Sashe 32
Kirjin Mai Hankali Part 2 Complete Hausa Novel · about 8 min read
A bangaren Ammi kuwa, tana cikin falonta tana tunanin irin kallon da Nabeeha ke yi mata tun jiya. Duk da cewa ta gama shari’ar da kanta cewa Nabeeha za ta dauki lokaci kafin ta gama karbar gaskiya, ta san cewa yarinyar nan tana da son sanin hakikanin gaskiya.
A ranar, tana zaune tare da Gwaggo Hafsatu a dakin. Bayan dogon shiru, sai Gwaggo Hafsatu ta kalle ta.
“Zaytunah, ya kamata ki shirya kanki.”
Hajiya Zaytunah ta dago ido. “Meye hakan ke nufi, Gwaggo?”
Gwaggo Hafsatu ta dan ja dogon numfashi. “Nabeeha za ta iya tunkarar mahaifinta da kanta. Idan har hakan ta faru, ba zai kasance da sauki ba.”
Hajiya Zaytunah ta dafe kanta. “Gwaggo, har yanzu ban shirya fuskantar sa ba. Ban shirya fuskantar dukkan su ba.”
Gwaggo Hafsatu ta kalli Zaytunah da kulawa. “Dole ne ki shirya. Idan har Nabeeha ta tunkare shi da kanta, ba zai kasance da sauki gare ki ba. Idan har gaskiya ta fito, ba za ki so a same ki cikin rashin shiri ba.”
Shiru ya ratsa dakin. Hajiya Zaytunah ta san cewa Gwaggo Hafsatu na da gaskiya, amma har yanzu zuciyarta tana tafasa da fargaba.
---
A ranar, da yamma, Nabeeha ta tsaya gaban madubi tana kallon kanta. Idanunta sun cike da damuwa, zuciyarta tana bugawa da sauri. .
MX
*KIRJIN MAI HANKALI*
_(AKWATIN SIRRIN SA)_
🧳➿💞
*PG :28*
*AREWABOOKS VVIP:👇*
https://www.arewabooks.com/book?id=670bd07e35879b101764c0eb
×××Alhaji Uzairu ya ja dogon numfashi a daya bangaren wayar, yana jin yadda zuciyarsa ke bugawa da sauri.
"Nabeeha, menene wannan magana?"
Nabeeha ta rufe idonta da karfi, zuciyarta tana tsananta bugawa. Wannan shi ne lokaci mafi wahala da ta taba fuskanta.
"Abba na,Ashe inada rabon ganawa da ku a doron duniyar nan? Ashe muma munada mahaifi da yake a raye kamar su Humayrah? zan zo wajenka in gaya maka da kaina abba," ta fada a hankali.
Shiru ya ratsa tsakanin su na tsawon dakika goma. Sannan sai Alhaji Uzairu ya furta,
"Eh mana diyar albarka, wannan batu haka yake. To shikenan, ina jiranki."
Nabeeha ta kashe wayar, sannan ta dafe KIRJIN ta. Har yanzu, zuciyarta ba ta dai-daita ba. Shin ta yanke shawarar da ta dace? Shin hakan ba zai jefa Ammi cikin matsala ba?
Firgigit tajiyo karar sautin maganar Hammad ya shigo dakin yana kallonta.
"Me kike yi haka?"
Na beeha ta dago ido, tana jin yadda jikinta ya yi sanyi.ashe mafarki take yi?
"Na kira Abba. Zan je in gaya masa komai."
Hammad ya runtse ido yana girgiza kai.
"Wane Abba kuma dear sis? Me zaki fada masa? Mafarki kike ne?"
Nabeeha ta numfasa tana sauke katuwar ajiyar zuciya tace,
"Ina jin tsoron ci gaba da rayuwa cikin wannan duhun, Hammad" ta fada da shesshekar kuka.
"Ya kamata mu waiwaya dangin mahaifin mu. Tabbas ammi taga rayuwa tana kuma cikin jarabawar wannan kaddarori da taketa fuskanta..!"
Hammad ya dafe kansa, yana jin tsantsar tashin hankali. Bai san me zai ce ba, domin yasan cewa komai ya kusa fashewa.
"Inshaa Allah khair... Dear sis.... Kowani tsanani yanatare da sauki. Da yardar Allah lokacin warwarar komai ne yazo gangara..."
"Allah ya amince"
"Aameen"
🎀🎀🎀🎀
Cikin sanyin jiki da girmamawa, Gwaggo Hafsatu ta dubi fuskokin dake gabanta. Babban parlorn nata ya cika da nutsuwa, sai murmushin hikima dake kwance a gefen lebenta. Kowa ya zauna bisa kujera, duk da a kasa suka fara zama dukansu gwaggon taki kememe kan kowa ya koma kan kujera saboda sanyin ac dake busawa ko'ina na marbles din ya dauka da sanyi...
amma babu wanda ya iya fadin uffan. Fuskokin su Nabeeha da Hammad cike suke da tambayoyi, yayin da Hajiya Zaytunah ke daure fuska, tana kokarin kwantar da hankali.
A gefen dama Major General Dawud ne, yana zaune da kamewa. Kamar kullum, dattako ya rufe fuskarsa, sai idanunsa da ke bin komai a parlorn da kulawa. Hajiya Zaytunah na kusa da Gwaggo Hafsatu, tana dafe da mayafinta kamar mai jin sanyi. Nabeeha da Hammad kuwa, suna gefenta suna jiran jin abin da zai fito daga bakin Gwaggo Hafsatu.
Gwaggo Hafsatu ta numfasa a hankali, sannan ta dube su duka.
"Nasan kun dade kuna tunanin wanene ku, daga inda kuka fito. Lokaci yayi da ya kamata ku san asalin usulin ku," ta fara magana cikin muryarta mai nutsuwa.
Ta kalli Nabeeha da Hammad kai tsaye.
"Mahafiyarku, Hajiya Zaytunah, 'yar gidan kirki ce. Ta taso cikin jin dadi da kulawa, amma hakan bai hana rayuwa tura mata jarabawarta ba. Kafin a haife ku, ta yi aure da mutum mai tarin nutsuwa da hikima, sunansa Alhaji Uzairu Muhammad, mijin ta na sunnah. Shi da yayansa, Alhaji Amiru Muhammad, su ne suka gaji dukiyar gidan su. Sai dai fa wannan aure bai kasance cikin kwanciyar hankali ba, domin kishiyoyinta biyu, Hajiya Ladi da Hajiya Karama, sun mayar da ita kamar baiwar da ta shigo gidan da kafafunta."
Gwaggo Hafsatu ta dan ja numfashi. "Hajiya Ladi da Hajiya Karama sun yi iyakar bakin kokarinsu wajen ganin cewa mahaifiyarku ba ta sami kwanciyar hankali a gidan ba. Sun hada baki da wata uwa 'yar uwarta, Hajiya Rumanah, wadda ke da tsantsar tsana da kyashi gare ta tun suna yara. Hajiya Rumanah ba wai kishiyar mahaifiyarku bace da dai da ita zaa daura auren ta da Alhaji uzairu sai Allah yayi ikon sa aka daura aurenta da Alhaji Amiru.Wato yayan mahaifinku."
Gwaggo Hafsatu ta girgiza kai, sannan ta cigaba,
"Bayan mahaifiyarku ta haifi Nabeeha, ke kenan .. sannan ta dauki ciki na biyu,wanda ke cikinta shine kai, Hammad, aka shirya wata mummunar makarkashiya. Asiri aka mata! An hada baki da bokaye, aka tsara makircin da zai sa mahaifiyarku ta bar gidan ba tare da tunanin dawowa ba. Kuma hakan ya faru."
Nabeeha ta saki numfashi, tana kallon mahaifiyarta da idanun da suka cicciko da kwalla.
"Ammi, me yasa kika bar gidanmu? Me yasa baki koma ba?"
Hajiya Zaytunah ta rintse ido, ta dafa hannun Nabeeha.
"Ba zan iya komawa ba, Nabeeha. Na rasa komai. Ba ni da mafita, kuma a lokacin, Hajiya Ladi da Hajiya Karama sun makantar da Alhaji Uzairu da zargin karya akaina. Na san idan na tsaya, da za a kashe ni ko kuma na rasa hankalina."
Hammad ya dafa hannun mahaifiyarsa. "Ammi, na fahimta. Amma me yasa sai yanzu ake sanar mana?"
Gwaggo Hafsatu ta gyara zamanta.
"Saboda lokaci yayi. Har yanzu ana neman mahaifiyarku. Duk wanda ya mata wannan asiri, ba ya so ta dawo cikin iyalinta. Sai dai hakan ba zai canza gaskiyar lamarin ba."
Nabeeha ta runtse ido, zuciyarta cike da mamaki. Hammad kuma ya dafe goshinsa. Amma abu mafi tayar musu da hankali shine kalmomin da Gwaggo Hafsatu ta kara fadi,
"Sai Muhammad manemin ki Nabeeha, Da ne ga Alhaji amiru. Wato dan gidan hajia rumanah. Hajia rumanah Kuma da mahaifin ta da mahaifin mahaifiyar ku uwar su daya uban su daya, sannan rana daya aka haifi hajia rumanah da hajiya Zaytunah... atakaice dai Muhammad Hammad dan Alhaji Amiru Muhammad ne dan yayan mahaifin ku Alhaji uzairu!"
Wani mugun shock ya saukarwa Hammad da Nabeeha. Idanunsa suka firfito, yana kallon su duka.
"Dan Hajiya Rumanah ne?"suka hada baki wajen tambaya idanuwan su sun furfuto waje cike da mamaki ..
Gwaggo Hafsatu ta gyada kai.
"Eh, dan Alhaji Amiru da Hajiya Rumanah ne. "
Wani irin nauyi ya saukarwa Hammad da Nabeeha. Don Nabeeha kuwa, numfashinta ya fara hawa da sauka. ..
Major general dawud mafia yana daga gefen da yake zaune yana hankalce da komai gefe daya dinbin mamaki da sanyin jiki sun dabaibaye shi... Yana tausayin su sosai .
"To yanzu me zai faru?" Hammad ya tambaya, yana kokarin daidaita kansa.
Gwaggo Hafsatu ta dube shi da kulawa.
"Atakaice dai mahaifiyarku Hajiya Zaytunah tana son ku. Ta yarda da kaddara, kuma tana rokon Allah ya bayyana gaskiya. Abin da ya fi shine ku cigaba da rayuwar ku da hakuri da biyayya."
A wannan lokaci, dakin yayi shiru. Idanun Nabeeha da Hammad sun cika da kwalla, zuciyoyinsu suna cike da rudani. Rayuwarsu ta canza a cikin dare daya. Sun san iyayensu, sun san asalin su. Kuma sun san cewa komai da suka sani a baya—ya canza...
MX🧕
*KIRJIN MAI HANKALI*
_(AKWATIN SIRRIN SA)_
🧳➿💞
*PG :29*
*AREWABOOKS VVIP:👇*
https://www.arewabooks.com/book?id=670bd07e35879b101764c0eb
Tashin motar Fawaaz kadai ke karan kunne a kofar gidan Major General Dawud. Baba . Wato Major general dawud ne yace ya dauki nabeeha ya kaita workshop din da sukeyi na wani course na su na makaranta. Yana jingine da kujerar motar, hannayensa rike da sitiyari, yayin da zuciyarsa ke tafasa da tunanin wacce zai dauka a yau....
Nabeeha.
Ya lumshe ido a hankali, yana jin bugun zuciyarsa na karuwa da wani irin salo da ba kasafai yake jin sa ba. Bai san me ke damunsa ba, amma abu daya ne yake a fili—ya makara. Ta dade a shirye, kuma shi ke bata lokaci.
Daga cikin gidan, Nabeeha ta fito a nutse, sanye da riga da siket na atamfa mai launin royal blue, wanda ya kara fidda kyawun fatarta. Dogon gyalen kanta ya tsaya tsaf akan kafadunta, yana sauka daidai gadon bayanta.
Fawaaz ya dago idonsa daga sitiyari, idanuwansa suka sauka a kanta. Ya hadiye yawu.
Ya san cewa Nabeeha kyakkyawa ce. Amma a yau, akwai wani abu a tare da ita da ya kasa fassara.
"Sorry na bata lokaci," ta fada a hankali, tana kokarin bude kofar mota.
Fawaaz bai ce komai ba. Sai kawai ya juya yana kallon gaban motar, yana jin yadda zuciyarsa ke bugawa da wani irin nauyi.
Tana shiga, ya danna wani button, motar ta rufe da kanta. Ya daidaita sitiyari, sannan ya kunna motar, suka fara tafiya.
Shiru ya ratsa tsakanin su. Kamar kullum.
Nabeeha ta dan matsa jikinta gefe, tana kokarin tsaida zuciyarta daga bugun da take yi. Tunanin cewa yau Fawaaz ne zai kaita makaranta kadai ya ishi zuciyarta gamsuwa. Amma a lokaci guda, ya tuno mata da yadda shi mutum ne da ba ya taba magana da ita.
Ya kwana biyu yana wani iri. Yana kamar yana da damuwa, amma ba zai taba fada ba.
Sannu a hankali, karar kidan da ke fitowa daga stereo ya fara cika motar.
"Can’t help falling in love with you…"
Muryar Elvis Presley ta ratsa cikin motar a hankali, tana karawa yanayin shurun dake tsakaninsu nauyi.
A ranar, tana zaune tare da Gwaggo Hafsatu a dakin. Bayan dogon shiru, sai Gwaggo Hafsatu ta kalle ta.
“Zaytunah, ya kamata ki shirya kanki.”
Hajiya Zaytunah ta dago ido. “Meye hakan ke nufi, Gwaggo?”
Gwaggo Hafsatu ta dan ja dogon numfashi. “Nabeeha za ta iya tunkarar mahaifinta da kanta. Idan har hakan ta faru, ba zai kasance da sauki ba.”
Hajiya Zaytunah ta dafe kanta. “Gwaggo, har yanzu ban shirya fuskantar sa ba. Ban shirya fuskantar dukkan su ba.”
Gwaggo Hafsatu ta kalli Zaytunah da kulawa. “Dole ne ki shirya. Idan har Nabeeha ta tunkare shi da kanta, ba zai kasance da sauki gare ki ba. Idan har gaskiya ta fito, ba za ki so a same ki cikin rashin shiri ba.”
Shiru ya ratsa dakin. Hajiya Zaytunah ta san cewa Gwaggo Hafsatu na da gaskiya, amma har yanzu zuciyarta tana tafasa da fargaba.
---
A ranar, da yamma, Nabeeha ta tsaya gaban madubi tana kallon kanta. Idanunta sun cike da damuwa, zuciyarta tana bugawa da sauri. .
MX
*KIRJIN MAI HANKALI*
_(AKWATIN SIRRIN SA)_
🧳➿💞
*PG :28*
*AREWABOOKS VVIP:👇*
https://www.arewabooks.com/book?id=670bd07e35879b101764c0eb
×××Alhaji Uzairu ya ja dogon numfashi a daya bangaren wayar, yana jin yadda zuciyarsa ke bugawa da sauri.
"Nabeeha, menene wannan magana?"
Nabeeha ta rufe idonta da karfi, zuciyarta tana tsananta bugawa. Wannan shi ne lokaci mafi wahala da ta taba fuskanta.
"Abba na,Ashe inada rabon ganawa da ku a doron duniyar nan? Ashe muma munada mahaifi da yake a raye kamar su Humayrah? zan zo wajenka in gaya maka da kaina abba," ta fada a hankali.
Shiru ya ratsa tsakanin su na tsawon dakika goma. Sannan sai Alhaji Uzairu ya furta,
"Eh mana diyar albarka, wannan batu haka yake. To shikenan, ina jiranki."
Nabeeha ta kashe wayar, sannan ta dafe KIRJIN ta. Har yanzu, zuciyarta ba ta dai-daita ba. Shin ta yanke shawarar da ta dace? Shin hakan ba zai jefa Ammi cikin matsala ba?
Firgigit tajiyo karar sautin maganar Hammad ya shigo dakin yana kallonta.
"Me kike yi haka?"
Na beeha ta dago ido, tana jin yadda jikinta ya yi sanyi.ashe mafarki take yi?
"Na kira Abba. Zan je in gaya masa komai."
Hammad ya runtse ido yana girgiza kai.
"Wane Abba kuma dear sis? Me zaki fada masa? Mafarki kike ne?"
Nabeeha ta numfasa tana sauke katuwar ajiyar zuciya tace,
"Ina jin tsoron ci gaba da rayuwa cikin wannan duhun, Hammad" ta fada da shesshekar kuka.
"Ya kamata mu waiwaya dangin mahaifin mu. Tabbas ammi taga rayuwa tana kuma cikin jarabawar wannan kaddarori da taketa fuskanta..!"
Hammad ya dafe kansa, yana jin tsantsar tashin hankali. Bai san me zai ce ba, domin yasan cewa komai ya kusa fashewa.
"Inshaa Allah khair... Dear sis.... Kowani tsanani yanatare da sauki. Da yardar Allah lokacin warwarar komai ne yazo gangara..."
"Allah ya amince"
"Aameen"
🎀🎀🎀🎀
Cikin sanyin jiki da girmamawa, Gwaggo Hafsatu ta dubi fuskokin dake gabanta. Babban parlorn nata ya cika da nutsuwa, sai murmushin hikima dake kwance a gefen lebenta. Kowa ya zauna bisa kujera, duk da a kasa suka fara zama dukansu gwaggon taki kememe kan kowa ya koma kan kujera saboda sanyin ac dake busawa ko'ina na marbles din ya dauka da sanyi...
amma babu wanda ya iya fadin uffan. Fuskokin su Nabeeha da Hammad cike suke da tambayoyi, yayin da Hajiya Zaytunah ke daure fuska, tana kokarin kwantar da hankali.
A gefen dama Major General Dawud ne, yana zaune da kamewa. Kamar kullum, dattako ya rufe fuskarsa, sai idanunsa da ke bin komai a parlorn da kulawa. Hajiya Zaytunah na kusa da Gwaggo Hafsatu, tana dafe da mayafinta kamar mai jin sanyi. Nabeeha da Hammad kuwa, suna gefenta suna jiran jin abin da zai fito daga bakin Gwaggo Hafsatu.
Gwaggo Hafsatu ta numfasa a hankali, sannan ta dube su duka.
"Nasan kun dade kuna tunanin wanene ku, daga inda kuka fito. Lokaci yayi da ya kamata ku san asalin usulin ku," ta fara magana cikin muryarta mai nutsuwa.
Ta kalli Nabeeha da Hammad kai tsaye.
"Mahafiyarku, Hajiya Zaytunah, 'yar gidan kirki ce. Ta taso cikin jin dadi da kulawa, amma hakan bai hana rayuwa tura mata jarabawarta ba. Kafin a haife ku, ta yi aure da mutum mai tarin nutsuwa da hikima, sunansa Alhaji Uzairu Muhammad, mijin ta na sunnah. Shi da yayansa, Alhaji Amiru Muhammad, su ne suka gaji dukiyar gidan su. Sai dai fa wannan aure bai kasance cikin kwanciyar hankali ba, domin kishiyoyinta biyu, Hajiya Ladi da Hajiya Karama, sun mayar da ita kamar baiwar da ta shigo gidan da kafafunta."
Gwaggo Hafsatu ta dan ja numfashi. "Hajiya Ladi da Hajiya Karama sun yi iyakar bakin kokarinsu wajen ganin cewa mahaifiyarku ba ta sami kwanciyar hankali a gidan ba. Sun hada baki da wata uwa 'yar uwarta, Hajiya Rumanah, wadda ke da tsantsar tsana da kyashi gare ta tun suna yara. Hajiya Rumanah ba wai kishiyar mahaifiyarku bace da dai da ita zaa daura auren ta da Alhaji uzairu sai Allah yayi ikon sa aka daura aurenta da Alhaji Amiru.Wato yayan mahaifinku."
Gwaggo Hafsatu ta girgiza kai, sannan ta cigaba,
"Bayan mahaifiyarku ta haifi Nabeeha, ke kenan .. sannan ta dauki ciki na biyu,wanda ke cikinta shine kai, Hammad, aka shirya wata mummunar makarkashiya. Asiri aka mata! An hada baki da bokaye, aka tsara makircin da zai sa mahaifiyarku ta bar gidan ba tare da tunanin dawowa ba. Kuma hakan ya faru."
Nabeeha ta saki numfashi, tana kallon mahaifiyarta da idanun da suka cicciko da kwalla.
"Ammi, me yasa kika bar gidanmu? Me yasa baki koma ba?"
Hajiya Zaytunah ta rintse ido, ta dafa hannun Nabeeha.
"Ba zan iya komawa ba, Nabeeha. Na rasa komai. Ba ni da mafita, kuma a lokacin, Hajiya Ladi da Hajiya Karama sun makantar da Alhaji Uzairu da zargin karya akaina. Na san idan na tsaya, da za a kashe ni ko kuma na rasa hankalina."
Hammad ya dafa hannun mahaifiyarsa. "Ammi, na fahimta. Amma me yasa sai yanzu ake sanar mana?"
Gwaggo Hafsatu ta gyara zamanta.
"Saboda lokaci yayi. Har yanzu ana neman mahaifiyarku. Duk wanda ya mata wannan asiri, ba ya so ta dawo cikin iyalinta. Sai dai hakan ba zai canza gaskiyar lamarin ba."
Nabeeha ta runtse ido, zuciyarta cike da mamaki. Hammad kuma ya dafe goshinsa. Amma abu mafi tayar musu da hankali shine kalmomin da Gwaggo Hafsatu ta kara fadi,
"Sai Muhammad manemin ki Nabeeha, Da ne ga Alhaji amiru. Wato dan gidan hajia rumanah. Hajia rumanah Kuma da mahaifin ta da mahaifin mahaifiyar ku uwar su daya uban su daya, sannan rana daya aka haifi hajia rumanah da hajiya Zaytunah... atakaice dai Muhammad Hammad dan Alhaji Amiru Muhammad ne dan yayan mahaifin ku Alhaji uzairu!"
Wani mugun shock ya saukarwa Hammad da Nabeeha. Idanunsa suka firfito, yana kallon su duka.
"Dan Hajiya Rumanah ne?"suka hada baki wajen tambaya idanuwan su sun furfuto waje cike da mamaki ..
Gwaggo Hafsatu ta gyada kai.
"Eh, dan Alhaji Amiru da Hajiya Rumanah ne. "
Wani irin nauyi ya saukarwa Hammad da Nabeeha. Don Nabeeha kuwa, numfashinta ya fara hawa da sauka. ..
Major general dawud mafia yana daga gefen da yake zaune yana hankalce da komai gefe daya dinbin mamaki da sanyin jiki sun dabaibaye shi... Yana tausayin su sosai .
"To yanzu me zai faru?" Hammad ya tambaya, yana kokarin daidaita kansa.
Gwaggo Hafsatu ta dube shi da kulawa.
"Atakaice dai mahaifiyarku Hajiya Zaytunah tana son ku. Ta yarda da kaddara, kuma tana rokon Allah ya bayyana gaskiya. Abin da ya fi shine ku cigaba da rayuwar ku da hakuri da biyayya."
A wannan lokaci, dakin yayi shiru. Idanun Nabeeha da Hammad sun cika da kwalla, zuciyoyinsu suna cike da rudani. Rayuwarsu ta canza a cikin dare daya. Sun san iyayensu, sun san asalin su. Kuma sun san cewa komai da suka sani a baya—ya canza...
MX🧕
*KIRJIN MAI HANKALI*
_(AKWATIN SIRRIN SA)_
🧳➿💞
*PG :29*
*AREWABOOKS VVIP:👇*
https://www.arewabooks.com/book?id=670bd07e35879b101764c0eb
Tashin motar Fawaaz kadai ke karan kunne a kofar gidan Major General Dawud. Baba . Wato Major general dawud ne yace ya dauki nabeeha ya kaita workshop din da sukeyi na wani course na su na makaranta. Yana jingine da kujerar motar, hannayensa rike da sitiyari, yayin da zuciyarsa ke tafasa da tunanin wacce zai dauka a yau....
Nabeeha.
Ya lumshe ido a hankali, yana jin bugun zuciyarsa na karuwa da wani irin salo da ba kasafai yake jin sa ba. Bai san me ke damunsa ba, amma abu daya ne yake a fili—ya makara. Ta dade a shirye, kuma shi ke bata lokaci.
Daga cikin gidan, Nabeeha ta fito a nutse, sanye da riga da siket na atamfa mai launin royal blue, wanda ya kara fidda kyawun fatarta. Dogon gyalen kanta ya tsaya tsaf akan kafadunta, yana sauka daidai gadon bayanta.
Fawaaz ya dago idonsa daga sitiyari, idanuwansa suka sauka a kanta. Ya hadiye yawu.
Ya san cewa Nabeeha kyakkyawa ce. Amma a yau, akwai wani abu a tare da ita da ya kasa fassara.
"Sorry na bata lokaci," ta fada a hankali, tana kokarin bude kofar mota.
Fawaaz bai ce komai ba. Sai kawai ya juya yana kallon gaban motar, yana jin yadda zuciyarsa ke bugawa da wani irin nauyi.
Tana shiga, ya danna wani button, motar ta rufe da kanta. Ya daidaita sitiyari, sannan ya kunna motar, suka fara tafiya.
Shiru ya ratsa tsakanin su. Kamar kullum.
Nabeeha ta dan matsa jikinta gefe, tana kokarin tsaida zuciyarta daga bugun da take yi. Tunanin cewa yau Fawaaz ne zai kaita makaranta kadai ya ishi zuciyarta gamsuwa. Amma a lokaci guda, ya tuno mata da yadda shi mutum ne da ba ya taba magana da ita.
Ya kwana biyu yana wani iri. Yana kamar yana da damuwa, amma ba zai taba fada ba.
Sannu a hankali, karar kidan da ke fitowa daga stereo ya fara cika motar.
"Can’t help falling in love with you…"
Muryar Elvis Presley ta ratsa cikin motar a hankali, tana karawa yanayin shurun dake tsakaninsu nauyi.