)_
🧳➿💞
*PG :24*
*AREWABOOKS VVIP:👇*
https://www.arewabooks.com/book?id=670bd07e35879b101764c0eb
__
Nabeeha ta kalli wayar a hannunta, zuciyarta cike da tunani. Kalaman Fawaaz sun sake dawo mata da karfi,
"Nabeeha, ki yi amfani da ita. Hakanan."
Hakanan? Ta girgiza kai a hankali. Duk da miskilancinsa da kamun kansa, Fawaaz ba mutum bane da zai bada kyauta haka kawai. Wani abu ya sa shi yin haka, amma bai iya furtawa ba.
Ta lumshe ido, zuciyarta na bugawa da wani iri. Me yasa Fawaaz yake haka? Me yasa bai iya cewa komai kai tsaye ba? Me yasa yake boye komai a karkashin miskilancinsa?
***
Bayan kwana biyu, Nabeeha ta saba da sabuwar wayarta. Sai dai har yanzu, bata daina mamakin Fawaaz ba.
Tun daga lokacin da ya bata wayar, bai sake magana da ita ba. Kamar yadda ya saba, sai dai idanunshi da take ji kamar suna bin ta a duk lokacin da suke tare da kowa.
Wannan dare, tana dakin ta tana duba wayar. Bata san dalili ba, amma sai da ta shiga sakon ta na WhatsApp ta fara neman lambarsa. Sai ta tsinci kanta da kallon chat dinsu.
Kusan duk sakon da ya taba turawa yana da kamewa. "OK."
"Na gani."
"Zan duba."
Ko da wasa bai taba cewa wani abu mai yawa ba. Sai dai a tsakanin wadannan sakonnin masu takaitaccen lafazi, tana jin akwai abu da yake boyewa.
A hankali ta zura yatsarta ta rubuta,
"Yaa Fawaaz, nagode."
Ta aika, tana jin bugun zuciyarta yana karuwa.
Tana shirin kashe wayar, sai ta ga alamar typing. Zuciyarta ta tsaya cak.
Daga nan, sai sakonsa ya shigo.
"Ba komai."
Saukakken kalma ce. Amma tana jin kamar akwai wani nauyi tattare da ita.
Ta cije leɓe. Hannunta na rawa kaɗan, ta sake rubuta wani sako.
"Me yasa ka siya min ita?"
Sai shiru. Babu alamar typing. Babu komai.
Duk da haka, ta tabbata ya gani. Kuma ta tabbata yana ji kamar yadda take ji.
Tana ajiye wayar a kan filo, zuciyarta cike da tambayoyi da ba ta da amsarsu.
Fawaaz yana son boye kansa. Amma ita, tana jin kamar lokaci na zuwa da zai fuskanci zuciyarsa, ko da kuwa da kalmomi masu sauki ne.
Zuciyar da Ba Ta Magana
Fawaaz yana kwance a gadonsa, wayarsa a hannu, yana kallon sakon Nabeeha.
"Me yasa ka siya min ita?"
Zuciyarsa ta harba, amma bai motsa ba. Bai rubuta komai ba. Bai san me zai ce ba.
Me zai ce? "Saboda ina son ki"?
Hakan ba zai taba fita daga bakinsa ba.
Ko "Saboda ina kaunarki"?
Ai ma ya kasa furtawa ga kansa, balle kuma gareta.
Hannunsa ya kara matse wayar. Bai taba jin kansa haka ba. Bai taba jin tsoron furta abu ba kamar haka. Amma ita, ta sanya shi jin wani yanayi da bai saba da shi ba.
Sai ya kashe wayar, ya ajiye a gefensa, yana jin nauyin zuciyarsa.
***
A rana ta gaba, sun hadu a farfajiyar gidan. Kamar yadda aka saba, Fawaaz yana zaune ne yana duba laptop dinsa, yana duba wasu bayanai na aikin sa.
Nabeeha ta karaso, hannunta rike da wayar da ya bata.
A hankali ta tsaya a gabansa, tana kallonsa.
"Fawaaz."
Ya dago ido, fuskarsa kamar ba shi ya jiya sakonta ba jiya.
"Me yasa ka siya min ita?" Ta sake tambaya, kamar yadda ta rubuta a sakon WhatsApp.
Shiru. Ya kalleta, amma ba tare da ya furta komai ba.
Ta sauke ajiyar zuciya. "Idan ba ka son fada, ba komai. Amma na gode."
Ta juya da niyyar barin wajen.
Amma kafin ta taka mataki na biyu, sai ta ji muryarsa—mai sanyi, mai nauyi, wadda ta sa numfashinta tsayawa.
"Saboda na san wata rana, zan so jin muryarki... ko da kuwa ba za ki taba ji na na magana ba."
Ta tsaya cak, ta juyo da sauri. Idanunta suka sauka a kansa, amma har ya riga ya sunkuyar da kai, yana sake maida hankalinsa kan laptop dinsa, kamar ba shi ya furta kalmomin ba.
Zuciyarta ta harba. Ta bude baki da niyyar cewa wani abu, amma ba ta san me zata ce ba.
A karo na farko, Fawaaz ya bar zuciyarsa ta yi magana. Ko da kuwa a takaice ne.
Kuma ita ta fahimta. Ta fahimci komai.
______
Dakin shiru ne. Babu komai sai kiran iskar dare daga waje da kukan agogon bango yana tafiya a hankali.
Fawaaz yana kwance a gadonsa, hannunsa daya a dunkule, dayan kuma yana shafa gashin kansa a hankali, tamkar wanda yake tunanin matsala mai wuyar warwarewa.
Idanunsa a rufe, amma zuciyarsa ba ta huta ba. Duk da shiru da duhun dakin, tunaninta yana nan da shi. Yana jin numfashinta a cikin tunaninsa, yana ganin murmushinta a cikin duhun da ke rufe idanuwansa.
Ya juyo da gefen jikinsa, yana jin nauyin zuciyarsa kamar tana cike da wani abu da ba zai iya furtawa ba.
Yana son ta.
Ya san hakan.
Ya tabbatar da hakan fiye da yadda yake tabbatar da komai a rayuwarsa.
Amma yana gudu. Yana gudun furta abin da zuciyarsa ke ji.
Yana tsoron idan ya fadi, idan ya bayyana, me zai faru?
Me zai faru idan zuciyarsa ta bayyana sirrinta?
***
A cikin duhun dakin, idanunsa a rufe, yana iya hango ta kamar tana kusa da shi.
Yadda idanunta ke haskakawa idan tana magana. Yadda take dan taɓa hancinta idan tana tunani. Yadda take murmushi har dimples dinta su bayyana.
Ya tuno yadda take kokarin hana dariyarta fita idan wani abu ya bata dariya. Yadda idan tayi murmushi, zuciyarsa ke tafasa da wani yanayi da ya kasa misaltawa.
Kamar yana jin kamshin turarenta a kusa da shi. Wannan turaren da ya saba jin kamshinsa idan ta wuce kusa da shi, ko idan tana kusa da shi a dakin gaisuwa.
Ya runtse idanu da karfi.
Me yasa bai iya barin tunaninta ya fita daga zuciyarsa ba?
Ko zai yi bacci, da ita yake kwana.
A hankali ya kira Nabeeha, murya a daidai misali.
"Ina son ganinki a waje," kawai ya ce mata, ba tare da wata sharhi ba.
**A lokacin da ta fito, ya jingina da motarsa, hannayensa a cikin aljihu, idanunsa na kallon gefe tamkar ba shi ya kira ta ba. Nabeeha ta dan yi jinkiri tana nazarinsa, sannan ta karasa kusa da shi. Tana gayshe da shi..
"Ga wannan."
Bai iya kallonta ba yayin da ya miƙa mata wayar. Murya a dakile, kamar yana bayar da wani abu mara muhimmanci.😂
Nabeeha ta kalli wayar da mamaki. Idanunta sun cika da alamar tambaya.
"Wannan fa?"
Fawaaz bai amsa ba. Ya ɗan juya gefen fuskarsa, yana kallon wata hanya kamar wanda ba ruwansa da abin da ke faruwa.
"Ta waye.. ko tawa ce?" Ta tambaya a hankali, tana jin kamar mafarki take yi.
Ya numfasa kadan, yana cigaba da kallon gefe. "Ee."
Shiru ya biyo baya na ƴan dakiku. Sai da zuciyarta ta harba da wani yanayi mai rikitarwa.
"Nagode Allah ya Saka maka da alkhairi amin," ta ce cikin sanyin murya.
Bai amsa ba. Bai ce komai ba. Kawai ya jinjina kai kaɗan, sannan ya juya ya buɗe motarsa ya shiga fice daga gidan.
Yana barin wajen, zuciyarsa na bugawa da karfi. Bai ce mata komai ba. Bai iya furtawa ba. Amma ya san, daga yanzu, zai iya jin ta kusa da shi... ko da kuwa ta hanyar sakonni ne kawai.
Nabeeha ta tsaya a wajen, hannunta rike da wayar da ya bata. Kamar mafarki ne, kamar ba gaske ba. Idanunta sun cika da tambayoyi, amma wanda ya dace ya amsa su, tuni ya tafi.
Ta lumshe idanu, zuciyarta na harbawa. Ba wai sayen wayar bane matsalar amma yadda ya bayar. Yadda bai ce komai ba, yadda ko murmushi bai yi ba, yadda ya maze kamar ba wani abu mai muhimmanci ya aikata ba.
Wayar ta rike a tafin hannunta, tana jin nauyinta fiye da yadda ta kamata. A hankali ta shaka iska, sannan ta juya zuwa cikin gida, zuciyarta na ji kamar tana tafiya da wani SIRRI.
***
Fawaaz yana tuƙi, amma hankalinsa ba a kan titi yake ba. Bai masan dalilin futar sa daga gida ba, Ba don yana da horo ba, da tuni ya samu matsala. Yana ta kici-kicin tunanin abinda ya aikata.
Me yasa bai iya cewa komai ba?
Me yasa ba zai iya cewa "na siya miki ne domin dubun kaunar ki danake da tsananin kwadaituwa da son jin muryar ki.." ba?
Bai gama amsa wa kansa wadannan tambayoyin ba, sai wayarsa ta fara ƙara. Ya duba—Dr. Nabeeha Uzairu Muhammad.
Zuciyarsa ta harba. Sai dai ko da haka, ya tsare fuska kamar ba komai.
A hankali ya ɗaga, yana kokarin tabbatar da cewa muryarsa ba zata nuna wani motsin rai ba.
"Hello," ya ce a dakile.
Shiru daga dayan bangaren.
"Yaa Fawaaz..." Ta ambaci sunansa a hankali, kamar mai jin nauyin magana.
"Na'am," ya amsa, har yanzu ba tare da ya nuna wata alama ba.
"Ba ka gaya min me yasa ka siya min waya ba."
Sai da ya lumshe idanu kafin ya bude su a hankali. Bai san me zai ce ba.
"Saboda ina so ki dinga samun damar magana da kowa cikin sauki," ya ce, ba tare da ya yi tunani sosai ba.
Shiru.
"Yaa Fawaaz," ta sake kiran sunansa, murya a kasalance.
Ya ji kamar tana son tace wani abu. Kawai sai ya danyi ajiyar zuciya. "Nabeeha, ki yi amfani da ita. Hakanan."
Daga nan ya katse kiran.
Ya ajiye wayarsa a gefen kujera, ya dan tsare numfashinsa na ƴan dakiku. Bai san dalili ba, amma zuciyarsa na bugawa da wani iri.
Ya riga ya aikata. Kuma ko da kuwa bai fadi ba, ya san zata fahimta... ko ba yanzu ba, wata rana.
_1-KALBIM:MAMUH GEE_
_2-KIRJIN MAI HANKALI (AKWATIN SIRRIN SA):MSS XOXO_
_3-ADUNIYATAH :HUGUMAH_
_4-AJIYA A DUHU: BILYN ABDULL_
°°
_1-BOOK DAYA:DARI BIYAR_
_2-BOOKS BIYU:DUBU DAYA_
_3-BOOKS UKU: DUBU DAYA DA DARI BIYAR_
_4-BOOKS HUDU :DUBU BIYU_
_5_YAN NIJAR: 1000CF: 89825722 NOUSAIBA LAWALI MARADI_
_ku tura receipt zuwa ga 09033181070_
*IDAN KATI NE A TURO TA WANNAN NUMBER:*
*09032345899.. SHEDAR KATIN MA NAN ZAA TURA. KATIN MTN!!MTN!!*
____
*
*KIRJIN MAI HANKALI*
_(AKWATIN SIRRIN SA)_
🧳➿💞
*PG :24*
*AREWABOOKS VVIP:👇*
https://www.arewabooks.com/book?id=670bd07e35879b101764c0eb
__
Nabeeha ta kalli wayar a hannunta, zuciyarta cike da tunani. Kalaman Fawaaz sun sake dawo mata da karfi,
"Nabeeha, ki yi amfani da ita. Hakanan."
Hakanan? Ta girgiza kai a hankali. Duk da miskilancinsa da kamun kansa, Fawaaz ba mutum bane da zai bada kyauta haka kawai. Wani abu ya sa shi yin haka, amma bai iya furtawa ba.
Ta lumshe ido, zuciyarta na bugawa da wani iri. Me yasa Fawaaz yake haka? Me yasa bai iya cewa komai kai tsaye ba? Me yasa yake boye komai a karkashin miskilancinsa?
***
Bayan kwana biyu, Nabeeha ta saba da sabuwar wayarta. Sai dai har yanzu, bata daina mamakin Fawaaz ba.
Tun daga lokacin da ya bata wayar, bai sake magana da ita ba. Kamar yadda ya saba, sai dai idanunshi da take ji kamar suna bin ta a duk lokacin da suke tare da kowa.
Wannan dare, tana dakin ta tana duba wayar. Bata san dalili ba, amma sai da ta shiga sakon ta na WhatsApp ta fara neman lambarsa. Sai ta tsinci kanta da kallon chat dinsu.
Kusan duk sakon da ya taba turawa yana da kamewa. "OK."
"Na gani."
"Zan duba."
Ko da wasa bai taba cewa wani abu mai yawa ba. Sai dai a tsakanin wadannan sakonnin masu takaitaccen lafazi, tana jin akwai abu da yake boyewa.
A hankali ta zura yatsarta ta rubuta,
"Yaa Fawaaz, nagode."
Ta aika, tana jin bugun zuciyarta yana karuwa.
Tana shirin kashe wayar, sai ta ga alamar typing. Zuciyarta ta tsaya cak.
Daga nan, sai sakonsa ya shigo.
"Ba komai."
Saukakken kalma ce. Amma tana jin kamar akwai wani nauyi tattare da ita.
Ta cije leɓe. Hannunta na rawa kaɗan, ta sake rubuta wani sako.
"Me yasa ka siya min ita?"
Sai shiru. Babu alamar typing. Babu komai.
Duk da haka, ta tabbata ya gani. Kuma ta tabbata yana ji kamar yadda take ji.
Tana ajiye wayar a kan filo, zuciyarta cike da tambayoyi da ba ta da amsarsu.
Fawaaz yana son boye kansa. Amma ita, tana jin kamar lokaci na zuwa da zai fuskanci zuciyarsa, ko da kuwa da kalmomi masu sauki ne.
Zuciyar da Ba Ta Magana
Fawaaz yana kwance a gadonsa, wayarsa a hannu, yana kallon sakon Nabeeha.
"Me yasa ka siya min ita?"
Zuciyarsa ta harba, amma bai motsa ba. Bai rubuta komai ba. Bai san me zai ce ba.
Me zai ce? "Saboda ina son ki"?
Hakan ba zai taba fita daga bakinsa ba.
Ko "Saboda ina kaunarki"?
Ai ma ya kasa furtawa ga kansa, balle kuma gareta.
Hannunsa ya kara matse wayar. Bai taba jin kansa haka ba. Bai taba jin tsoron furta abu ba kamar haka. Amma ita, ta sanya shi jin wani yanayi da bai saba da shi ba.
Sai ya kashe wayar, ya ajiye a gefensa, yana jin nauyin zuciyarsa.
***
A rana ta gaba, sun hadu a farfajiyar gidan. Kamar yadda aka saba, Fawaaz yana zaune ne yana duba laptop dinsa, yana duba wasu bayanai na aikin sa.
Nabeeha ta karaso, hannunta rike da wayar da ya bata.
A hankali ta tsaya a gabansa, tana kallonsa.
"Fawaaz."
Ya dago ido, fuskarsa kamar ba shi ya jiya sakonta ba jiya.
"Me yasa ka siya min ita?" Ta sake tambaya, kamar yadda ta rubuta a sakon WhatsApp.
Shiru. Ya kalleta, amma ba tare da ya furta komai ba.
Ta sauke ajiyar zuciya. "Idan ba ka son fada, ba komai. Amma na gode."
Ta juya da niyyar barin wajen.
Amma kafin ta taka mataki na biyu, sai ta ji muryarsa—mai sanyi, mai nauyi, wadda ta sa numfashinta tsayawa.
"Saboda na san wata rana, zan so jin muryarki... ko da kuwa ba za ki taba ji na na magana ba."
Ta tsaya cak, ta juyo da sauri. Idanunta suka sauka a kansa, amma har ya riga ya sunkuyar da kai, yana sake maida hankalinsa kan laptop dinsa, kamar ba shi ya furta kalmomin ba.
Zuciyarta ta harba. Ta bude baki da niyyar cewa wani abu, amma ba ta san me zata ce ba.
A karo na farko, Fawaaz ya bar zuciyarsa ta yi magana. Ko da kuwa a takaice ne.
Kuma ita ta fahimta. Ta fahimci komai.
______
Dakin shiru ne. Babu komai sai kiran iskar dare daga waje da kukan agogon bango yana tafiya a hankali.
Fawaaz yana kwance a gadonsa, hannunsa daya a dunkule, dayan kuma yana shafa gashin kansa a hankali, tamkar wanda yake tunanin matsala mai wuyar warwarewa.
Idanunsa a rufe, amma zuciyarsa ba ta huta ba. Duk da shiru da duhun dakin, tunaninta yana nan da shi. Yana jin numfashinta a cikin tunaninsa, yana ganin murmushinta a cikin duhun da ke rufe idanuwansa.
Ya juyo da gefen jikinsa, yana jin nauyin zuciyarsa kamar tana cike da wani abu da ba zai iya furtawa ba.
Yana son ta.
Ya san hakan.
Ya tabbatar da hakan fiye da yadda yake tabbatar da komai a rayuwarsa.
Amma yana gudu. Yana gudun furta abin da zuciyarsa ke ji.
Yana tsoron idan ya fadi, idan ya bayyana, me zai faru?
Me zai faru idan zuciyarsa ta bayyana sirrinta?
***
A cikin duhun dakin, idanunsa a rufe, yana iya hango ta kamar tana kusa da shi.
Yadda idanunta ke haskakawa idan tana magana. Yadda take dan taɓa hancinta idan tana tunani. Yadda take murmushi har dimples dinta su bayyana.
Ya tuno yadda take kokarin hana dariyarta fita idan wani abu ya bata dariya. Yadda idan tayi murmushi, zuciyarsa ke tafasa da wani yanayi da ya kasa misaltawa.
Kamar yana jin kamshin turarenta a kusa da shi. Wannan turaren da ya saba jin kamshinsa idan ta wuce kusa da shi, ko idan tana kusa da shi a dakin gaisuwa.
Ya runtse idanu da karfi.
Me yasa bai iya barin tunaninta ya fita daga zuciyarsa ba?
Ko zai yi bacci, da ita yake kwana.