← Book details Kirjin Mai Hankali Part 2 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 22 OF 75

Sashe 22

Kirjin Mai Hankali Part 2 Complete Hausa Novel · about 8 min read

An fara da gwaje-gwaje na cikakken lafiya. An duba Hajia Zaytunah sosai, aka tabbatar babu wata matsala babba, sai dai radadin da ta ke ji a wurin da aka yanke mata gashin kanta. Don haka, likitocin suka yi mata karin ruwa don karfafa jikinta, sannan suka bata magungunan rage radadi.

Nabeeha da Hammad suma an yi musu gwaje-gwaje, aka tabbatar da cewa suna cikin koshin lafiya. Sai dai an musu allurori na kariya da magungunan antibiotics don hana kamuwa da wata cuta sakamakon wahalar da suka sha.

Gwaggo Hafsatu ta cigaba da nuna damuwarta har sai da likita ya tabbatar mata da cewa babu wata matsala.

Bayan an kammala komai, suka fito daga asibitin, kowa cikin kwanciyar hankali da godiya ga Allah. A cikin motocin da ke tafiya a nutsuwa, ana jin saukar zuciya a tare da kowa.

A zuciyar kowa, sun san cewa rayuwa za ta cigaba, kuma a wannan lokaci, sun san cewa akwai sabuwar fata da sabuwar soyayya da ke ci gaba da bayyana a zuciyoyinsu.

Duk da SIRRIN da ke tsakaninsu, akwai haske a gaban su.

Da zarar da motocinsu suka iso gida daga asibiti, sabuwar rayuwa ta soma fantsama cikin zuciyar kowa. Daga yanayin yadda Gwaggo Hafsatu ta sake rungume Hajia Zaytunah a lokacin da suka fito daga mota, har zuwa murmushin da ke fuskarta, ya nuna yadda take jin daɗin dawowarta gida cikin kwanciyar hankali.

"A yanzu, sai dai mu gode wa Allah," Gwaggo Hafsatu ta furta, tana kallon su Nabeeha da ke gefenta. "Kun ga, kowa ya dawo gida lafiya."

Wannan kalma ta sa Hammad ya saki murmushi yana jin wani irin nutsuwa yana ratsa shi. Duk wahalar da suka sha, sun samu nasarar komawa cikin iyalansu.

Nabeeha kuwa tana gefen mahaifiyarta, tana ta duba ta da kulawa. Tun daga asibiti har zuwa gida, ba ta dena tambayarta yadda take ji ba.

Fawaaz kuwa daga gefe yake, kamar kullum, yana kallon komai cikin nutsuwa da kamun kai. Bai ce komai ba, amma idanunsa sun nuna yadda zuciyarsa ke jin daɗin ganin kowa cikin farin ciki.

Da suka shiga falon, an sake jin daɗi a zuciyar kowa. Wurin ya cika da haske da kamshin turaren gida na kamfanin YERWA INCENSE AND MORE.. A gefen babban falon, manyan kujeru ne masu taushi da sanyin fata, suna ba da kwanciyar hankali ga wanda ya zauna a kansu.

Masu aiki sun taru suna murna, kowannensu na nuna farin ciki. Sun shirya kayan marmari da shayi mai zafi, don su samu nutsuwa bayan dawowarsu daga tafiya.

Daga nesa, motsin shigowar Major General Dawud. Da alama ya dade yana jiransu su dawo, saboda yana sanye da kaya masu sauki fiye da na jikinsa dazu, yana nuna cewa ya fi mayar da hankali ga tarbarsu a yau fiye da komai.

Da ya karaso, idanunsa suka fara sauka kan mahaifiyarsa. Daga nan sai ya dubi Hajia Zaytunah, wadda ke zaune kusa da 'ya'yanta. Kallon da ya yi mata ya nuna cewa yana jin tausayinta, amma ya fi jin daɗin ganin ta cikin koshin lafiya.

Ya numfasa kadan, sannan ya kalli su gaba ɗaya. "Mun gode wa Allah. Dukkanin ku kun sha wahala, amma Allah ya kawo mana sauki."

Hajia Zaytunah ta gyaɗa kai cikin jin daɗi. "Allah ya bar zumunci."

Gwaggo Hafsatu ta yi murmushi tana duban ɗanta. "Dawuda, zan sake cewa, mun gode maka. Kai da Fawaaz, da dukkan sojojin da suka bada gudunmawa wajen kubutar da yaran nan da mahaifiyarsu."

Ya girgiza kai cikin girmamawa. "Gwaggo na.., wannan aikina ne. Kuma na san duk wanda ke cikin wannan gida zai yi hakan idan da dama ta samu... Sannan sauran yan fashin da aka kama su da yardar Allah zamubi diddigin gano Wanda yasa suka aikata wannan abu. Sannan zamu hora su sosai zasu sha dukan sojoji sannan zamu dauki tsattsauran mataki akan su inn shaa' Allah"

Fawaaz ya gyada kai kadan. Duk da cewa bai fiye magana ba, yana jin irin godiyar da kowa ke yi a ransa.

🎀🎀

Bayan wannan rana, gidansu ya cika da kwanciyar hankali da farin ciki. Duk da cewa akwai abubuwan da ba a gama fahimtarsu ba, amma babu shakka, sun shiga wani sabon mataki na rayuwa. Daga bangaren Fawaaz kuwa, da sauran sojoji karkashin Dawud Mafia suna ci gaba da aiki don tabbatar da cewa babu wata barazana da ka iya sake samun su.

A gefe guda kuwa, akwai sabbin soyayyar da ke tasowa a hankali. Duk da cewa Fawaaz bai taɓa furta wani abu ba, amma yadda yake kulawa da Nabeeha ba boyayyen abu ba ne. A wasu lokuta, idan Nabeeha ta tashi daga zaune, idanunsa kan bita har ta fita daga falo. Idan kuma tana kusa da mahaifiyarta, yana lura da yadda take yi mata kulawa da so.

A ranar da Gwaggo Hafsatu ta lura da hakan, sai ta saki murmushi tana gyara zaninta. Ta kalli Nabeeha da ke gefen mahaifiyarta sannan ta kalli Fawaaz.

"Allah ya shiga cikin lamuran mu. Ya zaba mana abunda yafi alkhairi ," ta furta a hankali, tana jin cewa lokaci ne kawai zai nuna yadda za a shirya kaddarar da ke tafe.

_1-KALBIM:MAMUH GEE_

_2-KIRJIN MAI HANKALI (AKWATIN SIRRIN SA):MSS XOXO_

_3-ADUNIYATAH :HUGUMAH_

_4-AJIYA A DUHU: BILYN ABDULL_
°°
_1-BOOK DAYA:DARI BIYAR_

_2-BOOKS BIYU:DUBU DAYA_

_3-BOOKS UKU: DUBU DAYA DA DARI BIYAR_

_4-BOOKS HUDU :DUBU BIYU_

_5_YAN NIJAR: 1000CF: 89825722 NOUSAIBA LAWALI MARADI_
_ku tura receipt zuwa ga 09033181070_

*IDAN KATI NE A TURO TA WANNAN NUMBER:*

*09032345899.. SHEDAR KATIN MA NAN ZAA TURA. KATIN MTN!!MTN!!*
____
**
*KIRJIN MAI HANKALI*
_(Akwatin sirrin sa)_
_🧳👩‍❤️‍👨🌺_

*_The Vault Of His Secrets_*

_®️NANA HAFSATU (MX)_

_©️ZAFAFA BIYAR WRITERS_

*_BOOK TWO_*

_PAGE: 18_

Koda suka koma gidan su bayan sun bar gidan alhaji Uzairu , Hajiya Rumanah ta ajiye hijabinta sannan ta nufi sashen Alhaji Amiru. A tsaye ta tarar da shi a kan sallaya, yana karanta azkar cikin nutsuwa. Ta dan tsaya daga nesa tana kallonsa, sannan ta nisa da kyau kafin ta karasa kusa da shi.

"Alhaji," ta kira shi da wata murya mai rauni.

Ya dago ya dubeta, ba tare da ya ce komai ba. Sai da ta sunkuya ta zauna a gefen kujerar dake sashen nasa, sannan ta ci gaba da magana cikin kissa da kisisina.

"Gabana yana ta tsananta bugawa. Har yanzu ba mu da wani bayani a kan Hajiya Zaytunah da yaranta?"

Ta dan yi shiru kadan, tana nazarin fuskarsa. Alhaji Amiru ya ajiye tesbihinsa, yana me gyara zamansa. Fuskar nan tasa da ba a cika fassara ainihin abinda ke cikinta ba, ya dauki lokaci kafin ya dago ya kalleta.

"Me ya sa kike tambayar hakan a yanzu, eh rumanah?" Ya tambaya cikin yanayi mai cike da taka tsantsan.

Hajiya Rumanah ta dan gyara zama, tana wasa da zoben hannunta.

"Alhaji, shekara da shekaru muka dauka ba tare da sanin inda suka shiga ba. Kuma kai da kanka ka ce a lokacin ba sai mun ci gaba da bincike ba. Amma yanzu... yanzu abubuwa sun fara daure min kai. Ba ka ganin lokaci yayi da ya kamata mu san halin da suke ciki?"

Alhaji Amiru ya zuba mata ido, yana nazarin ta da kyau. A fili yana jin tsananin nauyin wannan tambaya, domin kuwa akwai SIRRIN da bai son ya bude.

Ya daure fuska, sannan ya ce cikin kakkausar murya,

"Rumanah, ki daina yawo da tunani mara amfani. Idan lokaci yayi, Allah zai bayyana komai."

Hajiya Rumanah ta runtse idanu, tana jin wani yanayi na takaici yana ratsa zuciyarta. A ranta, ta san akwai wani abu da Alhaji Amiru bai fada mata ba, amma ba ta da ikon matsa masa don jin ainihin gaskiyar lamarin.

Bayan Hajiya Rumanah ta tashi ta bar sashen nasa, Alhaji Amiru ya jingina da kujerarsa, yana kallon sararin dakin kamar mai neman amsar wata tambaya. Ya lumshe idanu, yana jin nauyin tunanin da maganganunta suka jefa shi ciki.

"Har yanzu ba mu da labarin Hajiya Zaytunah da 'ya'yanta?"

Wannan tambaya tana da nauyi a zuciyarsa. Tun kafin ta tambaye shi, wannan batu yana damunsa, amma yana kokarin rufe shi da tunanin cewa lokaci ne kawai bai kai ba. Amma me yasa Hajiya Rumanah ta kawo maganar yanzu? Shin tana jin wani abu ne?

Ya sauke ajiyar zuciya. Idan har za a waiwaya baya, babu shakka, Hajiya Zaytunah da 'ya'yanta sun bace a duniya kamar ba su taɓa wanzuwa ba. Bai taba ganin wata alama da ke nuna inda suka shiga ba, kuma babu wanda ya taba kawo musu wata kwakkwarar magana a kansu. Amma zuciyarsa tana tsananta bugawa a duk lokacin da aka ambaci sunanta.

A wani bangaren zuciyarsa, yana jin wani mugun nauyi. Yana sane da irin matsin da Zaytunah ta shiga kafin tafiyarta. Yana sane da halin da ta bar gidan kanin nasa a ciki, da irin yadda abubuwa suka rikice mata. Amma ko da yake, hakan ba ya nufin yana son ci gaba da wannan bincike da Hajiya Rumanah ke kokarin tunzura shi akai.

Ya dafe goshinsa, yana jin wani iri. Idan har Zaytunah tana raye, ina take? Shin tana can tana rayuwa cikin kunci da wahala, ko kuwa lokaci ne kawai ya jefa ta cikin duhun da babu mai iya ganinta? Kuma idan har tana raye, shin za ta taba yafe musu abin da ya faru?

Ya gyara zamansa, zuciyarsa na sake nauyaya. Idan da akwai wani abu daya ke tsoro a rayuwarsa, to yana tsoron wani lokaci ya zo da ahalin zasu fuskanci Zaytunah. Ya san idan hakan ta faru, ba zai iya boye duk wata damuwarsa ba.

🎀🎀🎀🎀

A tsakar dare, dakin Hajiya Rumanah ya dauki shiru, sai karan AC da ke busa iska a hankali. Ta juyi a kan gadonta, zuciyarta cike da damuwa, amma har yanzu barci ya gagara daukarta.

Wayarta ta fara vibration, sai karar shigowar kira ta ratsa cikin dakin. A firgice ta bude idanu, zuciyarta na harbawa da sauri kamar mai shirin tsallake KIRJIN ta. Ta kai hannu ta dauki wayar daga gefen filo, ba tare da ta duba sunan mai kiran ba, ta amsa cikin murya mai sanyi, kamar wadda aka taso daga mafarki.

"Waye?" Ta tambaya, muryarta na nuna alamun rashin kwanciyar hankali.
Chapter 22 · 0% Book details