Sashe 24
Kirjin Mai Hankali Part 2 Complete Hausa Novel · about 8 min read
A can bangaren, Hajiya Karama ta sauke ajiyar zuciya, sannan ta ce,
"To yanzu me za mu yi?"
"Dole mu dauki mataki kafin su fara magana!"
"Wane irin mataki?"
"Abu na farko shi ne dole mu tabbatar da cewa Alhaji Amiru bai ji wani abu ba. Abu na biyu, dole mu san yadda binciken nan ke tafiya ko sun riga sun samu wata hujja da zata iya kai su gare mu!"
"Tabbas!" Hajiya Karama ta ce cikin wata irin murya mai nuna damuwa. "Yanzu haka ya kamata ki kira Hajiya Ladi mu sanar da ita. Wannan magana fa ba karamin abu bane! Dare yayi ballantana naje wajenta.."
Hajiya Rumanah ta sauke ajiyar zuciya, sannan ta koma cikin lissafi. Ta san cewa Hajiya Ladi tana da muhimmanci a cikin wannan shiri. Ita ce ta fi sanin yadda za a yi da wannan lamarin, domin ta saba da irin wadannan dabaru.
Ba tare da bata lokaci ba, ta lalubi lambar Hajiya Ladi, ta danna kira.
Bugu biyu kacal aka dauka.
"Rumanah?" Muryar Hajiya Ladi ta fito da karfi, kamar wadda take cikin bacci. "Lafiya kuwa? Me ya faru?"
"Ladi, mun shiga matsala!"
"Matsala kuma?!"
"Eh! Sojoji sun kama su!"
A nan take, Hajiya Ladi ta mike a zaune. "Me kike nufi da sun kama su?"
"Na ce an kama ‘yan fashin nan baki daya! Daya ne kadai ya tsira, kuma ya bar garin gaba daya. Ya kira ni yanzu, yana cewa mutanen da muka saka a sace, sojoji sun kubutar da su!"
"Innalillahi wa inna ilaihi raji’un!" Hajiya Ladi ta furta, zuciyarta tana bugawa da sauri. "Rumanah, wannan abu yana da hadari sosai!"
"Na sani!" Hajiya Rumanah ta ce cikin tsawa. "Shi yasa na kira ku, don mu san matakin da za mu dauka kafin komai ya rikide!"
"To yanzu me kike ganin za a yi?"
Hajiya Rumanah ta lumshe idanu, tana kokarin tara duk wata dabara da zata iya amfani da ita.
"Na farko, dole mu samu cikakken bayani kan abin da ya faru. Dole ne mu san inda aka kai wadanda aka kama, su waye ke da alhakin binciken, sannan mu san ko akwai wanda ya riga ya fadawa Alhaji Amiru."
"Kwarai kuwa!" Hajiya Ladi ta ce, tana tunani. "Dole ne mu dauki mataki cikin gaggawa."
"Ba shakka!" Hajiya Karama ta katse su. "Ba za mu zauna muna jiran abin ya zo mana ba. Idan aka gano mu, to mu duka mun shiga uku!"
Hajiya Rumanah ta numfasa a hankali, tana jin zuciyarta tana tafarfasa. Ta san cewa daga wannan dare, dole ne ta tashi tsaye. Komai ya kusa rugujewa, kuma idan ba ta yi taka tsantsan ba, to babu shakka za ta iya rasa komai!
Hajiya Rumanah ta lumshe idanu, zuciyarta na tafarfasa. Hankalinta ya gama tashi, saboda tasirin wannan labari ya fi karfin yadda ta zata. Idan har sojoji sun kama su, kuma aka matsa musu da tambayoyi, babu makawa za su tona asirin ta!
Muryar Hajiya Ladi ce ta katse shirun da ya biyo bayan hirar su.
"Rumanah, lokaci ya kure! Dole mu dauki mataki yanzu kafin komai ya fita hannun mu."
Hajiya Karama ta gyada kai kamar tana kallonta, duk da cewa suna waya.
"Kwarai kuwa! Amma menene mafita? A ina aka ajiye su yanzu?"
Hajiya Rumanah ta dafe goshi, sannan ta ce cikin in'ina, "Ban sani ba har yanzu, amma na aika wani yaronmu da ya binciko. Da zarar ya dawo da bayani, zan sanar da ku."
"Ya kamata mu nemo wanda zai iya dakatar da wannan bincike tun kafin ya zurfafa," Hajiya Ladi ta ce da wata murya mai nuna karfin hali.
Hajiya Rumanah ta gyada kai. "Hakane. Idan muka samu wanda ke da karfi a wannan lamarin, zai iya hana maganar ta fita. Amma fa..." Ta yi shiru na dan lokaci.
"Me fa?" Hajiya Karama ta tambaya.
"Idan har Alhaji ya samu labari, ko kuma wani daga cikin su ya fadi sunana, to ko mene ne sai dai mu fuskanci hukunci."
Wani irin shiru ya ratsa tsakanin su. Kowannensu yana jin nauyin wannan magana.
Hajiya Ladi ce ta daka tsawa. "Ba zai yiwu hakan ba! Babu wanda zai tona mana asiri! Dole mu dauki matakin hana hakan faruwa."
"To yaya za mu yi?" Hajiya Karama ta tambaya, muryarta na nuna damuwa.
Hajiya Rumanah ta dube su cikin tunani. "Dole mu raba kan wadanda aka kama! Dole mu hana su yin magana tare, ko su hadu da wanda zai tunzura su su tona asirinmu."
Hajiya Ladi ta ja dogon numfashi. "Hakane. Amma har yanzu ba mu san wanda ke da alhakin binciken ba. Idan sojoji ne suka karbe shi gaba daya, to kuwa abu ya fi karfinmu."
"Zan bincika. Dole mu san da wa muke yi," Hajiya Rumanah ta ce, sannan ta kara da cewa, "Duk da haka, akwai abin da nake so ku kula da shi."
"Muna jinki," suka ce a tare.
Ta rage murya, kamar tana tsoron wani na sauraren su. "Dole mu yi taka-tsan-tsan da yadda muke mu'amala da Alhaji Idan muka nuna wata alama da zai sa ya fara tunani, zai iya gane komai."
Hajiya Karama ta gyada kai. "Hakane. Amma fa ya kamata mu shirya yadda za mu hana shi samun labarin nan gaba daya."
"Zan dauki matakin hana hakan faruwa," Hajiya Rumanah ta ce da wata murya mai cike da kaushin azama. "Idan har akwai wanda ya fara bincike ko ya samu wata shaida, dole mu dakatar da shi kafin ya kai labari wajen Alhaji"
Hajiya Ladi ta gyada kai, zuciyarta na bugawa da karfi. "Idan dai haka ne, to dole mu hada kai. Komai zai iya faruwa nan gaba kadan."
"Tabbas," Hajiya Rumanah ta ce. "Tun daga wannan dare, dole mu tashi tsaye! Dole mu yi komai don ganin ba a gano mu ba!"
Sun yi shiru na dan lokaci, kowannensu yana tunanin irin hadarin da ke gabansu. Wannan ba karamin aiki ba ne. Idan suka yi kuskure, to komai zai iya rikidewa zuwa masifa!
_1-KALBIM:MAMUH GEE_
_2-KIRJIN MAI HANKALI (AKWATIN SIRRIN SA):MSS XOXO_
_3-ADUNIYATAH :HUGUMAH_
_4-AJIYA A DUHU: BILYN ABDULL_
°°
_1-BOOK DAYA:DARI BIYAR_
_2-BOOKS BIYU:DUBU DAYA_
_3-BOOKS UKU: DUBU DAYA DA DARI BIYAR_
_4-BOOKS HUDU :DUBU BIYU_
_5_YAN NIJAR: 1000CF: 89825722 NOUSAIBA LAWALI MARADI_
_ku tura receipt zuwa ga 09033181070_
*IDAN KATI NE A TURO TA WANNAN NUMBER:*
*09032345899.. SHEDAR KATIN MA NAN ZAA TURA. KATIN MTN!!MTN!!*
____
*KIRJIN MAI HANKALI*
_(AKWATIN SIRRIN SA)_
🧳➿💞
*PG :20*
*AREWABOOKS VVIP:👇*
https://www.arewabooks.com/book?id=670bd07e35879b101764c0eb
___
Bayan sun kammala waya, Hajiya Rumanah ta sake komawa gefen gadonta, zuciyarta na bugawa da karfi. Dole ta yanke shawarar da zata kare ta kafin komai ya rikide.
Ta janyo wayarta, ta kira wani lambobi da ba kasafai take amfani da su ba. Tana danna kira, numfashinta ya sauya, hannunta yana kerma.
Bugu daya kacal aka dauka.
"Hajiya Rumanah," wata murya mai zurfi ta karanto sunanta, kamar wanda ya san dalilin kiran nata.
"Abubakar," ta furta cikin nutsuwa, "muna da matsala!"
"Na riga da na samu labari," ya ce, yana mai shafar gashinsa da ke gefe. "Meye kike so in yi?"
"Ina bukatar ka binciko min cikakken bayani, wa ke da alhakin binciken nan? Ina aka kai wadanda aka kama? Kuma ina so in san ko wani abu ya riga ya isa kunnen Alhaji Amiru."
"Zan yi hakan," ya ce ba tare da wata jinkiri ba. "Amma fa Hajiya, yana da kyau ki rage motsi a yanzu. Idan kika yi gaggawa da yawa, zai iya jawo hankali."
"Ba na bukatar shawararka!" ta katse shi da takaici. "Ina so ka yi abin da na ce, kuma ka tabbatar da cewa na samu bayani kafin gari ya waye!"
Ya yi shiru na dan lokaci, sannan ya ce, "Zan tuntuɓi mutanena."
"Kuma," ta kara da cewa, "idan akwai wanda ya fara magana, ko ake shirin tuhumarsa dole a dauki mataki kafin su tona asirinmu!"
Muryarsa ta koma mai nauyi. "Kin san me hakan ke nufi, ko?"
"Na sani!" ta furta da karfi. "Idan har muna son mu tsira, dole mu yi komai da zai hana mu faduwa!"
Ya sauke ajiyar zuciya, sannan ya ce, "Zan yi abin da zan iya."
"Kar ka bari wani abu ya kubuce mana," ta fadi, sannan ta kashe wayar batare da ta jira amsarsa ba.
A wannan lokacin, Alhaji Amiru yana zaune a falo, yana tunanin maganganun da Hajiya Rumanah ta fada masa da daddare. Wani irin matsanancin tunani ya lullube shi.
Me yasa take jin tsoro haka? Me yasa take ta matsawa da jin ko ya samu labari game da Hajiya Zaytunah da yaranta?
Ya dafa goshinsa, yana jin zuciyarsa na bugawa da karfi. Bai taba tunanin cewa wata rana zai fara zargin matarsa ba, amma yanzu yana jin kamar akwai wani abu da take boyewa!
Sai kawai ya dauki wayarsa, ya kira daya daga cikin mutanensa masu SIRRI.
"Baffa, ina bukatar ka bincika min wani abu."
"Ina sauraron ka ranka ya dade..."
"Ina so ka binciko min game da harin da aka kai kwanakin baya... na sace mutanen nan da aka ce sojoji sun ceto."
A dayan bangaren, Baffa ya dan yi shiru, sannan ya ce, "Alhaji, kana nufin garkuwa da mutanen nan? An ce fa an tarwatsa ‘yan fashin gaba daya."
"Eh," Alhaji Amiru ya ce, yana jin yadda zuciyarsa ke tafasa. "Ina so in san wa ke da alhakin wannan aika-aika. Kuma ina so a binciko min wanda ke da hannu a bayan fage."
Baffa ya numfasa. "Zan bincika, Alhaji. Amma fa wannan batu yana da sarkakiya."
"Kawai ka yi min bincike. Ina bukatar cikakken bayani cikin gaggawa."
Ya kashe wayar, sannan ya jingina da kujerarsa. Zuciyarsa na bugawa...
Idan har akwai wanda ya shigo da Hajiya Zaytunah cikin matsala, dole ya gano! Kuma idan har wannan abu yana da alaka da wani daga cikin iyalinsa… to, babu shakka, hakan ba zai wuce ba tare da hukunci ba!
Hajiya Rumanah ta gama fidda umarni, amma zuciyarta har yanzu bata samun nutsuwa. Wata zuciya na gaya mata ta bar komai haka nan, amma tsoron abin da zai iya biyo baya ya hana ta yin watsi da lamarin.
"To yanzu me za mu yi?"
"Dole mu dauki mataki kafin su fara magana!"
"Wane irin mataki?"
"Abu na farko shi ne dole mu tabbatar da cewa Alhaji Amiru bai ji wani abu ba. Abu na biyu, dole mu san yadda binciken nan ke tafiya ko sun riga sun samu wata hujja da zata iya kai su gare mu!"
"Tabbas!" Hajiya Karama ta ce cikin wata irin murya mai nuna damuwa. "Yanzu haka ya kamata ki kira Hajiya Ladi mu sanar da ita. Wannan magana fa ba karamin abu bane! Dare yayi ballantana naje wajenta.."
Hajiya Rumanah ta sauke ajiyar zuciya, sannan ta koma cikin lissafi. Ta san cewa Hajiya Ladi tana da muhimmanci a cikin wannan shiri. Ita ce ta fi sanin yadda za a yi da wannan lamarin, domin ta saba da irin wadannan dabaru.
Ba tare da bata lokaci ba, ta lalubi lambar Hajiya Ladi, ta danna kira.
Bugu biyu kacal aka dauka.
"Rumanah?" Muryar Hajiya Ladi ta fito da karfi, kamar wadda take cikin bacci. "Lafiya kuwa? Me ya faru?"
"Ladi, mun shiga matsala!"
"Matsala kuma?!"
"Eh! Sojoji sun kama su!"
A nan take, Hajiya Ladi ta mike a zaune. "Me kike nufi da sun kama su?"
"Na ce an kama ‘yan fashin nan baki daya! Daya ne kadai ya tsira, kuma ya bar garin gaba daya. Ya kira ni yanzu, yana cewa mutanen da muka saka a sace, sojoji sun kubutar da su!"
"Innalillahi wa inna ilaihi raji’un!" Hajiya Ladi ta furta, zuciyarta tana bugawa da sauri. "Rumanah, wannan abu yana da hadari sosai!"
"Na sani!" Hajiya Rumanah ta ce cikin tsawa. "Shi yasa na kira ku, don mu san matakin da za mu dauka kafin komai ya rikide!"
"To yanzu me kike ganin za a yi?"
Hajiya Rumanah ta lumshe idanu, tana kokarin tara duk wata dabara da zata iya amfani da ita.
"Na farko, dole mu samu cikakken bayani kan abin da ya faru. Dole ne mu san inda aka kai wadanda aka kama, su waye ke da alhakin binciken, sannan mu san ko akwai wanda ya riga ya fadawa Alhaji Amiru."
"Kwarai kuwa!" Hajiya Ladi ta ce, tana tunani. "Dole ne mu dauki mataki cikin gaggawa."
"Ba shakka!" Hajiya Karama ta katse su. "Ba za mu zauna muna jiran abin ya zo mana ba. Idan aka gano mu, to mu duka mun shiga uku!"
Hajiya Rumanah ta numfasa a hankali, tana jin zuciyarta tana tafarfasa. Ta san cewa daga wannan dare, dole ne ta tashi tsaye. Komai ya kusa rugujewa, kuma idan ba ta yi taka tsantsan ba, to babu shakka za ta iya rasa komai!
Hajiya Rumanah ta lumshe idanu, zuciyarta na tafarfasa. Hankalinta ya gama tashi, saboda tasirin wannan labari ya fi karfin yadda ta zata. Idan har sojoji sun kama su, kuma aka matsa musu da tambayoyi, babu makawa za su tona asirin ta!
Muryar Hajiya Ladi ce ta katse shirun da ya biyo bayan hirar su.
"Rumanah, lokaci ya kure! Dole mu dauki mataki yanzu kafin komai ya fita hannun mu."
Hajiya Karama ta gyada kai kamar tana kallonta, duk da cewa suna waya.
"Kwarai kuwa! Amma menene mafita? A ina aka ajiye su yanzu?"
Hajiya Rumanah ta dafe goshi, sannan ta ce cikin in'ina, "Ban sani ba har yanzu, amma na aika wani yaronmu da ya binciko. Da zarar ya dawo da bayani, zan sanar da ku."
"Ya kamata mu nemo wanda zai iya dakatar da wannan bincike tun kafin ya zurfafa," Hajiya Ladi ta ce da wata murya mai nuna karfin hali.
Hajiya Rumanah ta gyada kai. "Hakane. Idan muka samu wanda ke da karfi a wannan lamarin, zai iya hana maganar ta fita. Amma fa..." Ta yi shiru na dan lokaci.
"Me fa?" Hajiya Karama ta tambaya.
"Idan har Alhaji ya samu labari, ko kuma wani daga cikin su ya fadi sunana, to ko mene ne sai dai mu fuskanci hukunci."
Wani irin shiru ya ratsa tsakanin su. Kowannensu yana jin nauyin wannan magana.
Hajiya Ladi ce ta daka tsawa. "Ba zai yiwu hakan ba! Babu wanda zai tona mana asiri! Dole mu dauki matakin hana hakan faruwa."
"To yaya za mu yi?" Hajiya Karama ta tambaya, muryarta na nuna damuwa.
Hajiya Rumanah ta dube su cikin tunani. "Dole mu raba kan wadanda aka kama! Dole mu hana su yin magana tare, ko su hadu da wanda zai tunzura su su tona asirinmu."
Hajiya Ladi ta ja dogon numfashi. "Hakane. Amma har yanzu ba mu san wanda ke da alhakin binciken ba. Idan sojoji ne suka karbe shi gaba daya, to kuwa abu ya fi karfinmu."
"Zan bincika. Dole mu san da wa muke yi," Hajiya Rumanah ta ce, sannan ta kara da cewa, "Duk da haka, akwai abin da nake so ku kula da shi."
"Muna jinki," suka ce a tare.
Ta rage murya, kamar tana tsoron wani na sauraren su. "Dole mu yi taka-tsan-tsan da yadda muke mu'amala da Alhaji Idan muka nuna wata alama da zai sa ya fara tunani, zai iya gane komai."
Hajiya Karama ta gyada kai. "Hakane. Amma fa ya kamata mu shirya yadda za mu hana shi samun labarin nan gaba daya."
"Zan dauki matakin hana hakan faruwa," Hajiya Rumanah ta ce da wata murya mai cike da kaushin azama. "Idan har akwai wanda ya fara bincike ko ya samu wata shaida, dole mu dakatar da shi kafin ya kai labari wajen Alhaji"
Hajiya Ladi ta gyada kai, zuciyarta na bugawa da karfi. "Idan dai haka ne, to dole mu hada kai. Komai zai iya faruwa nan gaba kadan."
"Tabbas," Hajiya Rumanah ta ce. "Tun daga wannan dare, dole mu tashi tsaye! Dole mu yi komai don ganin ba a gano mu ba!"
Sun yi shiru na dan lokaci, kowannensu yana tunanin irin hadarin da ke gabansu. Wannan ba karamin aiki ba ne. Idan suka yi kuskure, to komai zai iya rikidewa zuwa masifa!
_1-KALBIM:MAMUH GEE_
_2-KIRJIN MAI HANKALI (AKWATIN SIRRIN SA):MSS XOXO_
_3-ADUNIYATAH :HUGUMAH_
_4-AJIYA A DUHU: BILYN ABDULL_
°°
_1-BOOK DAYA:DARI BIYAR_
_2-BOOKS BIYU:DUBU DAYA_
_3-BOOKS UKU: DUBU DAYA DA DARI BIYAR_
_4-BOOKS HUDU :DUBU BIYU_
_5_YAN NIJAR: 1000CF: 89825722 NOUSAIBA LAWALI MARADI_
_ku tura receipt zuwa ga 09033181070_
*IDAN KATI NE A TURO TA WANNAN NUMBER:*
*09032345899.. SHEDAR KATIN MA NAN ZAA TURA. KATIN MTN!!MTN!!*
____
*KIRJIN MAI HANKALI*
_(AKWATIN SIRRIN SA)_
🧳➿💞
*PG :20*
*AREWABOOKS VVIP:👇*
https://www.arewabooks.com/book?id=670bd07e35879b101764c0eb
___
Bayan sun kammala waya, Hajiya Rumanah ta sake komawa gefen gadonta, zuciyarta na bugawa da karfi. Dole ta yanke shawarar da zata kare ta kafin komai ya rikide.
Ta janyo wayarta, ta kira wani lambobi da ba kasafai take amfani da su ba. Tana danna kira, numfashinta ya sauya, hannunta yana kerma.
Bugu daya kacal aka dauka.
"Hajiya Rumanah," wata murya mai zurfi ta karanto sunanta, kamar wanda ya san dalilin kiran nata.
"Abubakar," ta furta cikin nutsuwa, "muna da matsala!"
"Na riga da na samu labari," ya ce, yana mai shafar gashinsa da ke gefe. "Meye kike so in yi?"
"Ina bukatar ka binciko min cikakken bayani, wa ke da alhakin binciken nan? Ina aka kai wadanda aka kama? Kuma ina so in san ko wani abu ya riga ya isa kunnen Alhaji Amiru."
"Zan yi hakan," ya ce ba tare da wata jinkiri ba. "Amma fa Hajiya, yana da kyau ki rage motsi a yanzu. Idan kika yi gaggawa da yawa, zai iya jawo hankali."
"Ba na bukatar shawararka!" ta katse shi da takaici. "Ina so ka yi abin da na ce, kuma ka tabbatar da cewa na samu bayani kafin gari ya waye!"
Ya yi shiru na dan lokaci, sannan ya ce, "Zan tuntuɓi mutanena."
"Kuma," ta kara da cewa, "idan akwai wanda ya fara magana, ko ake shirin tuhumarsa dole a dauki mataki kafin su tona asirinmu!"
Muryarsa ta koma mai nauyi. "Kin san me hakan ke nufi, ko?"
"Na sani!" ta furta da karfi. "Idan har muna son mu tsira, dole mu yi komai da zai hana mu faduwa!"
Ya sauke ajiyar zuciya, sannan ya ce, "Zan yi abin da zan iya."
"Kar ka bari wani abu ya kubuce mana," ta fadi, sannan ta kashe wayar batare da ta jira amsarsa ba.
A wannan lokacin, Alhaji Amiru yana zaune a falo, yana tunanin maganganun da Hajiya Rumanah ta fada masa da daddare. Wani irin matsanancin tunani ya lullube shi.
Me yasa take jin tsoro haka? Me yasa take ta matsawa da jin ko ya samu labari game da Hajiya Zaytunah da yaranta?
Ya dafa goshinsa, yana jin zuciyarsa na bugawa da karfi. Bai taba tunanin cewa wata rana zai fara zargin matarsa ba, amma yanzu yana jin kamar akwai wani abu da take boyewa!
Sai kawai ya dauki wayarsa, ya kira daya daga cikin mutanensa masu SIRRI.
"Baffa, ina bukatar ka bincika min wani abu."
"Ina sauraron ka ranka ya dade..."
"Ina so ka binciko min game da harin da aka kai kwanakin baya... na sace mutanen nan da aka ce sojoji sun ceto."
A dayan bangaren, Baffa ya dan yi shiru, sannan ya ce, "Alhaji, kana nufin garkuwa da mutanen nan? An ce fa an tarwatsa ‘yan fashin gaba daya."
"Eh," Alhaji Amiru ya ce, yana jin yadda zuciyarsa ke tafasa. "Ina so in san wa ke da alhakin wannan aika-aika. Kuma ina so a binciko min wanda ke da hannu a bayan fage."
Baffa ya numfasa. "Zan bincika, Alhaji. Amma fa wannan batu yana da sarkakiya."
"Kawai ka yi min bincike. Ina bukatar cikakken bayani cikin gaggawa."
Ya kashe wayar, sannan ya jingina da kujerarsa. Zuciyarsa na bugawa...
Idan har akwai wanda ya shigo da Hajiya Zaytunah cikin matsala, dole ya gano! Kuma idan har wannan abu yana da alaka da wani daga cikin iyalinsa… to, babu shakka, hakan ba zai wuce ba tare da hukunci ba!
Hajiya Rumanah ta gama fidda umarni, amma zuciyarta har yanzu bata samun nutsuwa. Wata zuciya na gaya mata ta bar komai haka nan, amma tsoron abin da zai iya biyo baya ya hana ta yin watsi da lamarin.