← Book details Kirjin Mai Hankali Part 2 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 41 OF 75

Sashe 41

Kirjin Mai Hankali Part 2 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Gwaggo zainabu ta dafa kafadar sa, tana kokarin kwantar masa da hankali. "Uzairu, ba fushi za mu yi ba. Abinda ya fi dacewa shi ne mu yi tunanin matakin da za mu ɗauka a yanzu."

Major General Dawud ya gyara zama, yana kallon su gaba ɗaya.

"Tabbas dole ne a yi abu akan wannan lamari. Amma kafin komai, dole ne mu tabbatar da cewa Zaytunah da iyalinta sun samu kariya daga duk wani abu da ka iya faruwa nan gaba."

Gwaggo Zainabu ta jinjina kai. "Eh, haka ya kamata. Mun dade muna neman ta, amma yanzu da Allah ya kawo mu gare ta, ba za mu ƙyale ta sake shan wahala ba."

A hankali, Alhaji Uzairu ya sauke ajiyar zuciya. Ya kalli Zaytunah, zuciyarsa na cike da raɗaɗi da kauna a lokaci guda.

"Ba zan taɓa barin ki sake fuskantar irin wannan ba, Zaytunah."

Hajiya Zaytunah ta lumshe ido, hawaye suka sake gangarowa daga idanunta. A karo na farko tun shekaru da dama, ta ji wata irin nutsuwa a cikin zuciyarta. Wataƙila, wannan ce ranar da za ta fara dawowa da kanta.

Shiru ne ya sake ratsa falon, kowa cikin dogon tunani. Wani irin nauyi ne ya danne zuciyar Alhaji Uzairu, amma dauriya kawai yake yi. A gefe guda yana ji kamar ya fusata, amma a dayan bangaren kuma zuciyarsa na cike da shauƙi da ƙauna, saboda a gaban sa ne matar da ya dade yana mafarkin ganin ta.

A hankali ya numfasa, ya kalli Zaytunah da idanunta suka cika da hawaye. A shekarun da suka wuce, ya yi tunanin cewa watakila ta manta da shi, watakila ta samu wani rayuwar daban, amma a yau, gashi da idanunsa yana jin labarin abin da ya raba su.

"Zaytunah..." Ya kira sunanta a hankali, kamar wanda ke jin tsoron ta ɓace masa.

Ta ɗan juyo, amma ba ta iya kallonsa kai tsaye ba. Numfashinta na fita a hankali, tana jin zuciyarta kamar zata fito waje.

"Kin dade a cikin duhu. Kin sha wahala. Amma na rantse da Allah, daga yau ba zan ƙyale wani ya sake cutar da ke ba." Muryarsa na nuna yadda zuciyarsa ta gama cika da alhini.

Hajiya Zaytunah ta lumshe ido, tana jin yadda kalamansa suka saukar mata da wani irin sanyi a zuciya. Daga lokacin da ta bar gidansa zuwa yanzu, ba ta taba jin irin wannan nutsuwa ba.

Gwaggo Hafsatu ta numfasa, ta kalli su duka da kulawa. "A yanzu, abin da yafi dacewa shi ne mu yanke shawarar yadda za a ci gaba. Zaytunah, ke dai kin shirya komawa gidan mijinki?"

Shiru ya ratsa falon. A hankali, Zaytunah ta dago kai, ta kalli Gwaggo Hafsatu.

"Ba wai ba na so ba, Gwaggo, amma ina jin tsoro. Ina jin tsoron komawa cikin wannan rayuwar, saboda har yanzu ba mu san abin da zai biyo baya ba."

Major General Dawud ya gyara zama, yana kallonta da kulawa. "Ba ke kadai kike jin hakan ba, Zaytunah. Amma muna tare da ke. Duk wanda ya sake kokarin cutar da ke, zai gamu da hukuncin da ya dace da shi."

Alhaji Amiru ya jinjina kai. "Haka ne. Kuma ba za mu tsaya a nan ba. Dole ne a bi wannan lamari a shari'ance. Mutanen da suka yi miki haka dole ne su fuskanci hukunci."

Alhaji Uzairu, wanda ya kasa jurewa, ya kalli Major General Dawud. "Ina bukatar taimakon ka, Janar. Ina so a yi bincike sosai a gano wadanda suka hada baki akan wannan mugun nufi."

Gwaggo Zainabu ta gyada kai cikin goyon baya. "Haka ya dace. Wannan ba abu ne da za a kyale ya wuce haka ba. Mun dade muna cikin duhu, amma yanzu gaskiya ta bayyana."

Hajiya Zaytunah ta sauke ajiyar zuciya, tana kallon su daya bayan daya. A karo na farko, ta fahimci cewa ba ita kadai ce. Tana da mutanen da suke tare da ita, wadanda za su kare ta, za su tsaya mata.

Ta juya, ta kalli Alhaji Uzairu. A karon farko tun bayan shigowarsa, ta kalle shi da tsananin kauna da tausayawa.

"Yaya uzairu..." Ta kira sunansa da wata irin nutsuwa. "Ina so ka fahimta cewa ba na manta da kai ba. Ban manta da kauna da zaman mu ba. Amma ina bukatar lokaci… Na shirya dawo wa, amma ina bukatar in tabbatar cewa babu hatsari."

Alhaji Uzairu ya fahimci tsoronta. Ya matso kusa da ita, yana dubanta da tsantsar soyayya. "Zaytunah, na amince da komai. Ba na matsa miki dole. Amma zan jira ki. Na jima ina jira, don haka babu matsala idan zan jira ki har sai da kika shirya."

Hajiya Zaytunah ta lumshe ido, ta dago cikin nutsuwa. "Nagode, Yaya Uzairu."

A gefen Gwaggo Hafsatu, Major General Dawud ya numfasa, yana jin wani nauyi ya sauka daga zuciyarsa. A yau, an warware wata babbar matsala da ta daɗe tana hana su sukuni.

Sai dai, wannan ba ƙarshen al’amari ba ne. Wannan ne farkon sabon babi a rayuwar su.

Sabon babi da ba za a iya hasashen yadda zai kaya ba....

ADVERT👇

YERWA INCENSE AND MORE
YERWA INCENSE AND MORE
YERWA INCENSE AND MORE

(THE SCENTS WITH DIFFERENT ESSENCE FOR YOU AND YOUR HOME)
(MASARAUTAR KAYAYYAKIN KAMSHI)

INA MA'ABOTA TURARE!
Shin kuna son gida mai ƙamshi da nutsuwa? Kaya masu ɗaukar hankalin kowa? YERWA INCENSE AND MORE ta kawo muku kayayyakin turaruka masu kyau, ingantattu, da tsada mai rahusa!

🌟 Mene ne za ku samu?

Turarukan wuta don gida, kaya, da tsugunno.

Khumrahs masu kamshi irin na Borno, Chadi, da Sudan.

Oil perfumes masu daɗin kamshi mai ɗorewa.

Turaren wanka, mopping, da wanki don dukkan sassan gida.

Man gashi mai gyara da fesa kamshi mai dadi.

Kayayyakin gyaran jiki na musamman don lafiya da ƙamshi mai ɗorewa.

📍 Adireshi:

Kano, amma muna tura kayayyakin mu duk fadin Najeriya da ƙetare.

📞 Tuntuɓe mu:

WhatsApp ko kira: 08095215215 / 09044191709 / 09134848107

Instagram: @yerwaincense_and_more

Facebook: @yerwacollection

Twitter:Hafsaaat00

🌐 Don ƙarin bayani da hotunan kayayyakin mu: Ku ziyarta mu a TikTok:
@besturarenwutainkano
https://www.tiktok.com/@besturarenwutainkano?_t=ZM-8s89xrbgS3x&_r=1

🎉 DON RAGI NA MUSAMMAN: Idan za ku siya, ku faɗi cewa daga ZAFAFA ne!

🌹 Ku more gida da jiki mai kamshi, nutsuwa, da farin ciki. Sai dai kayan turaren YERWA INCENSE AND MORE!

*KIRJIN MAI HANKALI*
_(Akwatin sirrin sa)_
              _🧳👩‍❤️‍👨🌺_

*_The Vault Of His Secrets_*

_®️NANA HAFSATU (MX)_

_©️ZAFAFA BIYAR WRITERS_

*_BOOK TWO_*

_PAGE:37_

Duhu ne ya mamaye dajin, iska mai sanyi na busawa yana tayar da ganyaye suna faduwa bisa kasa. Tsuntsaye sun daina rerawa, kamar sun san wani abu mai girma zai faru. A tsakiyar dajin, akwai wata bukka, daga gefe wuta tana tashi a cikin kwanon karfe, tana daukar wani irin hayaƙi mai wari. A cikin wannan bukkah ne Haruna ya hangi su Hajiya Rumanah, Hajiya Ladi, da Hajiya Karama zaune, suna fuskantar wani dattijo da ke rike da babban bokiti mai cike da ruwa.

Haruna ya dan tsuguna a bayan wata bishiya, zuciyarsa na bugawa da karfi. Bai taba zaton haka ba. Ya zo dajin ne don ya duba irin ayyukan da boka yake yi wa mutane, sai gashi ya hangi matan gidan Alhaji Uzairu cikin tsananin tawaya, suna rokon boka da yayi musu aiki.

“Me kuke so na yi muku?” Bokan ya tambaya da wata murya mai sautin tsoro.

Hajiya Rumanah ta dubi sauran matan, sannan ta ce, “Muna son ka kashe Hajiya Zaytunah da 'ya'yanta,Muhammad da Zainab. Wanda sunansu ya koma Nabeeha da Hammad! Ba mu son su dawo gidan Alhaji Uzairu, ba mu son su rayu ko kadan!”

Hajiya Ladi ta gyara zamanta, ta matsa kusa da boka. “Muna son ka hana ta komawa gidan. Idan har ta yi niyyar dawowa, sai ka kashe ta da wani mummunan ciwo.”

Hajiya Karama ta kara da cewa, “Dole ka tabbatar da cewa Nabeeha da Hammad ba su rayu ba. Muna bukatar su bace daga doron kasa.”

Bokan ya yi dariya, wacce ta girgiza zuciyar Haruna.

“Aiki ne mai sauki,” ya ce yana hada wasu magunguna cikin bokitinsa. “Zan musu tsibbu da kurciya. Matar ba za ta taba dawowa gidan mijinta ba, kuma idan har ta kuskura ta yi niyyar dawowa, to za ta halaka da kanta. Iyalanta kuwa, za su gamu da masifar da ba za su taba tsira da ita ba!”

Ya dauko wani farin foda ya yayyafa cikin ruwan da ke cikin bokiti. Wata irin hayaki mai duhu ya tashi, yana zagaye bukkarsa. Sai ya dauki wata kwarya ya dora a kan wutar. Daga nan ya fara karanta wasu munanan surkulle, yana hura iska cikin hayakin.

Haruna ya runtse idanuwansa, zuciyarsa na tafasa. Ya san cewa wannan bayani yana da matukar mahimmanci, dole ne a dauki mataki akai. Bai yi wata-wata ba, ya juya a hankali, yana kokarin barin wurin ba tare da sun gano shi ba.

Bayan Haruna ya sanar da Alhaji Amiru abin da ya gani, cikin sauri suka hada mutane suka shirya tafiya dajin. Sun san cewa dole ne a cafke wannan boka domin a gano gaskiyar lamari.

Suna isa bakin dajin, jami’an tsaro su goma sun rufe gefuna. Alhaji Amiru na gaba tare da Haruna, a gefensa akwai wasu manyan dattawa masu fada a ji. Kafin su karasa, sai suka hangi boka yana kokarin arcewa da wata kwarya a hannunsa.

“Kama shi!” Wani dan sanda ya daka tsawa, nan take wasu jami’ai suka danne shi suka daure hannayensa.

“Ku bar ni! Ku bar ni! Me kuke so ne da ni?” Bokan ya kurma ihu, yana kokarin kwace kansa.

Alhaji Amiru ya matso kusa, fuskarsa cike da tsananin takaici. “Za mu tafi da kai don ka fadi gaskiya! Za ka fadi wa duniya irin munanan ayyukan da kake aikatawa.”

Boka ya yi dariya, amma da ya hangi jami’an tsaro sun hada baki, sai ya sunkuyar da kansa. “To, zan fadi komai!”

A cikin babban dakin taro na gidan Gwaggo Zainabu, an daura boka a kujera, an daure hannayensa da igiya. A gabansa, su Alhaji Amiru, Alhaji Uzairu, Gwaggo Zainabu, da wasu manyan mutane sun yi shiru, suna jiran jin bayaninsa.

Gwaggo Zainabu ta matso kusa, idanunta cike da zafin rai. “Me yasa ka yarda ka karbi aikinsu?” Ta tambaya cikin daga murya.
Chapter 41 · 0% Book details