Sashe 55
Kirjin Mai Hankali Part 2 Complete Hausa Novel · about 8 min read
"Zan tafi yinin ɗaurin aure mana. Ka ce idan baka samu zuwa ba zan tafi da su"
"Ba tare da ni ba? Ba ki ga matsalar hakan bane?"
Nabeeha ta ja numfashi. "Yaa Fawaaz, dai-dai nake da sauran matan da za su tafi. Ba fa wani abu bane."
"Babu wani ‘dai-dai.’ Kin fi su daraja a gare ni."
Tayi murmushi. "To yanzu ka bani izini ko kuwa?"
Ya yi shiru na ƴan sakanni. "Bari in yi tunani."
Nabeeha ta dafe kanta. "Tunani? Akan fita ɗaurin aure?"
A ƙarshe, ya amince, amma da sharadi.
"Ki tsaya cikin mutuncinki. Kada ki yi wata mu'amala da wani namiji da ba dole ba. Ki kula da abinda kike yi. Ki turo min location."
"Na ji." Ta ce tana murmushi.
"Kiyi kyau sosai, amma kada ki burge kowa sai ni."
Nabeeha ta yi dariya. "To ai ko da na so ba zan iya burge kowa ba sai kai."
"Kin gane mana."
A cikin wurin taron, an tsara komai cikin tsari. Mata sun zauna a gefe guda, maza a gefe guda. Amma a wajen siyan baki, an haɗa matan amare da abokan ango.
Sajieedah ta ja hannun Nabeeha. "Mu je mu tsaya kusa da amarya. Daga baya sai a fara siyan bakin."
Nabeeha ta fara tafiya da ita, amma kafin su isa, sai taji ƙarar waya. Fawaaz ne!
Ta ɗaga da sauri. "Hello?"
"Ina kike?" Muryarsa ta sauya, kamar yana canza yanayi.
"Ina wajen bikin mana, kamar yadda na gaya maka."
"Dama kuna siyan baki da abokan ango ne?"
Nabeeha ta rufe ido. "Ya fawaaz… Ni ba ma cikin su fa."
"Ki fita daga wajen nan. Ba na son ki zauna kusa da su."
"To!"
Ba tare da wata gardama ba, ta ja hannun sajieedah suka koma gefe. Sajieedah ta kalleta cike da mamaki.
"Nabeeha! Wane irin saurayi me kishi ne haka?"
Nabeeha ta yi murmushi. "Wannan kishi ne mai daraja. Ki barshi kawai."
Bayan wani lokaci, sajieedah ta kalli gefe, sai ta hango wani mutum yana kallon Nabeeha.
"wani saurayi yana kallonki!" Ta ce tana dariya.
Nabeeha ta girgiza kai. "Wani kuma?"
Duk da ba ta kula shi ba, sai da taji ƙarar waya. Fawaaz ne!
Ta ɗaga da sauri. "Ina jin ka."
"Wani ne yana kallonki?" Muryarsa ta canza gaba ɗaya.
Ta haɗiye yawu. "Ban sani ba."
"To koma gida."
Ta zabura. "What?!"
"Nace ki koma gida! Ko sai nazo na same ki yanzu?"
Nabeeha ta sunkuyar da kai, ta ɗan murmusa. "Toh, zan koma."
A haka dai, ta bar bikin kafin kowa ya ankara!
Bayan ta koma gida, tana shiga ta tarar da Fawaaz yana zaune a falo.
"Kin fiye kyau da yawa." Ya ce yana kallonta da kulawa.
Ta zauna a gefensa, tana kallonsa da murmushi. "Na san dai baka barni na yi farin ciki a wajen bikin ba."
Ya ɗauki hannunta. "Ba zan so wani ya kalle ki da niyya ba."
Ta yi murmushi. "Kai fa akwai matsala!"
Ya yi dariya, ya zuba mata ido da tsananin kulawa. "Kiyi hakuri, my queen. Kishina ne kawai."
Nabeeha ta gyada kai. "Na san hakan. Kuma na yarda da kai."
A haka dai rayuwa da Fawaaz ke tafiya—cike da soyayya, kulawa, da kuma matsanancin kishi!
Bayan kwanaki, Nabeeha ta fara fahimtar cewa Fawaaz ba mutum ba ne mai sauƙin shawara idan har maganar kishinsa ce. A duk inda suke fita tare, yana da wani irin saurin lura da kallo ko motsi da wani namiji zai yi a kanta.
Ranar da Ta Fita Ba tare da Izinin Fawaaz ba
Wata rana, bayan Fawaaz ya fita zuwa aiki, Nabeeha ta kira saj don su fita zuwa boutique don yin siyayya. Tana tunanin cewa idan ta koma kafin Fawaaz ya dawo, ba zai sani ba.
Ta shirya cikin doguwar riga mai kyau da hijabi. Ba ta yi wata kwalliya mai nauyi ba, amma duk da haka ta kasance cikin wani irin kyau na halitta.
Suna tafiya a cikin boutique suna duba kaya, sai wani mai siyar da kaya ya kalleta da murmushi.
"Madam, wannan kayan ya yi miki kyau sosai. Ya kamata ki ɗauka."
Humairah ta kalle ta tana murmushi. "Lallai kuwa! Nabeeha, ki sayi wannan kayan."
Nabeeha ta ɗauki rigar tana nazari, amma kafin ta ce komai, sai taji wata murya daga bayansu.
"Ki ajiye kayan, ki zo mu tafi."
Gabanta ya faɗi. Tana juyowa, sai ta ga Fawaaz yana tsaye a ƙofar boutique ɗin, hannuwansa a haɗe, idonsa cike da tsawa.
Tayi shiru na ƴan dakiku kafin ta ce cikin sanyin murya. "Fawaaz… ka dawo kenan?"
Ya ɗan tsuke fuska. "Ba ma haka ba. Me kike yi a nan?"
Ta kalli saj da ke kallonsu da mamaki. Sai kuma ta ce cikin damuwa. "Na fita ne kawai don yin siyayya."
Fawaaz ya kalli mai siyar da kaya, yana hura hanci kamar zai ƙone da wuta. Sannan ya dawo da kallonsa kanta.
"Wato kin fita ba tare da izini na ba? Kuma wani yana yi miki murmushi yana cewa wannan kayan ya miki kyau?!"
Nabeeha ta buɗe baki zata yi magana, amma sai ya ce: "Mu tafi, yanzu!"
Tayi shiru, ta sauke rigar hannunta sannan ta bi shi da sauri. Saj ta bita da kallo cike da mamaki da sha’awa.
A cikin mota, babu wanda ya yi magana. Sai dai Fawaaz yana tuka motar da wani irin ƙarfin hali, yana riƙe sitiyari tamkar zai balla shi.
Bayan sun isa gida, sai ya tsaya yana kallonta da ido mai cike da kishi.
"Wani ne ya taɓa ki?"
Ta zaro ido. "A’uzu billah! Ya Fawaaz! Me kake nufi?"
"Wani ne ya ce yana son ki?"
Ta saki baki da mamaki. "Kai fa akwai matsala! Ba wanda ya ce haka!"
Ya harare ta. "To me ya sa ya ce miki wannan kayan ya miki kyau?"
Ta taɓe baki. "Ai hakan ba laifi bane. Yana siyar da kaya ne, ya kamata ya faɗi hakan."
Fawaaz ya ɗan matsa kusa da ita, yana kallonta da tsantsar kulawa. "Ki kula, Nabeeha. Ba zan yarda wani namiji ya kalli matata da wata manufa ba." Kai kace an shafa fatiha yadda yake nuna ikonsa akanta 🤣
Ta yi murmushi. "Fawaaz, kana da matsanancin kishi."
Ya yi murmushi shima. "Ba matsananci ba, sai dai na gaskiya."
🎀🎀
A nutsuwar dare mai annuri, tsit ya lullube anguwar da ake kyalli da fitilu, iska mai laushi na kadawa kamar tana busa saƙon wata soyayya da ke ɓoye. A gaban wani babban gida, wata bakar Jeep mai kyan gaske ta faka a gefen hanya. Wani saurayi tsaye a cikin motar, hannunsa na dama na bisa steering, na hagu kuma yana jan wayarsa don kiran wata ‘yar baiwa.
Captain fawaaz.
Cikakken mutum ne, dogo, mai murɗaɗɗen jiki irin na sojoji. Fuskar tasa cike take da kwarjini da miskilanci, amma yau idanunsa sun zubo da wani yanayi mai cike da salo. Yana sanye da bakar riga mai nauyin gaske, wadda ta kwanta ajikinsa, sai wando jeans mai tsari da sneakers na designers. Lallausan gashinsa yana kwance a saman goshinsa, idonsa masu kauri da tsantsar baƙi suna haskawa da natsuwa, lebensa yana ɗauke da ƙanƙantar murmushi.
Ya danna kiran.
Daga can cikin gida, Nabeeha na zaune akan gadonta, cikin farin riga ta shadda mai tsabta, wadda ta zauna luf akan ta. Gashinta a daure cikin style mai kyau, sai ta lulluba da mayafi irin na ladabi. Idonta suka sauka kan sunan da ya bayyana akan wayarta. "Captain Fawaaz Dawud." Kamar an danna mata wutar lantarki haka ta ji, zuciyarta ta buga, amma ta ɗauki wayar cikin sanyin jiki.
"Ina kika shiga?" Muryarsa mai daɗi da ƙara wa zuciya sauti ya fita daga wayar.
"Uhmm… ina daki." Ta amsa a hankali.
"Fito ki zo."
Shiru ta ɗan yi, kafin ta tashi da natsuwa, zuciyarta na harbawa da nau’in wata soyayya da ta kasa fassara. Har ta ƙarasa bakin kofa, tana jin yadda numfashinta ke sauyawa.
A hankali ta ƙarasa inda motarsa take, tana taku cikin cika alkawarin mace mai haiba da kamun kai. Fawaaz yana kallonta ta cikin madubin motarsa, yadda take tafiya da nutsuwa, yadda hasken fitilu ke bayyana kyanta, har sai da ya ɗan ja numfashi.
Da isarta kusa da motar, ya buɗe ƙofar gaba, ya watsa mata wani kallo na ƙwarjini. "Shigo."
Ba tare da wata gardama ba, ta shigo, numfashinta na luguden wata dabara da zuciyarta ke kokarin ɓoyewa.
Ya juyo gareta, ya sauke idanunsa cikin nata, sannan ya ɗan lumshe su kafin ya ce, "Kin san ba zan kira ki na ce ki fito haka kawai ba, ko?"
Ta ɗan haɗiye yawu, tana jinsa da kasala.
Ya ɗan ɗaga gira, yana kallonta kamar yana nazarinta. "Nabeeha… kin taɓa jin ana soyayya da zuciya amma baka san ta ina za ka fara furta kalmomin ba?"
Numfashinta ya tsinke. Ta kalli gefe. "Ba…" Muryarta ta makale.
Ya saki murmushi, mai ɗan ƙanƙantar gaske, sannan ya ce, "Ina fargabar gaya miki abubuwa da yawa, domin zuciyata tana da SIRRI ka da yawa. Amma daya daga ciki shine…"
Ya ɗan yi shiru, yana kallonta. "Kullum ina tunanin ki."
Nabeeha ta runtse idonta, tana jin yadda zuciyarta ke bugawa da sauri. Ajiyar zuciya ta sauke, amma bata iya cewa komai ba.
Fawaaz ya ci gaba. "Kina yi min yawa, Nabeeha. Idan kina kusa da ni, zuciyata na yin wani iri. Idan ba ki kusa, zuciyata na jin wani iri. Me kike so inyi da kaina?"
Tayi shiru, tana jin yadda kalmominsa suka daki zuciyarta.
Fawaaz ya ɗan matsa kusa da ita, yana kallon fuskarta da ido mai cike da wani sirrin soyayya. "Kin san tun farko bana tunanin zan iya cewa haka? Amma yanzu ba zan iya ɓoyewa ba."
Ya sauke wani numfashi, ya ɗan yi ƙasa da murya. "I love you, Nabeeha."
Wani irin abu ya tsarga a zuciyarta, idanunta suka lumshe, zuciyarta na dokawa kamar ana bugun ganga.
Ya juyo sosai gareta, yana jira ta ce wani abu. Amma ta yi shiru.
Fawaaz ya ɗan yi murmushi mai taushi. "Ba sai kin ce komai ba. Amma ki sani… zuciyata ta faɗa cikin wani launi da bai taɓa sanin sa ba saboda ke."
Shiru ne ya mamaye motar, sai kukan zuciyoyi biyu da ke tafiyar da soyayya cikin shauki.
MX 🧕
*KIRJIN MAI HANKALI*
_(Akwatin sirrin sa)_
_🧳👩❤️👨🌺_
"Ba tare da ni ba? Ba ki ga matsalar hakan bane?"
Nabeeha ta ja numfashi. "Yaa Fawaaz, dai-dai nake da sauran matan da za su tafi. Ba fa wani abu bane."
"Babu wani ‘dai-dai.’ Kin fi su daraja a gare ni."
Tayi murmushi. "To yanzu ka bani izini ko kuwa?"
Ya yi shiru na ƴan sakanni. "Bari in yi tunani."
Nabeeha ta dafe kanta. "Tunani? Akan fita ɗaurin aure?"
A ƙarshe, ya amince, amma da sharadi.
"Ki tsaya cikin mutuncinki. Kada ki yi wata mu'amala da wani namiji da ba dole ba. Ki kula da abinda kike yi. Ki turo min location."
"Na ji." Ta ce tana murmushi.
"Kiyi kyau sosai, amma kada ki burge kowa sai ni."
Nabeeha ta yi dariya. "To ai ko da na so ba zan iya burge kowa ba sai kai."
"Kin gane mana."
A cikin wurin taron, an tsara komai cikin tsari. Mata sun zauna a gefe guda, maza a gefe guda. Amma a wajen siyan baki, an haɗa matan amare da abokan ango.
Sajieedah ta ja hannun Nabeeha. "Mu je mu tsaya kusa da amarya. Daga baya sai a fara siyan bakin."
Nabeeha ta fara tafiya da ita, amma kafin su isa, sai taji ƙarar waya. Fawaaz ne!
Ta ɗaga da sauri. "Hello?"
"Ina kike?" Muryarsa ta sauya, kamar yana canza yanayi.
"Ina wajen bikin mana, kamar yadda na gaya maka."
"Dama kuna siyan baki da abokan ango ne?"
Nabeeha ta rufe ido. "Ya fawaaz… Ni ba ma cikin su fa."
"Ki fita daga wajen nan. Ba na son ki zauna kusa da su."
"To!"
Ba tare da wata gardama ba, ta ja hannun sajieedah suka koma gefe. Sajieedah ta kalleta cike da mamaki.
"Nabeeha! Wane irin saurayi me kishi ne haka?"
Nabeeha ta yi murmushi. "Wannan kishi ne mai daraja. Ki barshi kawai."
Bayan wani lokaci, sajieedah ta kalli gefe, sai ta hango wani mutum yana kallon Nabeeha.
"wani saurayi yana kallonki!" Ta ce tana dariya.
Nabeeha ta girgiza kai. "Wani kuma?"
Duk da ba ta kula shi ba, sai da taji ƙarar waya. Fawaaz ne!
Ta ɗaga da sauri. "Ina jin ka."
"Wani ne yana kallonki?" Muryarsa ta canza gaba ɗaya.
Ta haɗiye yawu. "Ban sani ba."
"To koma gida."
Ta zabura. "What?!"
"Nace ki koma gida! Ko sai nazo na same ki yanzu?"
Nabeeha ta sunkuyar da kai, ta ɗan murmusa. "Toh, zan koma."
A haka dai, ta bar bikin kafin kowa ya ankara!
Bayan ta koma gida, tana shiga ta tarar da Fawaaz yana zaune a falo.
"Kin fiye kyau da yawa." Ya ce yana kallonta da kulawa.
Ta zauna a gefensa, tana kallonsa da murmushi. "Na san dai baka barni na yi farin ciki a wajen bikin ba."
Ya ɗauki hannunta. "Ba zan so wani ya kalle ki da niyya ba."
Ta yi murmushi. "Kai fa akwai matsala!"
Ya yi dariya, ya zuba mata ido da tsananin kulawa. "Kiyi hakuri, my queen. Kishina ne kawai."
Nabeeha ta gyada kai. "Na san hakan. Kuma na yarda da kai."
A haka dai rayuwa da Fawaaz ke tafiya—cike da soyayya, kulawa, da kuma matsanancin kishi!
Bayan kwanaki, Nabeeha ta fara fahimtar cewa Fawaaz ba mutum ba ne mai sauƙin shawara idan har maganar kishinsa ce. A duk inda suke fita tare, yana da wani irin saurin lura da kallo ko motsi da wani namiji zai yi a kanta.
Ranar da Ta Fita Ba tare da Izinin Fawaaz ba
Wata rana, bayan Fawaaz ya fita zuwa aiki, Nabeeha ta kira saj don su fita zuwa boutique don yin siyayya. Tana tunanin cewa idan ta koma kafin Fawaaz ya dawo, ba zai sani ba.
Ta shirya cikin doguwar riga mai kyau da hijabi. Ba ta yi wata kwalliya mai nauyi ba, amma duk da haka ta kasance cikin wani irin kyau na halitta.
Suna tafiya a cikin boutique suna duba kaya, sai wani mai siyar da kaya ya kalleta da murmushi.
"Madam, wannan kayan ya yi miki kyau sosai. Ya kamata ki ɗauka."
Humairah ta kalle ta tana murmushi. "Lallai kuwa! Nabeeha, ki sayi wannan kayan."
Nabeeha ta ɗauki rigar tana nazari, amma kafin ta ce komai, sai taji wata murya daga bayansu.
"Ki ajiye kayan, ki zo mu tafi."
Gabanta ya faɗi. Tana juyowa, sai ta ga Fawaaz yana tsaye a ƙofar boutique ɗin, hannuwansa a haɗe, idonsa cike da tsawa.
Tayi shiru na ƴan dakiku kafin ta ce cikin sanyin murya. "Fawaaz… ka dawo kenan?"
Ya ɗan tsuke fuska. "Ba ma haka ba. Me kike yi a nan?"
Ta kalli saj da ke kallonsu da mamaki. Sai kuma ta ce cikin damuwa. "Na fita ne kawai don yin siyayya."
Fawaaz ya kalli mai siyar da kaya, yana hura hanci kamar zai ƙone da wuta. Sannan ya dawo da kallonsa kanta.
"Wato kin fita ba tare da izini na ba? Kuma wani yana yi miki murmushi yana cewa wannan kayan ya miki kyau?!"
Nabeeha ta buɗe baki zata yi magana, amma sai ya ce: "Mu tafi, yanzu!"
Tayi shiru, ta sauke rigar hannunta sannan ta bi shi da sauri. Saj ta bita da kallo cike da mamaki da sha’awa.
A cikin mota, babu wanda ya yi magana. Sai dai Fawaaz yana tuka motar da wani irin ƙarfin hali, yana riƙe sitiyari tamkar zai balla shi.
Bayan sun isa gida, sai ya tsaya yana kallonta da ido mai cike da kishi.
"Wani ne ya taɓa ki?"
Ta zaro ido. "A’uzu billah! Ya Fawaaz! Me kake nufi?"
"Wani ne ya ce yana son ki?"
Ta saki baki da mamaki. "Kai fa akwai matsala! Ba wanda ya ce haka!"
Ya harare ta. "To me ya sa ya ce miki wannan kayan ya miki kyau?"
Ta taɓe baki. "Ai hakan ba laifi bane. Yana siyar da kaya ne, ya kamata ya faɗi hakan."
Fawaaz ya ɗan matsa kusa da ita, yana kallonta da tsantsar kulawa. "Ki kula, Nabeeha. Ba zan yarda wani namiji ya kalli matata da wata manufa ba." Kai kace an shafa fatiha yadda yake nuna ikonsa akanta 🤣
Ta yi murmushi. "Fawaaz, kana da matsanancin kishi."
Ya yi murmushi shima. "Ba matsananci ba, sai dai na gaskiya."
🎀🎀
A nutsuwar dare mai annuri, tsit ya lullube anguwar da ake kyalli da fitilu, iska mai laushi na kadawa kamar tana busa saƙon wata soyayya da ke ɓoye. A gaban wani babban gida, wata bakar Jeep mai kyan gaske ta faka a gefen hanya. Wani saurayi tsaye a cikin motar, hannunsa na dama na bisa steering, na hagu kuma yana jan wayarsa don kiran wata ‘yar baiwa.
Captain fawaaz.
Cikakken mutum ne, dogo, mai murɗaɗɗen jiki irin na sojoji. Fuskar tasa cike take da kwarjini da miskilanci, amma yau idanunsa sun zubo da wani yanayi mai cike da salo. Yana sanye da bakar riga mai nauyin gaske, wadda ta kwanta ajikinsa, sai wando jeans mai tsari da sneakers na designers. Lallausan gashinsa yana kwance a saman goshinsa, idonsa masu kauri da tsantsar baƙi suna haskawa da natsuwa, lebensa yana ɗauke da ƙanƙantar murmushi.
Ya danna kiran.
Daga can cikin gida, Nabeeha na zaune akan gadonta, cikin farin riga ta shadda mai tsabta, wadda ta zauna luf akan ta. Gashinta a daure cikin style mai kyau, sai ta lulluba da mayafi irin na ladabi. Idonta suka sauka kan sunan da ya bayyana akan wayarta. "Captain Fawaaz Dawud." Kamar an danna mata wutar lantarki haka ta ji, zuciyarta ta buga, amma ta ɗauki wayar cikin sanyin jiki.
"Ina kika shiga?" Muryarsa mai daɗi da ƙara wa zuciya sauti ya fita daga wayar.
"Uhmm… ina daki." Ta amsa a hankali.
"Fito ki zo."
Shiru ta ɗan yi, kafin ta tashi da natsuwa, zuciyarta na harbawa da nau’in wata soyayya da ta kasa fassara. Har ta ƙarasa bakin kofa, tana jin yadda numfashinta ke sauyawa.
A hankali ta ƙarasa inda motarsa take, tana taku cikin cika alkawarin mace mai haiba da kamun kai. Fawaaz yana kallonta ta cikin madubin motarsa, yadda take tafiya da nutsuwa, yadda hasken fitilu ke bayyana kyanta, har sai da ya ɗan ja numfashi.
Da isarta kusa da motar, ya buɗe ƙofar gaba, ya watsa mata wani kallo na ƙwarjini. "Shigo."
Ba tare da wata gardama ba, ta shigo, numfashinta na luguden wata dabara da zuciyarta ke kokarin ɓoyewa.
Ya juyo gareta, ya sauke idanunsa cikin nata, sannan ya ɗan lumshe su kafin ya ce, "Kin san ba zan kira ki na ce ki fito haka kawai ba, ko?"
Ta ɗan haɗiye yawu, tana jinsa da kasala.
Ya ɗan ɗaga gira, yana kallonta kamar yana nazarinta. "Nabeeha… kin taɓa jin ana soyayya da zuciya amma baka san ta ina za ka fara furta kalmomin ba?"
Numfashinta ya tsinke. Ta kalli gefe. "Ba…" Muryarta ta makale.
Ya saki murmushi, mai ɗan ƙanƙantar gaske, sannan ya ce, "Ina fargabar gaya miki abubuwa da yawa, domin zuciyata tana da SIRRI ka da yawa. Amma daya daga ciki shine…"
Ya ɗan yi shiru, yana kallonta. "Kullum ina tunanin ki."
Nabeeha ta runtse idonta, tana jin yadda zuciyarta ke bugawa da sauri. Ajiyar zuciya ta sauke, amma bata iya cewa komai ba.
Fawaaz ya ci gaba. "Kina yi min yawa, Nabeeha. Idan kina kusa da ni, zuciyata na yin wani iri. Idan ba ki kusa, zuciyata na jin wani iri. Me kike so inyi da kaina?"
Tayi shiru, tana jin yadda kalmominsa suka daki zuciyarta.
Fawaaz ya ɗan matsa kusa da ita, yana kallon fuskarta da ido mai cike da wani sirrin soyayya. "Kin san tun farko bana tunanin zan iya cewa haka? Amma yanzu ba zan iya ɓoyewa ba."
Ya sauke wani numfashi, ya ɗan yi ƙasa da murya. "I love you, Nabeeha."
Wani irin abu ya tsarga a zuciyarta, idanunta suka lumshe, zuciyarta na dokawa kamar ana bugun ganga.
Ya juyo sosai gareta, yana jira ta ce wani abu. Amma ta yi shiru.
Fawaaz ya ɗan yi murmushi mai taushi. "Ba sai kin ce komai ba. Amma ki sani… zuciyata ta faɗa cikin wani launi da bai taɓa sanin sa ba saboda ke."
Shiru ne ya mamaye motar, sai kukan zuciyoyi biyu da ke tafiyar da soyayya cikin shauki.
MX 🧕
*KIRJIN MAI HANKALI*
_(Akwatin sirrin sa)_
_🧳👩❤️👨🌺_