← Book details Kirjin Mai Hankali Part 2 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 29 OF 75

Sashe 29

Kirjin Mai Hankali Part 2 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Ko zai farka, tana nan cikin tunaninsa.

Ko yana aiki, yana jin kamar zata fito daga wani wuri ta sake ce masa, "Yaa Fawaaz."

Muryarta tana da laushi, tana da wani irin sauti da ke sanya shi tsayawa tunani ko da kuwa yana cikin gagarumin aiki.

***

Ya kai hannu ya dauki wayarsa, yana kallon fuskar wayar na tsawon lokaci. Bai san dalili ba, amma sai da ya bude chat dinsu.

"Me yasa ka siya min ita?"

Tun jiya take jiran amsa. Tun jiya take son jin dalilin da yasa ya bata kyauta.

Shiru yayi yana kallon rubutun. Zuciyarsa na bugawa da karfi.

Yana da abubuwa da yawa da zai ce.

"Saboda kina da muhimmanci a wajena."
"Saboda na riga da na saba da kasancewarki kusa da zuciyata."
"Saboda... ina son ki, Nabeeha."

Sai ya dafe goshinsa a hankali.

Zai iya cewa haka?

Zai iya bude zuciyarsa da kansa?

Wani sashe na zuciyarsa yana son rubutawa. Yana son furta gaskiyar da yake boyewa tun farko.

Amma wani sashen yana hana shi.

Fawaaz ya kashe wayar, ya sake kwanciya, yana jin zuciyarsa tana bugawa kamar zai ji kalmomin da bai iya furtawa suna fitowa da kansu.

Zai iya boye zuciyarsa daga mutane.

Amma ba zai iya boye ta daga kansa ba.

Kuma babu shakka—wata rana, watakila daga bakin ta ko daga nashi, amma wata rana, wannan gaskiya da yake gujewa za ta fito fili.
....
Yana tsaye a cikin duhun bishiyoyi, yana boye jikinsa da kyau domin kada su gan shi. Daga inda yake, yana iya hango su Hajia Karama, Hajia Ladi, da Hajia Rumanah suna tsaye a gaban wani tsoho mai dogon gemu da jajayen idanun da ke cike da alamun sihiri.

A hankali ya matso da kunensa domin jin abin da suke fadi.

"Ba mu son kuskure wannan karon," cewar Hajia Karama, tana hadiye yawu.

"Dole a tabbata an shafe su gaba daya," Hajia Ladi ta ce tana girgiza kai. "Idan Zaytunah da yaranta sun wanzu, to wallahi, mu za mu zama matsala a idanun duniya."

Bokan ya kada sandarsa mai bakin ƙaho. "Kun tabbata ba wanda ya biyo ku?"

Hajia Rumanah ta dan saki murmushi. "Babu. Mun fito a hankalce sosai. Muna son a yi aikin da babu wanda zai taba sanin mu ne muka aikata."

"Toh ai na gaya muku," cewar bokan yana mai kada kansa. "Idan za a yi aikin, sai kun kawo mini wani abu da ke jikin wannan Zaytunah. Na biyu, dole a samo wani abu da zai shafi yaranta—wanda suka fi amfani da shi kullum."

Hajia Karama ta kalli Hajia Ladi, sai ta ce, "Zan samu mayafinta. Ni na san yadda zan yi hakan."

"Ina da kofin shan shayi da take amfani da shi kullum a baya" Hajia Rumanah ta kara da cewa.

Bokan ya kada kansa. "Duk wannan yana da kyau. Amma ku sani, idan har kuka biya kudin da ake bukata, to babu komai. Za a shafe su daga doron kasa."

Hajia Ladi ta zaro kudade masu yawa ta aje a gabansa. "Idan kudin ne, babu matsala. A tabbata aikin an yi shi yadda ya kamata."

Suka tsaya suna ci gaba da tsara yadda za a aikata abin da suke shiryawa.

Amma Haruna, daya daga cikin ma’aikatan gidan Alhaji Uzairu, yana jin komai daga inda yake laɓe.

Sun manta cewa idanun wani yana kansu.

Suna gamawa, suka fice cikin dare.

Haruna ya saki ajiyar zuciya, yana jin yadda gumi ya lulluɓe shi.

A cikin zuciyarsa, ya san wannan lamari yana da matukar hatsari. Idan har bai yi abu akai ba, to ba zai yafe wa kansa ba.

Dole ne ya sanar da Alhaji Amiru...

***

Alhaji Amiru yana zaune a cikin falonsa, yana nazarin wasu takardu, lokacin da Haruna ya shigo da sauri.

Da yake ya san shi a matsayin ma’aikacin gidan Alhaji Uzairu, sai ya kalle shi da mamaki.

"Haruna, lafiya kuwa?"

Haruna ya duka a gaban sa, yana kokarin daidaita numfashinsa.

"Alhaji... akwai matsala babba! Wata babbar fitina ake shiryawa!"

Alhaji Amiru ya jingina da kujera, yana jiran karin bayani.

"Alhaji," Haruna ya ci gaba da cewa, "Ni ne da idona na ji, da kunnuwana na saurara. Su Hajia Karama, Hajia Ladi, da Hajia Rumanah... sun je wajen boka domin a kashe su Zaytunah gaba daya! Sun bada kudi, sun kuma tsara yadda za a aikata hakan."

Zuciyar Alhaji Amiru ta buga da karfi.

Ya kafe Haruna da ido na sakanni da dama.

"Wani irin abu kake fada haka?" Ya tambaya, yana jin wani abu yana taso masa a KIRJI.

"Wallahi da gaskiya nake magana, Alhaji!" Haruna ya kara tabbatar da cewa ba karya yake ba. "Sun ce za su kawo wani abu da ke jikin Hajiya Zaytunah da yaranta domin a kammala aikin."

Alhaji Amiru ya shafa fuska da hannunsa, zuciyarsa na tafasa.

Ya san cewa su Hajia Karama suna da tsananin kiyayya, amma bai taba zaton za su kai ga irin wannan mummunan nufi ba.

Dole ne ya dauki mataki.

Bai tsaya wata-wata ba, ya dauki waya ya kira Alhaji Uzairu, sannan ya kira mahaifiyarsu, Gwaggo Zainabu.

***

A lokacin da suka zauna a babban falon gidan Alhaji Uzairu, shiru ne ya ratsa bayan Alhaji Amiru ya bayyana musu duk abin da ke faruwa.

Alhaji Uzairu ya girgiza kai, yana jin kamar ba a duniya yake ba.

"Babu yadda za a ce matana sun je wajen boka saboda su kashe Zaytunah!" Ya ce da karfi.

Alhaji Amiru ya kafe shi da ido. "Uzairu, ka tabbata da hakan? Ka tabbata da cewa su Hajia Karama ba su da irin wannan niyyar?"

Shiru ya biyo baya.

Gwaggo Zainabu ta sauke ajiyar zuciya.

"Idan da gaske ne wannan magana," ta ce cikin yanayi mai nauyi, "to dole ne mu dauki mataki kafin su aikata abin da suke so."

Alhaji Amiru ya mike tsaye, yana jin zuciyarsa na harbawa da karfi.

Idan har matan gidan suna da wannan mugun nufi, to dole a dakatar da su.

Domin ko ba komai, Zaytunah da ‘ya’yanta suna da hakkin rayuwa.

Ba za a bari wani ya shafe su daga doron kasa ba!

_1-KALBIM:MAMUH GEE_

_2-KIRJIN MAI HANKALI (AKWATIN SIRRIN SA):MSS XOXO_

_3-ADUNIYATAH :HUGUMAH_

_4-AJIYA A DUHU: BILYN ABDULL_
°°
_1-BOOK DAYA:DARI BIYAR_

_2-BOOKS BIYU:DUBU DAYA_

_3-BOOKS UKU: DUBU DAYA DA DARI BIYAR_

_4-BOOKS HUDU :DUBU BIYU_

_5_YAN NIJAR: 1000CF: 89825722 NOUSAIBA LAWALI MARADI_
_ku tura receipt zuwa ga 09033181070_

*IDAN KATI NE A TURO TA WANNAN NUMBER:*

*09032345899.. SHEDAR KATIN MA NAN ZAA TURA. KATIN MTN!!MTN!!*
____
*KIRJIN MAI HANKALI*
_(AKWATIN SIRRIN SA)_
            🧳➿💞

*PG :25*

*AREWABOOKS VVIP:👇*

https://www.arewabooks.com/book?id=670bd07e35879b101764c0eb

___

Shiru ya ratsa falon, kowanne daga cikinsu zuciyarsa tana tafasa.

Alhaji Uzairu ya jingina da kujera, yana girgiza kai tamkar wanda ya kasa yarda da abinda kunnuwansa suka ji.

"Subhan'Allah, Yaya Amiru," ya furta a hankali, yana dafe goshi. "An tabbatar da gaske Ladi da karama sune suka je wajen boka domin kashe Zaytunah?"

Alhaji Amiru ya cije lebe, yana kafe shi da ido. "Uzairu, ya kamata ka gane cewa kai ba ka san matanka ba. Kawai kana zaune kana tunanin komai lafiya kalau, alhalin wasu suna neman shafe daya daga cikin matan ka da ya’yan ka daga doron kasa!"

Gwaggo Zainabu ta sauke ajiyar zuciya mai nauyi.

"Yanzu me za a yi?" Ta tambaya, tana kallon Alhaji Amiru.

Alhaji Amiru ya kalli Haruna, wanda ya yi ta bayani a baya, ya kuma tabbatar da cewa abin da ya ji da kunnensa ba karya ba ne.

Daga bisani, ya kalli Alhaji Uzairu.

"Uzairu, ya kamata ka dauki mataki kafin lokaci ya kure," ya fada da kakkausar murya.

Alhaji Uzairu ya numfasa, zuciyarsa na tafasa da tunani iri-iri. Bai san cewa haka matansa suke ba. Bai taba tunanin cewa za su iya aikata irin wannan mummunan abu ba.

"Amma... ina bukatar hujja," ya ce cikin kasala.

"Kana bukatar hujja?" Alhaji Amiru ya tambaya yana kallonsa da mamaki. "Shin har yanzu baka yarda da abinda aka fada ba?"

"Ba wai ban yarda ba bane," Alhaji Uzairu ya ce, yana shafa fuskarsa. "Amma dole ne a tabbatar da komai kafin a dauki mataki."

Haruna ya gyara zama, yana fuskantar Alhaji Uzairu.

"Alhaji, wallahi da idona na gani, da kunnuwana na ji," ya fada cikin tabbaci. "Idan kuwa kuna bukatar wani shaida, zan iya komawa har wajen bokan domin a tabbatar."

"Ba dole sai ka koma ba," in ji Alhaji Amiru. "Dole ne mu dauki mataki tun kafin lokaci ya kure."

Gwaggo Zainabu ta jinjina kai.

"Amma su kansu ba su san an tona musu asiri ba, ko?"

"A’a," Haruna ya amsa. "Babu wanda ya san cewa na bi su, babu wanda ya san na ji komai."

Shiru ya sake ratsa falon.

Alhaji Uzairu ya dafe kansa, yana jin yadda zuciyarsa ke karyewa. Shin haka matansa suka zama? Su ne da suka daɗe suna tare da shi?

Gwaggo Zainabu ta yi gyaran murya, sannan ta kalli Alhaji Amiru.

"Yanzu me za ku yi?"

Alhaji Amiru ya sauke ajiyar zuciya.

"Muna bukatar mu fara da kare su Zaytunah," ya ce. "Dole ne mu tabbatar cewa sun fi kowane lokaci a cikin kariya."

"Ta yaya?" Gwaggo Zainabu ta tambaya.

Alhaji Amiru ya gyara zama. "Za mu samu Major General Dawud," ya ce. "Shi kadai ne zai iya tabbatar da cewa ba za a cutar da su ba. Idan har akwai wanda zai iya daukar mataki cikin gaggawa, to shi ne."

Gwaggo Zainabu ta gyada kai. "Hakan yayi. Amma fa, ba za mu bari su Karama su fahimci cewa an tona musu asiri ba."

"Tabbas," in ji Alhaji Amiru.

Sannan ya juyo ga Alhaji Uzairu.

"Uzairu, dole ne ka kara lura da matanka," ya ce cikin tsananin takaici. "Idan har ka barsu da wannan mugun nufi, to za su iya aikata abinda ba za ka taba yarda da shi ba."

Alhaji Uzairu ya lumshe ido, yana jin tamkar kansa zai fashe.

Bai san cewa matsalar ta kai haka ba.

Amma yanzu, babu abin da ya rage face daukar mataki....

Shiru ya sake ratsa falon, kowanne daga cikinsu zuciyarsa cike da tunani mai nauyi.

Gwaggo Zainabu ta dafa gefen kujera, ta dubi Alhaji Uzairu da idanuwanta da ke dauke da damuwa.
Chapter 29 · 0% Book details