Sashe 12
Kirjin Mai Hankali Part 2 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Idanun Hajiya Zaytunah suka ciko da hawaye. “Na amince da ita… Na dauke ta tamkar uwar mu daya ubanmu daya. mijinta yayan mijina ne, Mahaifin ta yayan mahaifi nane. Rana daya aka haife mu. Tare muka tashi tun yarinta. Karewarta rana daya aka daura auren mu. Kai komai namu iri daya ne. … yaya za ta iya min haka?”
Nabeeha ta matso kusa da ita, ta rike hannunta. “Ammi…” Ta kira sunanta da murya mai rauni.
Hajiya Zaytunah ta girgiza kai, tana jin zuciyarta tana karyewa.
“Hakan ba zai yuwu ba… Rumanah ba za ta iya min haka ba…”
Amma zuciyarta ta sani, Idan har Gora da Bala sun fadi haka, to akwai gaskiya. Kuma hakan yana nufin akwai wani abu da take bukatar sani.
Bayan ‘yan dakiku, Hajiya Zaytunah ta dago kanta. Idanunta sun canza, sun yi ja. Ba hawaye take ba yanzu, Ba tsoro take ji ba, sai fushi da ƙudurin gano dalilin da yasa Hajiya Rumanah ta aikata wannan danyen aiki.
“Dole ne in san gaskiya.”
Ta juyo ta kalli Bala da Gora. “Ina son jin komai. Ina son sanin dalilin da ya sa ta aikata hakan.”
Bala ya lumshe ido, sannan ya furta: “Za ki ji komai, Hajiya. Amma dole ne mu fice daga nan da farko.”
Hajiya Zaytunah ta gyada kai, tana jin zuciyarta cike da zafi. Duk da cewa har yanzu ba ta gama fahimtar dalilin da yasa ‘yar uwarta za ta aikata hakan ba, ta san abu daya, ba za ta kyale wannan lamari haka kawai ba.
Da wannan kuduri a zuciyarta, Hajiya Zaytunah ta tsaya da ƙarfi. Babu gudu, babu ja da baya.
“lokaci yayi da AKWATI zai bude, SIRRI ka zasu bayyana. Fargaaba zata cika KIRJI, HANKALIn mutane da dama zai hauhawa.."
Haka dai suka dauki matakin barin wurin, yayin da zuciyar Hajiya Zaytunah ke tafasa da zafi, tana jira ta hadu da Hajiya Rumanah domin jin dalilin wannan mugunyar makarkashiya…
A cikin dare, motarsu na tafiya da sauri yayin da Bala ke kokarin kauce wa duk wata barazana. Gora yana zaune a baya tare da Hajiya Zaytunah da Nabeeha, amma duk zuciyarsu cike take da damuwa.
Hajiya Zaytunah ta kasa hakura. Ta sake duban Bala da Gora, zuciyarta na tafasa da fushi.
"Don Allah, ku gaya min komai. Ku daina ɓoye min gaskiya!"
Bala ya yi shiru, yana tunanin yadda zai bayyana abin da ya sani. Amma kafin ya iya magana, Gora ya riga shi.
"Hajiya, ba mu san ainihin dalilin da ya sa ta aikata hakan ba, amma shugabanmu ya ce Hajiya Rumanah ta fi son mu cutar da ku sosai kafin wai akai gashin kan ki da aka aske gareta, Ta bada umarni cewa a azabtar da ku a wulakanta ku, A tozarta ku. A Kuma raba wannan budurwar yar ta ki da mutuncin ta... Tamafi jaddada sunan yarinyar nan ta ki. Tace a tabbatar an rabata da martabarta.."
Jikin Hajiya Zaytunah ya yi sanyi. Ta jinjina kai, tana jin wani irin raɗaɗi a cikin zuciyarta.
"Ta yaya za ta iya yin haka? Me nayi mata?"
Bala ya gyada kai. "Wataƙila ta gaji da kasancewarki a duniya. Wataƙila tana jin tsoron wani abu a kanki."
Nabeeha, wadda ke shiru tun tuni, ta juyo tana kallon Ammin ta. "Me hakan ke nufi, Ammi? Me yasa za ta yi hakan?"
Hajiya Zaytunah ta numfasa, hawaye na taruwa a idanunta. "Nabeeha, Hajiya Rumanah matar yayan mahaifin kuce kamar yadda na fada, sannan yayata ce. Yar wan mahaifi na ce..gidan mu daya. Mun daɗe tare da ita, mun rayu a gida daya. Ban taɓa tunanin cewa wata rana za ta nemi hallakani ba."
Nabeeha ta ji jikin ta na rawa.
"Matar yayan baba na ce?!"
"Eh," Hajiya Zaytunah ta tabbatar da hakan. "Ta kasance kamar ‘yar uwa a gare ni, amma yanzu ta juyawa rayuwata baya."
Bala ya kalli Gora, sannan ya sake fuskantar Hajiya Zaytunah.
"Hajiya, akwai abu daya da ya kamata ki sani. A lokacin da aka ba mu aikin, an ce mana cewa dole ne mu tabbata cewa babu wanda zai sake jin labarinki ko ‘yar ki da danki. Kuma mun fahimci cewa tana matukar tsoron wani abu."
Hajiya Zaytunah ta jinjina kai, zuciyarta na tambayar kanta me hakan ke nufi. Me Rumanah ke tsoro har ta kai ga neman rayuwarta?
Bala ya ci gaba da magana, yana bayyana abinda ya ji daga bakin shugaban ‘yan fashin.
"Wani abu ne da ke tsakanin ki da ita. Wani abu da ya shafi rayuwar mijinta ko yayanta ne ko danta na dai manta"
Hajiya Zaytunah ta runtse ido. Ta san cewa akwai abubuwa da yawa da suka faru a baya, amma ko daya daga cikinsu bai yi mata kama da dalilin da zai sa Hajiya Rumanah ta nemi hallakawa ba.
"Dole ne in samu amsar tambayoyi na," ta furta a hankali, amma da ƙuduri mai karfi. "Ba zan bar wannan lamari haka ba."
Duk da cewa sun tsira daga wannan haɗari, hakan bai nufin cewa sun gama da barazana ba. Har yanzu akwai Hajiya Rumanah a can, mai cike da makirci da sharrinta. Kuma har yanzu ba su san menene ainihin dalilinta na yin haka ba.
Hajiya Zaytunah ta matse hannun Nabeeha, sannan ta dube su Bala da Gora.
"Babu komai, Allah yana tare da mu. Yadda ya kubutar da mu daga sansanin yan fashi. Da yardar Allah zai karasa warware duk wani tuggu da makirci, sharri da ma sihiri da ake aikatawa da yardar Allah. Komai nisan dare gari zai waye..Allah zai bayyana gaskiya.. Kuma shi sharri dan aike ne..idan ka turashi karka rufe kofa zai dawo maka..."
_1-KALBIM:MAMUH GEE_
_2-KIRJIN MAI HANKALI (AKWATIN SIRRIN SA):MSS XOXO_
_3-ADUNIYATAH :HUGUMAH_
_4-AJIYA A DUHU: BILYN ABDULL_
°°
_1-BOOK DAYA:DARI BIYAR_
_2-BOOKS BIYU:DUBU DAYA_
_3-BOOKS UKU: DUBU DAYA DA DARI BIYAR_
_4-BOOKS HUDU :DUBU BIYU_
_5_YAN NIJAR: 1000CF: 89825722 NOUSAIBA LAWALI MARADI_
_ku tura receipt zuwa ga 09033181070_
*IDAN KATI NE A TURO TA WANNAN NUMBER:*
*09032345899.. SHEDAR KATIN MA NAN ZAA TURA. KATIN MTN!!MTN!!*
____
*IDAN BANKI NE A TURA SHEDA ZUWA GA*
*09033181070*
*BANK NAME/SUNAN BANKI: ACCESS BANK*
*ACCOUNT NUMBER/LAMBAR ASUSUN BANKI: 0022419171*
*ACCOUNT NAME/SUNAN DAKE ASUSUN BANKI: MARYAM SANI GUMMI
*KIRJIN MAI HANKALI*
_(Akwatin sirrin sa)_
_🧳👩❤️👨🌺_
*_The Vault Of His Secrets_*
_®️NANA HAFSATU (MX)_
_©️ZAFAFA BIYAR WRITERS_
*_BOOK TWO_*
_PAGE: 11_
A dai-dai lokacin da Bala da Gora suka tsere da Hajiya Zaytunah dasu Nabeeha, wani sakon gaggawa ya isa wajen Hajiya Rumanah. Wani daga cikin mutanenta ya durƙusa gabanta yana sauke numfashi, alamar gajiya da hanzarin isowa.
“Hajiya, akwai matsala!”
Hajiya Rumanah ta ɗago daga inda take zaune a cikin wani falo mai ɗauke da kayan alfarma. Idanunta suka kaɗa, alamar ba ta da niyyar karɓar wata matsala a wannan lokacin.
“Wace irin matsala?!” Ta tambaya, muryarta cike da ƙwarin gwiwa.
Mutumin ya haɗiye yawu. “‘Yan fashin da aka ba aikin sun yi kuskure. Wataƙila wasu daga cikinsu sun canza ra’ayi, suka fitar da matar da yaranta daga hannunsu.”
Hajiya Rumanah ta tsinci kanta tana matse mayafinta da ƙarfi, zuciyarta na bugawa da sauri.
“Ba abu ne mai yiyuwa ba! Me kake nufi?!”
Mutumin ya sunkuyar da kansa. “Har yanzu ba mu da cikakken bayani, amma an ga wata mota da ta tsere daga sansanin. Shugaban ‘yan fashin yana kokarin bin sawu.”
Hajiya Rumanah ta tashi daga kujerarta cikin zafin rai.
"Ina bukatar su dawo hannuna da wuri! Ku nemo su, ku kamota, ko da kuwa za a kashe wanda ya aikata wannan cin amanar.”
Ta juyo ta kalle shi tana ɗaga hannu.
“Kira Shugaban ‘yan fashin! Ina son jin bayaninsa.”
A can gefen Bala da Gora kuwa, motarsu na cigaba da tafiya da sauri, suna kokarin kauce wa duk wata barazana. Amma duk da haka, suna jin tsoron cewa ba su gama da matsalar ba.
“Mun tsira daga sansanin, amma har yanzu ba mu fita daga haɗari ba, saboda manyan dazuka ne. Sanda Wanda muke cikinsa babban dajine mai zurfin kilomitoci” Bala ya faɗi, yana tsananta riƙon sitiyari.
Nabeeha ta cije leɓe, tana jin tsoron irin makomar da ke gabansu. Hajiya Zaytunah kuwa tana ta yi addu’a a cikin zuciyarta.
A can bayan su, fitilun motoci sun bayyana, alamar cewa suna bin sawu!
Gora ya juya da sauri ya duba ta bayan gilashin mota.
**
Bala ya yi kokarin tsayar da motar da sauri a bayan wani tsohon gini mai fashe-fashe. Wurin ya yi shiru sosai, kamar ba a taba zama a cikinsa ba. Ya juyo ya dubi Gora, yana busar da iska cikin gajiya.
“Muna bukatar mu ɓuya a nan har sai mun san inda suke.”
Gora ya duba kewayen wurin, zuciyarsa tana bugawa da sauri. “Amma idan sun same mu nan fa? Za su iya harbe mu kafin mu yi wani yunƙuri.”
Bala ya sauke ajiyar zuciya. “Muna da zabin da ya fi haka? Idan muka cigaba da tafiya cikin dare, za su iya bin sawun mu.”
Hajiya Zaytunah ta kalli su cikin damuwa. “Kun tabbata wurin nan zai iya kare mu?”
Bala ya juyo ya dubeta. “In Allah Ya yarda, muna da damar tsira. Amma dole ne ku bi umarninmu.”
Nabeeha ta kalli kewayen ginin, zuciyarta na dukan uku-uku. Wurin ya yi tsit, sai dai shure-shuren namun daji da iska mai kaɗawa. Ta kama hannun Hajiya Zaytunah, tana jin fargaba.
“Ammi, me zai faru da mu?” Ta tambaya a hankali.
Hajiya Zaytunah ta dafa kanta, tana murmushin da ke boye tsoro. “Za mu tsira, In Sha Allah.”
Bala da Gora suka fita daga motar suna lekawa don ganin ko akwai wata hanyar guduwa idan har abin ya tashi. Sun san cewa idan ‘yan fashin suka iso, ba za su tsaya da sunan neman bayani ba za su iya harbinsu a take.
A can gefe, hayakin tayar motoci ya bayyana daga nesa. Fitilun su na haskawa cikin duhun dare, alamar cewa ‘yan fashin sun kusa isowa.
Gora ya runtse ido. “Bala, ba su yi kasa a gwiwa ba. Har yanzu suna binmu.”
Bala ya furzar da iska mai zafi. “Idan sun shigo nan, za mu yi yunkurin juyar da hankalinsu. Idan na ce ku gudu, ku gudu babu ja da baya.”
Hajiya Zaytunah ta dubi Bala cikin damuwa. “Ya kuke tunanin za mu tsira daga gare su?”
Nabeeha ta matso kusa da ita, ta rike hannunta. “Ammi…” Ta kira sunanta da murya mai rauni.
Hajiya Zaytunah ta girgiza kai, tana jin zuciyarta tana karyewa.
“Hakan ba zai yuwu ba… Rumanah ba za ta iya min haka ba…”
Amma zuciyarta ta sani, Idan har Gora da Bala sun fadi haka, to akwai gaskiya. Kuma hakan yana nufin akwai wani abu da take bukatar sani.
Bayan ‘yan dakiku, Hajiya Zaytunah ta dago kanta. Idanunta sun canza, sun yi ja. Ba hawaye take ba yanzu, Ba tsoro take ji ba, sai fushi da ƙudurin gano dalilin da yasa Hajiya Rumanah ta aikata wannan danyen aiki.
“Dole ne in san gaskiya.”
Ta juyo ta kalli Bala da Gora. “Ina son jin komai. Ina son sanin dalilin da ya sa ta aikata hakan.”
Bala ya lumshe ido, sannan ya furta: “Za ki ji komai, Hajiya. Amma dole ne mu fice daga nan da farko.”
Hajiya Zaytunah ta gyada kai, tana jin zuciyarta cike da zafi. Duk da cewa har yanzu ba ta gama fahimtar dalilin da yasa ‘yar uwarta za ta aikata hakan ba, ta san abu daya, ba za ta kyale wannan lamari haka kawai ba.
Da wannan kuduri a zuciyarta, Hajiya Zaytunah ta tsaya da ƙarfi. Babu gudu, babu ja da baya.
“lokaci yayi da AKWATI zai bude, SIRRI ka zasu bayyana. Fargaaba zata cika KIRJI, HANKALIn mutane da dama zai hauhawa.."
Haka dai suka dauki matakin barin wurin, yayin da zuciyar Hajiya Zaytunah ke tafasa da zafi, tana jira ta hadu da Hajiya Rumanah domin jin dalilin wannan mugunyar makarkashiya…
A cikin dare, motarsu na tafiya da sauri yayin da Bala ke kokarin kauce wa duk wata barazana. Gora yana zaune a baya tare da Hajiya Zaytunah da Nabeeha, amma duk zuciyarsu cike take da damuwa.
Hajiya Zaytunah ta kasa hakura. Ta sake duban Bala da Gora, zuciyarta na tafasa da fushi.
"Don Allah, ku gaya min komai. Ku daina ɓoye min gaskiya!"
Bala ya yi shiru, yana tunanin yadda zai bayyana abin da ya sani. Amma kafin ya iya magana, Gora ya riga shi.
"Hajiya, ba mu san ainihin dalilin da ya sa ta aikata hakan ba, amma shugabanmu ya ce Hajiya Rumanah ta fi son mu cutar da ku sosai kafin wai akai gashin kan ki da aka aske gareta, Ta bada umarni cewa a azabtar da ku a wulakanta ku, A tozarta ku. A Kuma raba wannan budurwar yar ta ki da mutuncin ta... Tamafi jaddada sunan yarinyar nan ta ki. Tace a tabbatar an rabata da martabarta.."
Jikin Hajiya Zaytunah ya yi sanyi. Ta jinjina kai, tana jin wani irin raɗaɗi a cikin zuciyarta.
"Ta yaya za ta iya yin haka? Me nayi mata?"
Bala ya gyada kai. "Wataƙila ta gaji da kasancewarki a duniya. Wataƙila tana jin tsoron wani abu a kanki."
Nabeeha, wadda ke shiru tun tuni, ta juyo tana kallon Ammin ta. "Me hakan ke nufi, Ammi? Me yasa za ta yi hakan?"
Hajiya Zaytunah ta numfasa, hawaye na taruwa a idanunta. "Nabeeha, Hajiya Rumanah matar yayan mahaifin kuce kamar yadda na fada, sannan yayata ce. Yar wan mahaifi na ce..gidan mu daya. Mun daɗe tare da ita, mun rayu a gida daya. Ban taɓa tunanin cewa wata rana za ta nemi hallakani ba."
Nabeeha ta ji jikin ta na rawa.
"Matar yayan baba na ce?!"
"Eh," Hajiya Zaytunah ta tabbatar da hakan. "Ta kasance kamar ‘yar uwa a gare ni, amma yanzu ta juyawa rayuwata baya."
Bala ya kalli Gora, sannan ya sake fuskantar Hajiya Zaytunah.
"Hajiya, akwai abu daya da ya kamata ki sani. A lokacin da aka ba mu aikin, an ce mana cewa dole ne mu tabbata cewa babu wanda zai sake jin labarinki ko ‘yar ki da danki. Kuma mun fahimci cewa tana matukar tsoron wani abu."
Hajiya Zaytunah ta jinjina kai, zuciyarta na tambayar kanta me hakan ke nufi. Me Rumanah ke tsoro har ta kai ga neman rayuwarta?
Bala ya ci gaba da magana, yana bayyana abinda ya ji daga bakin shugaban ‘yan fashin.
"Wani abu ne da ke tsakanin ki da ita. Wani abu da ya shafi rayuwar mijinta ko yayanta ne ko danta na dai manta"
Hajiya Zaytunah ta runtse ido. Ta san cewa akwai abubuwa da yawa da suka faru a baya, amma ko daya daga cikinsu bai yi mata kama da dalilin da zai sa Hajiya Rumanah ta nemi hallakawa ba.
"Dole ne in samu amsar tambayoyi na," ta furta a hankali, amma da ƙuduri mai karfi. "Ba zan bar wannan lamari haka ba."
Duk da cewa sun tsira daga wannan haɗari, hakan bai nufin cewa sun gama da barazana ba. Har yanzu akwai Hajiya Rumanah a can, mai cike da makirci da sharrinta. Kuma har yanzu ba su san menene ainihin dalilinta na yin haka ba.
Hajiya Zaytunah ta matse hannun Nabeeha, sannan ta dube su Bala da Gora.
"Babu komai, Allah yana tare da mu. Yadda ya kubutar da mu daga sansanin yan fashi. Da yardar Allah zai karasa warware duk wani tuggu da makirci, sharri da ma sihiri da ake aikatawa da yardar Allah. Komai nisan dare gari zai waye..Allah zai bayyana gaskiya.. Kuma shi sharri dan aike ne..idan ka turashi karka rufe kofa zai dawo maka..."
_1-KALBIM:MAMUH GEE_
_2-KIRJIN MAI HANKALI (AKWATIN SIRRIN SA):MSS XOXO_
_3-ADUNIYATAH :HUGUMAH_
_4-AJIYA A DUHU: BILYN ABDULL_
°°
_1-BOOK DAYA:DARI BIYAR_
_2-BOOKS BIYU:DUBU DAYA_
_3-BOOKS UKU: DUBU DAYA DA DARI BIYAR_
_4-BOOKS HUDU :DUBU BIYU_
_5_YAN NIJAR: 1000CF: 89825722 NOUSAIBA LAWALI MARADI_
_ku tura receipt zuwa ga 09033181070_
*IDAN KATI NE A TURO TA WANNAN NUMBER:*
*09032345899.. SHEDAR KATIN MA NAN ZAA TURA. KATIN MTN!!MTN!!*
____
*IDAN BANKI NE A TURA SHEDA ZUWA GA*
*09033181070*
*BANK NAME/SUNAN BANKI: ACCESS BANK*
*ACCOUNT NUMBER/LAMBAR ASUSUN BANKI: 0022419171*
*ACCOUNT NAME/SUNAN DAKE ASUSUN BANKI: MARYAM SANI GUMMI
*KIRJIN MAI HANKALI*
_(Akwatin sirrin sa)_
_🧳👩❤️👨🌺_
*_The Vault Of His Secrets_*
_®️NANA HAFSATU (MX)_
_©️ZAFAFA BIYAR WRITERS_
*_BOOK TWO_*
_PAGE: 11_
A dai-dai lokacin da Bala da Gora suka tsere da Hajiya Zaytunah dasu Nabeeha, wani sakon gaggawa ya isa wajen Hajiya Rumanah. Wani daga cikin mutanenta ya durƙusa gabanta yana sauke numfashi, alamar gajiya da hanzarin isowa.
“Hajiya, akwai matsala!”
Hajiya Rumanah ta ɗago daga inda take zaune a cikin wani falo mai ɗauke da kayan alfarma. Idanunta suka kaɗa, alamar ba ta da niyyar karɓar wata matsala a wannan lokacin.
“Wace irin matsala?!” Ta tambaya, muryarta cike da ƙwarin gwiwa.
Mutumin ya haɗiye yawu. “‘Yan fashin da aka ba aikin sun yi kuskure. Wataƙila wasu daga cikinsu sun canza ra’ayi, suka fitar da matar da yaranta daga hannunsu.”
Hajiya Rumanah ta tsinci kanta tana matse mayafinta da ƙarfi, zuciyarta na bugawa da sauri.
“Ba abu ne mai yiyuwa ba! Me kake nufi?!”
Mutumin ya sunkuyar da kansa. “Har yanzu ba mu da cikakken bayani, amma an ga wata mota da ta tsere daga sansanin. Shugaban ‘yan fashin yana kokarin bin sawu.”
Hajiya Rumanah ta tashi daga kujerarta cikin zafin rai.
"Ina bukatar su dawo hannuna da wuri! Ku nemo su, ku kamota, ko da kuwa za a kashe wanda ya aikata wannan cin amanar.”
Ta juyo ta kalle shi tana ɗaga hannu.
“Kira Shugaban ‘yan fashin! Ina son jin bayaninsa.”
A can gefen Bala da Gora kuwa, motarsu na cigaba da tafiya da sauri, suna kokarin kauce wa duk wata barazana. Amma duk da haka, suna jin tsoron cewa ba su gama da matsalar ba.
“Mun tsira daga sansanin, amma har yanzu ba mu fita daga haɗari ba, saboda manyan dazuka ne. Sanda Wanda muke cikinsa babban dajine mai zurfin kilomitoci” Bala ya faɗi, yana tsananta riƙon sitiyari.
Nabeeha ta cije leɓe, tana jin tsoron irin makomar da ke gabansu. Hajiya Zaytunah kuwa tana ta yi addu’a a cikin zuciyarta.
A can bayan su, fitilun motoci sun bayyana, alamar cewa suna bin sawu!
Gora ya juya da sauri ya duba ta bayan gilashin mota.
**
Bala ya yi kokarin tsayar da motar da sauri a bayan wani tsohon gini mai fashe-fashe. Wurin ya yi shiru sosai, kamar ba a taba zama a cikinsa ba. Ya juyo ya dubi Gora, yana busar da iska cikin gajiya.
“Muna bukatar mu ɓuya a nan har sai mun san inda suke.”
Gora ya duba kewayen wurin, zuciyarsa tana bugawa da sauri. “Amma idan sun same mu nan fa? Za su iya harbe mu kafin mu yi wani yunƙuri.”
Bala ya sauke ajiyar zuciya. “Muna da zabin da ya fi haka? Idan muka cigaba da tafiya cikin dare, za su iya bin sawun mu.”
Hajiya Zaytunah ta kalli su cikin damuwa. “Kun tabbata wurin nan zai iya kare mu?”
Bala ya juyo ya dubeta. “In Allah Ya yarda, muna da damar tsira. Amma dole ne ku bi umarninmu.”
Nabeeha ta kalli kewayen ginin, zuciyarta na dukan uku-uku. Wurin ya yi tsit, sai dai shure-shuren namun daji da iska mai kaɗawa. Ta kama hannun Hajiya Zaytunah, tana jin fargaba.
“Ammi, me zai faru da mu?” Ta tambaya a hankali.
Hajiya Zaytunah ta dafa kanta, tana murmushin da ke boye tsoro. “Za mu tsira, In Sha Allah.”
Bala da Gora suka fita daga motar suna lekawa don ganin ko akwai wata hanyar guduwa idan har abin ya tashi. Sun san cewa idan ‘yan fashin suka iso, ba za su tsaya da sunan neman bayani ba za su iya harbinsu a take.
A can gefe, hayakin tayar motoci ya bayyana daga nesa. Fitilun su na haskawa cikin duhun dare, alamar cewa ‘yan fashin sun kusa isowa.
Gora ya runtse ido. “Bala, ba su yi kasa a gwiwa ba. Har yanzu suna binmu.”
Bala ya furzar da iska mai zafi. “Idan sun shigo nan, za mu yi yunkurin juyar da hankalinsu. Idan na ce ku gudu, ku gudu babu ja da baya.”
Hajiya Zaytunah ta dubi Bala cikin damuwa. “Ya kuke tunanin za mu tsira daga gare su?”