Sashe 7
Kirjin Mai Hankali Part 2 Complete Hausa Novel · about 8 min read
"Wallahi a yanzu haka ma... Babban da na Fawaaz suna can shida matemaka suna iyakar kokarin binciken inda su zaytunah suke. Wallahi tallahi billahi gwaggo bamusan inda su Zaytunah suke ba. Ko suna a raye? Ko akasin haka..Amman inshaa Allahu. Da yardar Allah zamu tsaurara tsananta bincike don gano halin da suke ciki..." Yakarasa yana duban gwaggo Hafsatu. Da tayi murmushi sosai tana dubansa. Don duk a maganganun da yayi babu na karya. Da gaske basusan inda su zaytunah suke ba.. Kuma fawaaz yana bakin kokarinsa shida matemaka suna kokarin gano inda suke...
Duk kuwa da su su Gwaggo zainabu suna magana ne akan tun Zaytunah tana goyan baby Muhammad Wanda yake Hammad a yanzu. Yayinda take rike da Zainab wadda itama karama ce alokacin. A yanzu kuma take Nabeeha. Shekarun baya kenan...
Yayinda su Kuma su major general suna amsa su ne abisa abunda yake faruwa a yanzu. A wannan shekarar da suke ciki.. Major general ya cigaba da cewa,
"Game da batun Nabeeha kuwa, ina mai baku hakuri cewa ba ta nan a halin yanzu. Sun tafi wani shirin makaranta na yawon koyo (excursion) tare da sauran dalibai, kuma suna cikin wani yankin da babu isasshen layin sadarwa. Amma da zarar sun dawo, insha Allah, za mu tabbatar kun hadu da ita domin ku gaisa a zahiri. Idan kuma kuna so, za mu iya shirya wata hira ta wayar tarho ko ta bidiyo da zarar ta samu damar yin hakan, kafin ta dawo gida.
"Ina kara baku hakuri kan wannan jinkiri, kuma muna fatan Allah ya sa a yi komai cikin sauki da alheri. Muna godiya da fahimtar ku da kuma goyon bayan da kuke nunawa a wannan lokaci mai muhimmanci."
Bayan ya kammala wannan jawabi, Major General Dawud ya dauki wayarsa don kiran Nabeeha, Duk kuwa da yasan halin da ake ciki. Wato faduwa tazo dai dai da zama. Nan da nan ya shiga kiran number Nabeeha ya Saka a handsfre.
'The number you're calling is switched off... " Ya sake kira not available.
"Bara na gwada ta sauran yan uwan ta da suka je... " Nanma ya shiga Kiran number Hammad da Hajia Zaytunah. Duka dai zancen daya ne..
"The number you're calling is not available to pick your call at the moment. Dayar number Kuma akace The number youre calling is not reachable at the moment please try again later"
"Kunji ta sauran ma ko? Sun tafi excursion ne. Amma inshaa Allah da zarar sun dawo ko idan an same su a waya. Da yardar Allah"
Ya kara jaddada alkawarin cewa za su tuntube ta da zarar ta samu damar yin hakan, domin ta gaisa da Gwaggo Zainabu da sauran iyalan da suka zo tare.
Bayan Major General Dawud ya bayyana halin da ake ciki game da Nabeeha, Gwaggo Zainabu ta dube shi da murmushi mai cike da jin ƙai, ta ce,
"Alhamdulillah, mun gode ƙwarai da wannan bayani. Mun fahimci cewa Nabeeha tana cikin wani shirin makaranta, kuma muna fatan Allah ya kiyaye ta tare da sauran ɗalibai, ya kuma dawo da su gida lafiya. Muna godiya da yadda kuka nuna kulawa wajen tabbatar da cewa za mu sami damar haɗuwa da ita da zarar ta dawo. Hakan ya nuna mana yadda kuke daraja wannan alaƙa da muke son kafawa.... Sannan mungode kwarai da yadda kuke cigaba da bibiya don tsawaita bincike akan zaytunah da iyalanta. Allah ya Saka da alkhairi yasa mu dache"
Alhaji Uzairu, wanda ke zaune kusa da Gwaggo Zainabu, ya gyara zamansa sannan ya ƙara da cewa,
"Hakika, muna matuƙar godiya da yadda kuka karɓe mu hannu biyu, da kuma yadda kuka saurari buƙatunmu da kulawa. Mun ji daɗin ganin yadda kuke da kyakkyawar zuciya da kuma yadda kuke ɗaukar wannan lamari da muhimmanci. Muna fatan Allah ya sa wannan zama ya zama farkon kyakkyawar alaƙa mai ɗorewa tsakanin iyalanmu."
Gwaggo Zainabu ta sake duban Major General Dawud, ta ce,
"Muna roƙon Allah ya ci gaba da ba ku nasara a aikinku, ya kuma ba ku ƙarfin guiwa wajen ci gaba da hidima ga al'umma. Muna fatan za mu ci gaba da wannan zumunci da muka Kara kullawa a yau, kuma Allah ya sa ya zama alheri ga kowa da kowa."
Alhaji Amiru yana daga gefe yana nazartar komai. Musanman maganganun major general. Sai gaba daya ya rasa madafa ma. Tukukwin maganar data tsaya masa a wuya yana kallon major general da wata fuska ta daban sai yaji komai ya wuce. Ya sauke katuwar ajiyar zuciya..
Bayan Gwaggo Zainabu da Alhaji Uzairu sun nuna godiyarsu ga Major General Dawud, Alhaji Amiru, wanda shi ma ya kasance tare da su, ya gyara zamansa cikin tawali'u, ya dubi Major General Dawud da murmushi, sannan ya fara magana cikin ladabi,
"Assalamu alaikum wa rahmatullahi wa barakatuhu. Hakika, muna matuƙar godiya da yadda kuka karɓe mu hannu biyu, da kulawa da girmamawa. Mun ji daɗin yadda kuka saurari buƙatunmu da kuma yadda kuka nuna ƙwazo wajen taimaka mana, musamman kan batun Zaytunah da 'ya'yanta. Allah ya saka da alheri, ya kuma ƙara muku nasara a aikinku."
Duk da wannan furuci na godiya, a zuciyar Alhaji Amiru akwai ɗan ƙaramin ƙwaƙwƙwafi kan saƙon da aka turo masa a baya. Ya cigaba da tunanin ko wannan saƙo makirci ne ko kuma sharri..
Bayan Alhaji Amiru ya nuna godiyarsa ga Major General Dawud, zuciyarsa ta shiga cikin yanayin tunani mai zurfi. A baya, ya karɓi wani saƙo ta hanyar text message da ya ƙunsa wasu bayanai masu tayar da hankali game da Zaytunah da 'ya'yanta biyu da usulin su
. a Yanzu, bayan jin bayanan da Major General Dawud ya bayar, Alhaji Amiru ya fara tunanin ko wannan saƙo da ya karɓa makirci ne ko kuma sharrin wasu da ke son kawo ruɗani.
Don tabbatar da gaskiyar lamarin, da muhimmancin yin hattara wajen yarda da duk wani saƙo da aka tura masa akan wannan yanayi, Alhaji Amiru sai ya yanke shawarar tambayar Major General Dawud kai tsaye don samun ƙarin bayani kan halin da ake ciki, tare da neman ƙarin haske kan saƙon da ya karɓa. Domin aganinsa hakan zai taimaka masa wajen fahimtar gaskiyar lamarin, da kuma kauce wa yarda da bayanan da ba su da tabbataccen tushe...
Daga nan, suka ci gaba da tattaunawa cikin annashuwa, suna musayar labarai da dariya, tare da ƙara fahimtar juna da gina kyakkyawar alaƙa tsakanin iyalan biyu.
Sai bayan da sukayi sallah suka fara Shirin haramar komawa garin su wato gidah. Gwaggo Hafsatu ta rokesu da su kwana mana..Amman dake sunada abubuwan yi sai suka dan kawo musu nasu uzurin da doriyar zasu dawo inshaa Allah..
Bayan sun firfita harabar gidan ne suna cigaba da magana. Major general shima ya hada tagomashin arziki ya basu. Muhammad dai duk jikinsa yayi sanyi baiji dadi ba. Don idanuwansa basuyi tozali da bugun zuciyar sa ba wato Nabeeha.. Murmushin yake kawai yake amman a zuciyar sa kuka na yake sharara da hawaye..
Bayan tattaunawar da suka yi a gaban kowa, Alhaji Amiru ya sake maimaiata muhimmin batu da yake buƙatar magana ta SIRRI da Major General Dawud. Cikin ladabi, ya nemi izinin yin magana da shi a gefe.
Suna samun wuri mai nisa da sauran jama'a, Alhaji Amiru ya fara da cewa,
"Yallabai, da farko ina so in nemi afuwarka kan wani abu da ya faru. Na karɓi wani saƙo ta text message da private number. Sakonnya ƙunshi wasu bayanai masu tayar da hankali game da Zaytunah da 'ya'yanta biyu. Kan kasan masaniyar inda suke . Sannan Nabeeha ba yar ka bace yar zaytunah ce. A lokacin, na yi zaton cewa dagaske kai ne ka aikata hakan, Ma'ana kanada masaniya akai. Kuma na yi maka zargin da bai dace ba. Amma bayan jin bayaninka a yau, na fahimci cewa wannan saƙo makirci ne da sharri daga wasu masu nufin ɓata. Don haka, ina roƙon ka da ka yafe mini bisa wannan kuskuren da na yi."
Major General Dawud ya dubi Alhaji Amiru da murmushi, Gabansa na tsananta bugawa yana neman afuwar Allah ya ce,
"Alhaji Amiru, babu komai. Kowa na iya yin kuskure, kuma ina godiya da ka zo ka bayyana min wannan. Na yafe maka daga zuciyata, Ina Kuma fatan ka yafemun kai ma. Dagaske Nabeeha 'yar 'yar uwata ce. A hannuna take tun tana karama..ni ne tamkar mahaifin ta. Tare suka tashi da yayan wajena. Kamar yadda bansan masaniya akan Muhammad ba dan wajen chief judge bane sai daga baya, Duk munyi kuskure. Ina fatan zaka yafemun kai ma, kuma mu ci gaba da haɗin kai wajen ganin an gano Zaytunah da 'ya'yanta."
Alhaji Amiru ya numfasa da sauƙi, sannan ya ƙara da cewa,
"Mashaa Allah! Wannan batu haka yake, Na gode ƙwarai, Yallabai. Haka zalika, muna matuƙar godiya da yadda ka amince da buƙatar ɗanmu Muhammad ya auri 'yarka Nabeeha.. Ai da na kowa ne. Don haka da Kai da kaya duk mallakar wuya ne. Yar yar uwarka yar ka ce. Mashaa Allah! Muhammd Kuma har Sako na turo nima akan hakan inaga baka gani ba matsalar network.. Muna fatan Allah ya sa wannan haɗin ya zama alheri ga iyalanmu baki ɗaya."
Major General Dawud ya amsa da cewa,
"Zahiri kam. Network. Ai komai ya wuce. Abdulfatah amini nane. Kowa wani ya kawo na daban yace ya bawa ya ta zan aminta bare dan wajen ka.. Allah yasa mu dache, Muna fatan Allah ya sa a yi komai cikin nasara da farin ciki."
Daga nan, suka koma cikin taron tare, zuciyoyinsu cike da farin ciki da kuma kyakkyawar fahimta...
Su gwaggo zainabu suka shisshiga mota.. motocin su suka fita daga gidan zukatan su cike da farin cikin wannan rana mai tarin dimbin alkhairi..
Hajia Hauwa ta ciji yatsa ... Bataso haakn ta faru ba. Taso sun tabbatar sa su Zaytunah suna gidan. Amman ta ya ya? Bayan anyi garkuwa da su. Ta numfasa tana adduar Allah ya watsa komai su zaytunah su tattara su tafi. Idan kuma rai yayi halinsa ma shikenan.
Yayinda gwaggo Hafsatu ta major general suka sauke numfashi mai tattare da hamdalar yadda komai ya kasance a tsare. Suka koma godewa Allah da ba abunda ya taso na tashin hankali. Major general ya sanarwa mahaifiyar sa gwaggo Hafsatu yadda sukayi da Alhaji Amiru...
Duk kuwa da su su Gwaggo zainabu suna magana ne akan tun Zaytunah tana goyan baby Muhammad Wanda yake Hammad a yanzu. Yayinda take rike da Zainab wadda itama karama ce alokacin. A yanzu kuma take Nabeeha. Shekarun baya kenan...
Yayinda su Kuma su major general suna amsa su ne abisa abunda yake faruwa a yanzu. A wannan shekarar da suke ciki.. Major general ya cigaba da cewa,
"Game da batun Nabeeha kuwa, ina mai baku hakuri cewa ba ta nan a halin yanzu. Sun tafi wani shirin makaranta na yawon koyo (excursion) tare da sauran dalibai, kuma suna cikin wani yankin da babu isasshen layin sadarwa. Amma da zarar sun dawo, insha Allah, za mu tabbatar kun hadu da ita domin ku gaisa a zahiri. Idan kuma kuna so, za mu iya shirya wata hira ta wayar tarho ko ta bidiyo da zarar ta samu damar yin hakan, kafin ta dawo gida.
"Ina kara baku hakuri kan wannan jinkiri, kuma muna fatan Allah ya sa a yi komai cikin sauki da alheri. Muna godiya da fahimtar ku da kuma goyon bayan da kuke nunawa a wannan lokaci mai muhimmanci."
Bayan ya kammala wannan jawabi, Major General Dawud ya dauki wayarsa don kiran Nabeeha, Duk kuwa da yasan halin da ake ciki. Wato faduwa tazo dai dai da zama. Nan da nan ya shiga kiran number Nabeeha ya Saka a handsfre.
'The number you're calling is switched off... " Ya sake kira not available.
"Bara na gwada ta sauran yan uwan ta da suka je... " Nanma ya shiga Kiran number Hammad da Hajia Zaytunah. Duka dai zancen daya ne..
"The number you're calling is not available to pick your call at the moment. Dayar number Kuma akace The number youre calling is not reachable at the moment please try again later"
"Kunji ta sauran ma ko? Sun tafi excursion ne. Amma inshaa Allah da zarar sun dawo ko idan an same su a waya. Da yardar Allah"
Ya kara jaddada alkawarin cewa za su tuntube ta da zarar ta samu damar yin hakan, domin ta gaisa da Gwaggo Zainabu da sauran iyalan da suka zo tare.
Bayan Major General Dawud ya bayyana halin da ake ciki game da Nabeeha, Gwaggo Zainabu ta dube shi da murmushi mai cike da jin ƙai, ta ce,
"Alhamdulillah, mun gode ƙwarai da wannan bayani. Mun fahimci cewa Nabeeha tana cikin wani shirin makaranta, kuma muna fatan Allah ya kiyaye ta tare da sauran ɗalibai, ya kuma dawo da su gida lafiya. Muna godiya da yadda kuka nuna kulawa wajen tabbatar da cewa za mu sami damar haɗuwa da ita da zarar ta dawo. Hakan ya nuna mana yadda kuke daraja wannan alaƙa da muke son kafawa.... Sannan mungode kwarai da yadda kuke cigaba da bibiya don tsawaita bincike akan zaytunah da iyalanta. Allah ya Saka da alkhairi yasa mu dache"
Alhaji Uzairu, wanda ke zaune kusa da Gwaggo Zainabu, ya gyara zamansa sannan ya ƙara da cewa,
"Hakika, muna matuƙar godiya da yadda kuka karɓe mu hannu biyu, da kuma yadda kuka saurari buƙatunmu da kulawa. Mun ji daɗin ganin yadda kuke da kyakkyawar zuciya da kuma yadda kuke ɗaukar wannan lamari da muhimmanci. Muna fatan Allah ya sa wannan zama ya zama farkon kyakkyawar alaƙa mai ɗorewa tsakanin iyalanmu."
Gwaggo Zainabu ta sake duban Major General Dawud, ta ce,
"Muna roƙon Allah ya ci gaba da ba ku nasara a aikinku, ya kuma ba ku ƙarfin guiwa wajen ci gaba da hidima ga al'umma. Muna fatan za mu ci gaba da wannan zumunci da muka Kara kullawa a yau, kuma Allah ya sa ya zama alheri ga kowa da kowa."
Alhaji Amiru yana daga gefe yana nazartar komai. Musanman maganganun major general. Sai gaba daya ya rasa madafa ma. Tukukwin maganar data tsaya masa a wuya yana kallon major general da wata fuska ta daban sai yaji komai ya wuce. Ya sauke katuwar ajiyar zuciya..
Bayan Gwaggo Zainabu da Alhaji Uzairu sun nuna godiyarsu ga Major General Dawud, Alhaji Amiru, wanda shi ma ya kasance tare da su, ya gyara zamansa cikin tawali'u, ya dubi Major General Dawud da murmushi, sannan ya fara magana cikin ladabi,
"Assalamu alaikum wa rahmatullahi wa barakatuhu. Hakika, muna matuƙar godiya da yadda kuka karɓe mu hannu biyu, da kulawa da girmamawa. Mun ji daɗin yadda kuka saurari buƙatunmu da kuma yadda kuka nuna ƙwazo wajen taimaka mana, musamman kan batun Zaytunah da 'ya'yanta. Allah ya saka da alheri, ya kuma ƙara muku nasara a aikinku."
Duk da wannan furuci na godiya, a zuciyar Alhaji Amiru akwai ɗan ƙaramin ƙwaƙwƙwafi kan saƙon da aka turo masa a baya. Ya cigaba da tunanin ko wannan saƙo makirci ne ko kuma sharri..
Bayan Alhaji Amiru ya nuna godiyarsa ga Major General Dawud, zuciyarsa ta shiga cikin yanayin tunani mai zurfi. A baya, ya karɓi wani saƙo ta hanyar text message da ya ƙunsa wasu bayanai masu tayar da hankali game da Zaytunah da 'ya'yanta biyu da usulin su
. a Yanzu, bayan jin bayanan da Major General Dawud ya bayar, Alhaji Amiru ya fara tunanin ko wannan saƙo da ya karɓa makirci ne ko kuma sharrin wasu da ke son kawo ruɗani.
Don tabbatar da gaskiyar lamarin, da muhimmancin yin hattara wajen yarda da duk wani saƙo da aka tura masa akan wannan yanayi, Alhaji Amiru sai ya yanke shawarar tambayar Major General Dawud kai tsaye don samun ƙarin bayani kan halin da ake ciki, tare da neman ƙarin haske kan saƙon da ya karɓa. Domin aganinsa hakan zai taimaka masa wajen fahimtar gaskiyar lamarin, da kuma kauce wa yarda da bayanan da ba su da tabbataccen tushe...
Daga nan, suka ci gaba da tattaunawa cikin annashuwa, suna musayar labarai da dariya, tare da ƙara fahimtar juna da gina kyakkyawar alaƙa tsakanin iyalan biyu.
Sai bayan da sukayi sallah suka fara Shirin haramar komawa garin su wato gidah. Gwaggo Hafsatu ta rokesu da su kwana mana..Amman dake sunada abubuwan yi sai suka dan kawo musu nasu uzurin da doriyar zasu dawo inshaa Allah..
Bayan sun firfita harabar gidan ne suna cigaba da magana. Major general shima ya hada tagomashin arziki ya basu. Muhammad dai duk jikinsa yayi sanyi baiji dadi ba. Don idanuwansa basuyi tozali da bugun zuciyar sa ba wato Nabeeha.. Murmushin yake kawai yake amman a zuciyar sa kuka na yake sharara da hawaye..
Bayan tattaunawar da suka yi a gaban kowa, Alhaji Amiru ya sake maimaiata muhimmin batu da yake buƙatar magana ta SIRRI da Major General Dawud. Cikin ladabi, ya nemi izinin yin magana da shi a gefe.
Suna samun wuri mai nisa da sauran jama'a, Alhaji Amiru ya fara da cewa,
"Yallabai, da farko ina so in nemi afuwarka kan wani abu da ya faru. Na karɓi wani saƙo ta text message da private number. Sakonnya ƙunshi wasu bayanai masu tayar da hankali game da Zaytunah da 'ya'yanta biyu. Kan kasan masaniyar inda suke . Sannan Nabeeha ba yar ka bace yar zaytunah ce. A lokacin, na yi zaton cewa dagaske kai ne ka aikata hakan, Ma'ana kanada masaniya akai. Kuma na yi maka zargin da bai dace ba. Amma bayan jin bayaninka a yau, na fahimci cewa wannan saƙo makirci ne da sharri daga wasu masu nufin ɓata. Don haka, ina roƙon ka da ka yafe mini bisa wannan kuskuren da na yi."
Major General Dawud ya dubi Alhaji Amiru da murmushi, Gabansa na tsananta bugawa yana neman afuwar Allah ya ce,
"Alhaji Amiru, babu komai. Kowa na iya yin kuskure, kuma ina godiya da ka zo ka bayyana min wannan. Na yafe maka daga zuciyata, Ina Kuma fatan ka yafemun kai ma. Dagaske Nabeeha 'yar 'yar uwata ce. A hannuna take tun tana karama..ni ne tamkar mahaifin ta. Tare suka tashi da yayan wajena. Kamar yadda bansan masaniya akan Muhammad ba dan wajen chief judge bane sai daga baya, Duk munyi kuskure. Ina fatan zaka yafemun kai ma, kuma mu ci gaba da haɗin kai wajen ganin an gano Zaytunah da 'ya'yanta."
Alhaji Amiru ya numfasa da sauƙi, sannan ya ƙara da cewa,
"Mashaa Allah! Wannan batu haka yake, Na gode ƙwarai, Yallabai. Haka zalika, muna matuƙar godiya da yadda ka amince da buƙatar ɗanmu Muhammad ya auri 'yarka Nabeeha.. Ai da na kowa ne. Don haka da Kai da kaya duk mallakar wuya ne. Yar yar uwarka yar ka ce. Mashaa Allah! Muhammd Kuma har Sako na turo nima akan hakan inaga baka gani ba matsalar network.. Muna fatan Allah ya sa wannan haɗin ya zama alheri ga iyalanmu baki ɗaya."
Major General Dawud ya amsa da cewa,
"Zahiri kam. Network. Ai komai ya wuce. Abdulfatah amini nane. Kowa wani ya kawo na daban yace ya bawa ya ta zan aminta bare dan wajen ka.. Allah yasa mu dache, Muna fatan Allah ya sa a yi komai cikin nasara da farin ciki."
Daga nan, suka koma cikin taron tare, zuciyoyinsu cike da farin ciki da kuma kyakkyawar fahimta...
Su gwaggo zainabu suka shisshiga mota.. motocin su suka fita daga gidan zukatan su cike da farin cikin wannan rana mai tarin dimbin alkhairi..
Hajia Hauwa ta ciji yatsa ... Bataso haakn ta faru ba. Taso sun tabbatar sa su Zaytunah suna gidan. Amman ta ya ya? Bayan anyi garkuwa da su. Ta numfasa tana adduar Allah ya watsa komai su zaytunah su tattara su tafi. Idan kuma rai yayi halinsa ma shikenan.
Yayinda gwaggo Hafsatu ta major general suka sauke numfashi mai tattare da hamdalar yadda komai ya kasance a tsare. Suka koma godewa Allah da ba abunda ya taso na tashin hankali. Major general ya sanarwa mahaifiyar sa gwaggo Hafsatu yadda sukayi da Alhaji Amiru...