Sashe 2
Kirjin Mai Hankali Part 2 Complete Hausa Novel · about 8 min read
A wani sashe na daban, cikin wani katafaren gida mai dauke da kayan alatu, Hajiya Rumanah zaune take akan wata kujerar alfarma, hannunta rike da kofin shayi. Idanunta sun kada sun cika da tunani., Hajiya Karama da Hajiya Ladi suna zaune atare da ita , Da juice a hannayen su. kowacce na da fuskar da ba ta bayyana yarda ko damuwa.
Hajiya Karama ce ta fara magana, tana dube-dube kamar mai son tabbatar da cewa ba wanda ke leken su.
"Yanzu dai an kama su. Kuma an tafi da su wurin da ba wanda zai iya samun su." Ta fada da murya mai cike da kwanciyar hankali.
Hajiya Ladi ta gyara zaman mayafinta, ta kada kai tana murmushin jin dadi.
"Wannan ai babban nasara ne. Har yanzu ba wanda ya fahimci cewa mu muka tsara komai."
Hajiya Rumanah ta ajiye kofin shayinta a hankali, sannan ta dago kai, idanunta sun cika da wani irin kallo mai cike da natsuwa amma har yanzu ba ta nuna wata alama ta farin ciki ba.
"Ku tabbata cewa babu wata matsala. Ban yarda da waɗancan mutane ba sosai. Ko sun tabbatar mana da cewa sun yi abin da ya kamata?"
Hajiya Karama ta yi murmushi, sannan ta dan rankwafa kadan cikin muryar rada mai cakude da munafurci tace,
"Kada ki damu, Rumanah. Yan fashin nan sun fi kowa kwarewa. Mun tabbatar da cewa ba wanda zai iya kubutar da su."
Hajiya Ladi ta sake gyara mayafinta dake zumewa, ta dube su tana dariya.
"Yanzu dai abin da ya rage shine mu jira jin yadda za a yi. Idan dai komai ya tafi daidai, wannan maganar ta kare."
Hajiya Rumanah ta runtse idanu na wani lokaci, tana tunani mai zurfi. Daga bisani ta bude su, ta numfasa.
"Idan har suka samu damar kubuta, kun san abin da zai faru, ko?"
Dukansu suka yi shiru na dan lokaci. Sai Hajiya Karama ta gyara zaman rigarta, ta ce da murmushi,
"Ba za su kubuta ba."
"Aameen..Dan akwai babbar matsala idan hakan ta kasance..."
Haka dai suka cigaba da tattauna irin sake 'damarar shirin muguntar da zasu cigaba da yiwa Hajia Zaytunah da yaranta Nabeeha da Hammad...
🎀🎀🎀🎀
Hankalin Gwaggo Hafsatu gaba ɗaya ya tashi, tana a zaune a kan gadon asibitin da aka kwantar da ita. Duk da irin ciwon da kanta ya soma yi, zuciyarta na a tare da Zaytunah da 'ya'yanta.
Major General Dawud yana zaune gefenta, hannunsa rungume da wayarsa. Zuciyarsa na cike da damuwa, amma bai nuna sosai ba. Tun da aka kwantar da Gwaggo, yake jiran su Hajiya Zaytunah su iso. Basu iso ba. Tun dazu Kuma ya sanarwa mai dakin sa Hajiya Maijiddah kanta sanarwa Hajia Zaytunah ..
Ya ɗaga kai ya dubi matarsa, Hajiya Hauwa Maijidda, da ke tsaye a gefe tana gyara zaman hijabinta.
"Hauwa, kin tabbatar da kin sanar da su su taho?"
Ta gyada kai da tabbaci. Tana duban screen din wayarta..
"Eh, na tura mata sako tun dazu."
Ya gyara zama, zuciyarsa na raya masa wani abu. Ya ɗauki wayarsa, ya kira lambar Hajiya Zaytunah da kansa. Wayar ta yi ƙarar bata shiga..
Ya sake gwadawa, amma sai aka nuna "number not reachable."
Ya tsagaita, yana kallon wayar da jajayen idanu. Sai ya sake gwada lambar Nabeeha. A kashe.
Damuwa ta fara shigar masa da kyau. Hammad fa? Shi ma aka kashe tasa.
Wani irin sanyi ya ratsa zuciyarsa. Ya dubi Hajia Hauwa da jajayen idanu.
"Ki sake gwadawa mana, ko ta karanta sakon?"
Hajiya Hauwa Maijidda ta sake duba wayarta, ta shiga sakon da ta tura. Ta karanta.. Batare da bata lokaci ba, ta kira lambobin gida. Daya bayan daya, babu wanda ya daga.
Kamar yadda ya zata, babu wanda ke kusa da waya. Sai ya kira lambobin ma’aikatan gidan domin jin halin da ake ciki.
Babu wanda ke ɗauka.
Nan take zuciyarsa ta buga!
Gwaggo Hafsatu ta lura da yanayin fuskarsa.
"Dawuda, me ke faruwa?" Ta tambaya cikin raunanniyar murya.
Ya buɗe baki da ƙyar yana kokarin daidaita kansa yace
"Ba ma iya samun su."
"Me kake nufi da hakan?"
"Bakomai gwaggo. Kwantar da HANKALIn ki.." Bayan yace da gwaggon haka,
Ya tashi tsaye da sauri, yana kiran daya daga cikin masu gadin sa . Ya ɗauka a take. Bayan sun gaysa, Mai gadin ya tanbayi jikin gwaggon .. Major general yace da shi,
"Kana gida?"
"A'a, ranka ya daɗe, ni da wasu daga cikin ma'aikata mun fita siye-siye."
"Kana da masaniya kan inda su Hajiya Zaytunah da sauran yaran suke?"
"Eh, ranka ya daɗe. Ai sun fita tun dazu da motar Hammad. Sun ce zasu taho asibiti."
"Amma har yanzu basu iso ba!"
Mai gadin ya yi shiru na wasu dakiku..kafin yace,
"Allah Sarki, ranka ya daɗe. To ban san inda suka wuce ba. Ko sun samu cunkosu a titi"
Major General ya kashe wayar a fusace...
Gwaggo Hafsatu ta dafe KIRJIN ta.
"Innalillahi wa inna ilaihi raji’un! Dawuda, kar ka ce an samu matsala!"
Hajiya Hauwa Maijidda ta dube shi da tsananin tashin hankali.
"Ko dai hatsari suka yi?"
"Haba Hauwa. For heaven sake. " Ya karasa bata amsa yana narka mata uwar harara.
A wani yanayi mai cike da firgici, Major General Dawud ya sake duban wayarsa, ya fara kiran lambobin da suka dace don a fara bincike.
Zuciyarsa na bugawa da sauri. Bai taɓa jin irin wannan tsoron ba. Wannan ba al'ada ba ce..
Gwaggo Hafsatu ta rungume kanta da tafin hannayenta, idanuwanta sun kada.
"Allah Ka tsare su! Allah Ka kawo su lafiya!"
Major General ya furta da ƙarfi,
"Ba zan zauna ba har sai an gano inda suke. Inshaaa Allah gwaggo ba matsala." Ya shiga cewa da ita haka yana kokarin karfafa mata gwiwa..
"Tohm dawuda..." Ta fada tana sauke nannauyar ajiyar zuciya. Hade da rarumar carbinta ta cigaba da lazimi tana rokon Allah ya kawo musu mafita.
_1-KALBIM:MAMUH GEE_
_2-KIRJIN MAI HANKALI (AKWATIN SIRRIN SA):MSS XOXO_
_3-ADUNIYATAH :HUGUMAH_
_4-AJIYA A DUHU: BILYN ABDULL_
°°
_1-BOOK DAYA:DARI BIYAR_
_2-BOOKS BIYU:DUBU DAYA_
_3-BOOKS UKU: DUBU DAYA DA DARI BIYAR_
_4-BOOKS HUDU :DUBU BIYU_
_5_YAN NIJAR: 1000CF: 89825722 NOUSAIBA LAWALI MARADI_
_ku tura receipt zuwa ga 09032345899_
*IDAN KATI NE A TURO TA WANNAN NUMBER:*
*09032345899.. SHEDAR KATIN MA NAN ZAA TURA. KATIN MTN!!MTN!!*
____
*KIRJIN MAI HANKALI*
_(Akwatin sirrin sa)_
_🧳👩❤️👨🌺_
*_The Vault Of His Secrets_*
_®️NANA HAFSATU (MX)_
_©️ZAFAFA BIYAR WRITERS_
*_BOOK TWO_*
_PAGE:3_
Gabanta ya shiga dukan tara tara, yayin da ilahirin gabobin jikinta suka soma yi mata sanyi. Ganin an sake daukar wasu lokutan shiru ba alamar su ba labarin su.. Gashi su Raudah har sun taho asibitin daga gidah..
Gwaggo Hafsatu ta fashe da kuka mai ban tausayi, jikinta na karkarwa. Duk dakiyar da take da ita da kauda kai a abubuwa da kokarin boye damuwa.. kasancewar ta tsohuwa mai kamun kai da jan girmanta..Amman a ranar ta gaza boye dukkanin damuwarta. Tashiga tsananin dimuwa mai wuyar fassarawa. Domin tana jin kaunar Hajiya Zaytunah tamkar yar data haifa daga cikin cikinta. Hakama su Nabeeha tamkar su Raudah suke awajen ta. Ma'ana jikokin ta. Takance hajia zaytunah da yaranta amanace Allah ya damka a hannayen su itada major general dawud.
"Dawuda, Kada ka bari wani abu ya same su! Wallahi zuciyata tana kara nauyi!"
Major General Dawud ya daure, amma a ciki jikinsa shi kansa ya gama sanyi.. Duk makota, da sauran shagunan sayayya da aka san zasu iya biyawa anje basa nan... Don haka major general ba shida wasu sauran zantukan kwantar da HANKALI da zai fadawa mahaifiyar sa gwaggo Hafsatu akansu hajia zaytunah.. Ya numfasa kawai yana kada kai cikin girmamawa yace,
"Inshaa Allah Gwaggo..Allah ya datar da mu.. Kiyi hakuri"
Ya sake ɗaukar waya ya kira Brigadier General Mukhtar dake military intelligence unit. abokin aikin same wanda yake a karkashin sa yake a baya kafin yayi retire, Bayan sun gaysa ne. Brigd Gen.. Mukhtar ya numfasa,
"Yallabai!" Brigadier General Mukhtar ya amsa da girmamawa.
"An samu matsala! Ana buƙatar gaggawar bincike kan bacewar kanwata da yayanta daga gidana. Duk hanyoyin sadarwa sun katse, Kaganmu atare da Gwaggo ma a asibiti. Munyi iyaa mai yiwuwa wajen tattambayar makota, shaguna da wuraren da akasan zasu iya biyawa. Yes asibitin zasu zo...Ah Alhamdulillah da sauki. Okay zataji.. No gaskia basa zuwa ko'ina. Ba masu fita bane. Dan yarinya daya cema ke zuwa jami'a tare da daya yarinyata. To kuma driver ne ke kai su ya dawo dasu ko yayan su idan yana gari. Eh su uku ne. Ita Zaytunah, sai Nabeeha. Sai Hammad. Hammad din shi bama anan yake karatu ba a oversea ne. Eh tabbas, muna tunanin yiwuwar an yi garkuwa da su."
A ɗaya ɓangaren, Brigadier General Mukhtar ya farka gaba ɗaya. Jin labarin ban mamaki da tu'ajjabi..
"Ranka ya daɗe! Za mu fara aiki nan take! Ko akwai wani bayani na ƙarin haske?"
Major General ya runtse idanuwansa yana kokarin dakile wani abu dake kokarin taso masa daga ciki mai zafi,
"No, Muna jiran su nema su zo nan asibitin alfirdaus specialist dinnan na outskirt of cikin gari dinnan.amma tun ɗazun ba su iso ba. Duk wayoyin su a kashe, Kaga kuwa. Wannan ba karamun abu bane, akwai wani abun a kasa"
"Mun fahimta! Bari mu tara jami’anmu don a fara bincike nan take!"
"Godia nake..." Ya katse wayar bayan sunyi sallama..
"Inshaa Allah yanzu zasu fara aiki Gwaggo... Yana ma duba jikin ki kafin ya iso yace"
"Toh Allah yasa mu dache... Ina amsawa nagode kwarai"
Major general baiyi kasa a gwiwa ba. Ya sake danno kiran wani yaron sa, Bayan sun gaysa ne yake tambayar yaron inda yake,
"Ina barracks yallabai!"
"Inaso ka jagoranci bincike kan motar number motar nan da zan turo maka, Daga nan ka yi coordination da Intelligence Unit don mu gano inda aka kwashe su."
"Za a fara aiki nan take, ranka ya daɗe!"
Major General Dawud ya sauke ajiyar zuciya. Amma har yanzu, zuciyarsa na bugawa da tsanani. Ya juya ga Gwaggo Hafsatu da Hajiya Hauwa Maijidda.
"Inshaa Allah, Duk yadda za a yi, sai mun gano inda suke..Allah ya shige mana gaba yasa mu dache Amin"
"Toh Allah ya amince"
"Aameen" suka amsa baki daya...
Hajiya Karama ce ta fara magana, tana dube-dube kamar mai son tabbatar da cewa ba wanda ke leken su.
"Yanzu dai an kama su. Kuma an tafi da su wurin da ba wanda zai iya samun su." Ta fada da murya mai cike da kwanciyar hankali.
Hajiya Ladi ta gyara zaman mayafinta, ta kada kai tana murmushin jin dadi.
"Wannan ai babban nasara ne. Har yanzu ba wanda ya fahimci cewa mu muka tsara komai."
Hajiya Rumanah ta ajiye kofin shayinta a hankali, sannan ta dago kai, idanunta sun cika da wani irin kallo mai cike da natsuwa amma har yanzu ba ta nuna wata alama ta farin ciki ba.
"Ku tabbata cewa babu wata matsala. Ban yarda da waɗancan mutane ba sosai. Ko sun tabbatar mana da cewa sun yi abin da ya kamata?"
Hajiya Karama ta yi murmushi, sannan ta dan rankwafa kadan cikin muryar rada mai cakude da munafurci tace,
"Kada ki damu, Rumanah. Yan fashin nan sun fi kowa kwarewa. Mun tabbatar da cewa ba wanda zai iya kubutar da su."
Hajiya Ladi ta sake gyara mayafinta dake zumewa, ta dube su tana dariya.
"Yanzu dai abin da ya rage shine mu jira jin yadda za a yi. Idan dai komai ya tafi daidai, wannan maganar ta kare."
Hajiya Rumanah ta runtse idanu na wani lokaci, tana tunani mai zurfi. Daga bisani ta bude su, ta numfasa.
"Idan har suka samu damar kubuta, kun san abin da zai faru, ko?"
Dukansu suka yi shiru na dan lokaci. Sai Hajiya Karama ta gyara zaman rigarta, ta ce da murmushi,
"Ba za su kubuta ba."
"Aameen..Dan akwai babbar matsala idan hakan ta kasance..."
Haka dai suka cigaba da tattauna irin sake 'damarar shirin muguntar da zasu cigaba da yiwa Hajia Zaytunah da yaranta Nabeeha da Hammad...
🎀🎀🎀🎀
Hankalin Gwaggo Hafsatu gaba ɗaya ya tashi, tana a zaune a kan gadon asibitin da aka kwantar da ita. Duk da irin ciwon da kanta ya soma yi, zuciyarta na a tare da Zaytunah da 'ya'yanta.
Major General Dawud yana zaune gefenta, hannunsa rungume da wayarsa. Zuciyarsa na cike da damuwa, amma bai nuna sosai ba. Tun da aka kwantar da Gwaggo, yake jiran su Hajiya Zaytunah su iso. Basu iso ba. Tun dazu Kuma ya sanarwa mai dakin sa Hajiya Maijiddah kanta sanarwa Hajia Zaytunah ..
Ya ɗaga kai ya dubi matarsa, Hajiya Hauwa Maijidda, da ke tsaye a gefe tana gyara zaman hijabinta.
"Hauwa, kin tabbatar da kin sanar da su su taho?"
Ta gyada kai da tabbaci. Tana duban screen din wayarta..
"Eh, na tura mata sako tun dazu."
Ya gyara zama, zuciyarsa na raya masa wani abu. Ya ɗauki wayarsa, ya kira lambar Hajiya Zaytunah da kansa. Wayar ta yi ƙarar bata shiga..
Ya sake gwadawa, amma sai aka nuna "number not reachable."
Ya tsagaita, yana kallon wayar da jajayen idanu. Sai ya sake gwada lambar Nabeeha. A kashe.
Damuwa ta fara shigar masa da kyau. Hammad fa? Shi ma aka kashe tasa.
Wani irin sanyi ya ratsa zuciyarsa. Ya dubi Hajia Hauwa da jajayen idanu.
"Ki sake gwadawa mana, ko ta karanta sakon?"
Hajiya Hauwa Maijidda ta sake duba wayarta, ta shiga sakon da ta tura. Ta karanta.. Batare da bata lokaci ba, ta kira lambobin gida. Daya bayan daya, babu wanda ya daga.
Kamar yadda ya zata, babu wanda ke kusa da waya. Sai ya kira lambobin ma’aikatan gidan domin jin halin da ake ciki.
Babu wanda ke ɗauka.
Nan take zuciyarsa ta buga!
Gwaggo Hafsatu ta lura da yanayin fuskarsa.
"Dawuda, me ke faruwa?" Ta tambaya cikin raunanniyar murya.
Ya buɗe baki da ƙyar yana kokarin daidaita kansa yace
"Ba ma iya samun su."
"Me kake nufi da hakan?"
"Bakomai gwaggo. Kwantar da HANKALIn ki.." Bayan yace da gwaggon haka,
Ya tashi tsaye da sauri, yana kiran daya daga cikin masu gadin sa . Ya ɗauka a take. Bayan sun gaysa, Mai gadin ya tanbayi jikin gwaggon .. Major general yace da shi,
"Kana gida?"
"A'a, ranka ya daɗe, ni da wasu daga cikin ma'aikata mun fita siye-siye."
"Kana da masaniya kan inda su Hajiya Zaytunah da sauran yaran suke?"
"Eh, ranka ya daɗe. Ai sun fita tun dazu da motar Hammad. Sun ce zasu taho asibiti."
"Amma har yanzu basu iso ba!"
Mai gadin ya yi shiru na wasu dakiku..kafin yace,
"Allah Sarki, ranka ya daɗe. To ban san inda suka wuce ba. Ko sun samu cunkosu a titi"
Major General ya kashe wayar a fusace...
Gwaggo Hafsatu ta dafe KIRJIN ta.
"Innalillahi wa inna ilaihi raji’un! Dawuda, kar ka ce an samu matsala!"
Hajiya Hauwa Maijidda ta dube shi da tsananin tashin hankali.
"Ko dai hatsari suka yi?"
"Haba Hauwa. For heaven sake. " Ya karasa bata amsa yana narka mata uwar harara.
A wani yanayi mai cike da firgici, Major General Dawud ya sake duban wayarsa, ya fara kiran lambobin da suka dace don a fara bincike.
Zuciyarsa na bugawa da sauri. Bai taɓa jin irin wannan tsoron ba. Wannan ba al'ada ba ce..
Gwaggo Hafsatu ta rungume kanta da tafin hannayenta, idanuwanta sun kada.
"Allah Ka tsare su! Allah Ka kawo su lafiya!"
Major General ya furta da ƙarfi,
"Ba zan zauna ba har sai an gano inda suke. Inshaaa Allah gwaggo ba matsala." Ya shiga cewa da ita haka yana kokarin karfafa mata gwiwa..
"Tohm dawuda..." Ta fada tana sauke nannauyar ajiyar zuciya. Hade da rarumar carbinta ta cigaba da lazimi tana rokon Allah ya kawo musu mafita.
_1-KALBIM:MAMUH GEE_
_2-KIRJIN MAI HANKALI (AKWATIN SIRRIN SA):MSS XOXO_
_3-ADUNIYATAH :HUGUMAH_
_4-AJIYA A DUHU: BILYN ABDULL_
°°
_1-BOOK DAYA:DARI BIYAR_
_2-BOOKS BIYU:DUBU DAYA_
_3-BOOKS UKU: DUBU DAYA DA DARI BIYAR_
_4-BOOKS HUDU :DUBU BIYU_
_5_YAN NIJAR: 1000CF: 89825722 NOUSAIBA LAWALI MARADI_
_ku tura receipt zuwa ga 09032345899_
*IDAN KATI NE A TURO TA WANNAN NUMBER:*
*09032345899.. SHEDAR KATIN MA NAN ZAA TURA. KATIN MTN!!MTN!!*
____
*KIRJIN MAI HANKALI*
_(Akwatin sirrin sa)_
_🧳👩❤️👨🌺_
*_The Vault Of His Secrets_*
_®️NANA HAFSATU (MX)_
_©️ZAFAFA BIYAR WRITERS_
*_BOOK TWO_*
_PAGE:3_
Gabanta ya shiga dukan tara tara, yayin da ilahirin gabobin jikinta suka soma yi mata sanyi. Ganin an sake daukar wasu lokutan shiru ba alamar su ba labarin su.. Gashi su Raudah har sun taho asibitin daga gidah..
Gwaggo Hafsatu ta fashe da kuka mai ban tausayi, jikinta na karkarwa. Duk dakiyar da take da ita da kauda kai a abubuwa da kokarin boye damuwa.. kasancewar ta tsohuwa mai kamun kai da jan girmanta..Amman a ranar ta gaza boye dukkanin damuwarta. Tashiga tsananin dimuwa mai wuyar fassarawa. Domin tana jin kaunar Hajiya Zaytunah tamkar yar data haifa daga cikin cikinta. Hakama su Nabeeha tamkar su Raudah suke awajen ta. Ma'ana jikokin ta. Takance hajia zaytunah da yaranta amanace Allah ya damka a hannayen su itada major general dawud.
"Dawuda, Kada ka bari wani abu ya same su! Wallahi zuciyata tana kara nauyi!"
Major General Dawud ya daure, amma a ciki jikinsa shi kansa ya gama sanyi.. Duk makota, da sauran shagunan sayayya da aka san zasu iya biyawa anje basa nan... Don haka major general ba shida wasu sauran zantukan kwantar da HANKALI da zai fadawa mahaifiyar sa gwaggo Hafsatu akansu hajia zaytunah.. Ya numfasa kawai yana kada kai cikin girmamawa yace,
"Inshaa Allah Gwaggo..Allah ya datar da mu.. Kiyi hakuri"
Ya sake ɗaukar waya ya kira Brigadier General Mukhtar dake military intelligence unit. abokin aikin same wanda yake a karkashin sa yake a baya kafin yayi retire, Bayan sun gaysa ne. Brigd Gen.. Mukhtar ya numfasa,
"Yallabai!" Brigadier General Mukhtar ya amsa da girmamawa.
"An samu matsala! Ana buƙatar gaggawar bincike kan bacewar kanwata da yayanta daga gidana. Duk hanyoyin sadarwa sun katse, Kaganmu atare da Gwaggo ma a asibiti. Munyi iyaa mai yiwuwa wajen tattambayar makota, shaguna da wuraren da akasan zasu iya biyawa. Yes asibitin zasu zo...Ah Alhamdulillah da sauki. Okay zataji.. No gaskia basa zuwa ko'ina. Ba masu fita bane. Dan yarinya daya cema ke zuwa jami'a tare da daya yarinyata. To kuma driver ne ke kai su ya dawo dasu ko yayan su idan yana gari. Eh su uku ne. Ita Zaytunah, sai Nabeeha. Sai Hammad. Hammad din shi bama anan yake karatu ba a oversea ne. Eh tabbas, muna tunanin yiwuwar an yi garkuwa da su."
A ɗaya ɓangaren, Brigadier General Mukhtar ya farka gaba ɗaya. Jin labarin ban mamaki da tu'ajjabi..
"Ranka ya daɗe! Za mu fara aiki nan take! Ko akwai wani bayani na ƙarin haske?"
Major General ya runtse idanuwansa yana kokarin dakile wani abu dake kokarin taso masa daga ciki mai zafi,
"No, Muna jiran su nema su zo nan asibitin alfirdaus specialist dinnan na outskirt of cikin gari dinnan.amma tun ɗazun ba su iso ba. Duk wayoyin su a kashe, Kaga kuwa. Wannan ba karamun abu bane, akwai wani abun a kasa"
"Mun fahimta! Bari mu tara jami’anmu don a fara bincike nan take!"
"Godia nake..." Ya katse wayar bayan sunyi sallama..
"Inshaa Allah yanzu zasu fara aiki Gwaggo... Yana ma duba jikin ki kafin ya iso yace"
"Toh Allah yasa mu dache... Ina amsawa nagode kwarai"
Major general baiyi kasa a gwiwa ba. Ya sake danno kiran wani yaron sa, Bayan sun gaysa ne yake tambayar yaron inda yake,
"Ina barracks yallabai!"
"Inaso ka jagoranci bincike kan motar number motar nan da zan turo maka, Daga nan ka yi coordination da Intelligence Unit don mu gano inda aka kwashe su."
"Za a fara aiki nan take, ranka ya daɗe!"
Major General Dawud ya sauke ajiyar zuciya. Amma har yanzu, zuciyarsa na bugawa da tsanani. Ya juya ga Gwaggo Hafsatu da Hajiya Hauwa Maijidda.
"Inshaa Allah, Duk yadda za a yi, sai mun gano inda suke..Allah ya shige mana gaba yasa mu dache Amin"
"Toh Allah ya amince"
"Aameen" suka amsa baki daya...