Sashe 16
Kirjin Mai Hankali Part 2 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Idan har Rumanah ta aikata haka, hakan yana nufin cewa akwai wani abu a zuciyarta tun tuni da ba su fahimta ba. Me ya sa ta tsane su haka? Me yasa take ganin su a matsayin abokan gaba?
"Ina jin akwai wani abu da zan gano." Ta furta a hankali.
Dole ne ta fahimci SIRRIN Rumanah, ta gano dalilin kiyayyar da take yi musu. Kuma kafin ta dauki mataki, dole ta tabbatar da cewa komai a fayace.
Ta numfasa da kyar, ta juyo ta kalli su Gora da suka gama sanar da ita SIRRIN da suka samu. Ta yi shiru na dan lokaci, sannan ta ce da su cikin murya mai tsanani,
"Kun ce min Rumanah ce ta dauke ku aiki?"
Gora ya gyada kai cikin girmamawa. "Eh, Hajiya. Ita ce ta biya mu, ta ce mu tabbata mun bata miki rai. Ta ce mu yi duk mai yiwuwa domin mu tabbatar da cewa kin yi nadamar rayuwa."
Wani takaici ya sake turnuke zuciyar Hajiya Zaytunah. Ta numfasa a hankali, sannan ta ce:
"Ba damuwa. Na gode da gaskiyar da kuka gaya min."
Ta juya tana kallon kofar da ke gabanta, zuciyarta na cike da sabbin tunani. Wannan abu ba zai kare haka ba. Dole ne ta dauki mataki.
_1-KALBIM:MAMUH GEE_
_2-KIRJIN MAI HANKALI (AKWATIN SIRRIN SA):MSS XOXO_
_3-ADUNIYATAH :HUGUMAH_
_4-AJIYA A DUHU: BILYN ABDULL_
°°
_1-BOOK DAYA:DARI BIYAR_
_2-BOOKS BIYU:DUBU DAYA_
_3-BOOKS UKU: DUBU DAYA DA DARI BIYAR_
_4-BOOKS HUDU :DUBU BIYU_
_5_YAN NIJAR: 1000CF: 89825722 NOUSAIBA LAWALI MARADI_
_ku tura receipt zuwa ga 09033181070_
*IDAN KATI NE A TURO TA WANNAN NUMBER:*
*09032345899.. SHEDAR KATIN MA NAN ZAA TURA. KATIN MTN!!MTN!!*
____
**KIRJIN MAI HANKALI*
_(Akwatin sirrin sa)_
_🧳👩❤️👨🌺_
*_The Vault Of His Secrets_*
_®️NANA HAFSATU (MX)_
_©️ZAFAFA BIYAR WRITERS_
*_BOOK TWO_*
_PAGE: 14_
Captain Fawaaz ya jinjina kai, bai ce komai ba. Idanunsa sun sauka kan na’urar tracking da ke gabansa, ya tuno da sakonnin daya turawa Nabeeha, Wannan yana nufin cewa a wannan lokacin layinta yana bisa sabis, kuma hakan na iya basu damar gano inda suke.
Ya matsa wani maballi a kan na'urar, ya duba taswirar da ke gabansa. Hanyar da suka bi tana da wahala, sai dai a haka ma ba zai yi kasa a gwiwa ba. Yana jin bugun zuciyarsa yana karuwa. Ko da yake ya saba da irin wannan aiki, wannan yana da bambanci , Yana nufin ceto most beloved love of his life, Wato Nabeeha.
"Kayi tracking ɗin network ɗin nata?" Lieutenant Ibrahim ya tambaya.
"Eh," Fawaaz ya amsa, yana duba wani karamin screen a gefen dashboard. Ya kara danna wasu maballan sannan ya ce,
"Anan sakon ya shiga, daga nan zuwa wani wuri a kusa da gabar rafin Chida."
"To, akwai wata gada kusa da wannan rafi, amma an ce tana da matsala, babu wanda ke amfani da ita," Warrant Officer Suleiman ya kara da furtawa, yana duba bayanai a cikin wata ƙaramar kwamfuta.
"To lallai sun bi waccan hanyar," Fawaaz ya yanke hukunci.
Sai ya kara gudun motarsa a hankali, yana bin alamar da suka samu. Sauran motocin biyu da ke biye da su suma suka kara saurin tafiya, dukkansu cikin shiri. Su na ci gaba da tafiya cikin dajin, tayoyin motocin su na dannan ciyayi da ƙurar dajin.
Kusan mintuna talatin suna tafiya, sai na’urar tracking ɗin ta soma nuna wani matsayi kusa da su. Zuciyar Fawaaz ta buga da sauri.
"Alhamdulillah suna nan kusa," ya furta da wata murya mai ƙarfi.
Yana tsayar da motarsa a hankali, sauran motocin suma suka tsaya. Dukkaninsu suka kama bindigoginsu suna shirin fuskantar duk wani haɗari.
"Mu fita a hankali. Kar mu yi saurin motsi har sai mun tabbatar da yanayin da muke ciki," Fawaaz ya umarta, yana kokarin danne tsananin kwadayin da yake ji na ganin Nabeeha.
Sai suka rarrafa cikin dajin da taka-tsantsan, kowannensu yana duban gefen daji. Bayan kusan minti goma da shiru-shiru, sai suka jiyo wata murya daga baya,
"Da alama su ne can!"
Fawaaz ya zura zooming tool. Ya na ware ido, zuciyarsa na dukan uku-uku. A cikin wata ruguwar kwantaccen ciyayi da wasu tsofaffin bishiyoyi, ya hangi wasu mutane suna zaune kusa da wata karamar bukka. A tsakiyarsu, su Nabeehan sa ce!
Haj. Zaytunah tana zaune a gefe, tana rike da hannun Hammad da ke jin tsoro sosai. Nabeeha kuma tana a gefe, idonta cike da damuwa. Sai kuma wasu mutum biyu, Gora da Bala, waɗanda suke kallon gefe-gefe, suna jin wani irin damuwa.
Fawaaz ya dan zaro iska daga bakinsa, yana kokarin nutsuwa. Amma a zuciyarsa, yana jin wani irin ƙarfi da ƙwazo sun lullube shi.
"A shirya!" ya furta cikin sassanyar murya. "Zamu yi aiki mai tsabta. Nabeeha da sauran su na bukatar mu."
Babu wanda ya musa. Sun san cewa wannan aiki ne da ba za su bari ya gaza ba.
Fawaaz ya gyara rike bindigarsa, idonsa ya fi komawa kan Nabeeha. Ko da yake ba ta ganshi ba tukunna, amma ya san cewa cikin 'yan dakikoki, zai yi duk mai yiwuwa don ganin sun fita daga wannan wuri lafiya!
Fawaaz ya dan sunkuya yana lura da yanayin wurin. Binciken idanuwansa ya nuna masa cewa mutanen da suka yi garkuwa da su Nabeeha ba su da yawan makamai, amma hakan ba yana nufin ba su da hatsari ba. Ya san cewa su Gora da Bala mutane ne masu dabara, kuma ba zai yi ƙasa a gwiwa wajen yaƙar su ba.
Ya yi alama ga abokan aikinsa su zagaya ta bangarori daban-daban domin su mamaye yankin da dazukan uku da suka rage, kudu, gabas dana yamma, Lieutenant Ibrahim da Warrant Officer Suleiman sun kama hagu, yayin da sauran suka kama dama. Fawaaz ya cigaba da lurawa da yadda ake tafiyar da abubuwa daga inda suke..
Nabeeha tana zaune a gefen Hajiya Zaytunah, idanunta cike da damuwa. Hammad yana nan rike da hannunta, yana ta kallon gefe cike da tsoro. Gora yana tsaye kusa da Bala, yana magana da wani karamin walkie-talkie, yana kokarin tuntubar wani a waje.
"Hello...."
Daidai lokacin, Nabeeha ta ji zuciyarta tana wani irin bugawa. Ta rufe idanuwanta na wasu dakiku, tana jin kamar numfashinta zai dauke. Amma cikin wannan yanayi na tsoro, sai wani tunani ya fado mata… Fawaaz!
Bata ankara ba, sai kawai ta ji karar wani abu yana kara kusa da su ,kamar motsin mutane cikin daji. Idanunta suka kai kan Gora, wanda shima ya ji motsin.
"Me ke faruwa?" Bala ya tambaya yana kai hannu kan bindigarsa.
A daidai wannan lokacin, Fawaaz ya bayar da umarni cikin walkie-talkie,
"Roger that soldiers..Yanzu! Mu Shiga!"
Cikin gaggawa, sojojin suka fantsama daga bangarori daban-daban! Wani dan karamin fashewar hayaki ya biyo baya, wanda ya sa Bala da Gora suka rude, suna kokarin zaro makamai.
Fawaaz bai bata lokaci ba, ya shiga ta babban kofar bukkar cikin matsanancin sauri, bindigarsa a hannu, idanunsa suna kan Gora da Bala.
"Kada ku motsa!" ya daka musu tsawa.
Bala ya yi kokarin daga bindigarsa, amma kafin ya ankara, sai Lieutenant Ibrahim ya karbe bindigar daga hannunsa. Gora kuwa ya yi kokarin tserewa ta bayan bukkar, amma kafin ya iya, Warrant Officer Suleiman ya cafke shi da karfi, ya buga shi kasa.
Fawaaz bai damu da su ba, idanunsa sun sauka kai tsaye kan Nabeeha!
Zuciyarta ta buga da karfi, tana jin kamar numfashinta zai tsaya. A karo na farko, ta ji wani irin kwanciyar hankali da ta dade tana jira.
Fawaaz ya taka kusa da ita, yana kallonta ido cikin ido. Babu wanda ya ce uffan. Ya mika mata hannu a hankali, idanunsa cike da nutsuwa.
"Kin ji tsoro?" ya tambaye ta da murya mai laushi.
Nabeeha ta girgiza kai, amma idanuwanta sun nuna cewa ta ji tsoro fiye da yadda zata iya furtawa.
Ba tare da wata shakka ba, ya kama hannunta ya rike da kyau.
"Don't be...Ssshhh is okayy" ya furta.
A gefe guda, Hajiya Zaytunah ta runtse idanuwa, tana fitar da ajiyar zuciya. Hammad kuwa ya ruga ya rungume Captain Fawaaz da karfi, yana kuka da murna.
Fawaaz ya dan matsa daga gefe, yana tabbatar da cewa komai yana tafiya daidai. Sauran sojojin sun riga sun kama Gora da Bala, sun daure hannayensu da igiya, sannan suka rufe musu baki domin su guji yin hayaniya. A gefe guda, Lieutenant Ibrahim yana duba motar da masu garkuwar suka kawo, yana tabbatar da cewa babu wani abin fashewa ko tarkon da zai iya kawo hatsari.
Nabeeha har yanzu tana tsaye a wurin, zuciyarta na harbawa da karfi. Idanunta sun cika da ruwaye, ba wai saboda tsoro ba, amma saboda yawan damuwar da ta sha. Har yanzu tana jin yadda hannun Fawaaz ke rike da nata , rikon da ya tabbatar mata cewa yanzu tana cikin aminci.
Fawaaz ya dan sunkuya yana shafa kansa, sannan ya ce, "Su daina damunki, Zamu mika su hannun hukuma, za su fuskanci hukuncin da ya dace da su."
Hammad ya dan yi shiru na wasu dakiku, sai daga baya ya jinjina kai. "Mungode, Captain brother!"
Fawaaz bai ce komai ba, sai ya mike tsaye, ya nuna musu hanyar da za su bi zuwa motocin su. Sauran sojojin sun bi sawu, suna rike da Gora da Bala da aka daure su.
A daidai lokacin da suka fara tafiya, sai Fawaaz ya lura da yadda Nabeeha ke tafiya a hankali, kamar wacce ba ta da kwari sosai. Bai yi wata-wata ba, ya dan riko hannunta, yana tafiya tare da ita.
"Kin gaji?" ya tambaya, amma yana kallonta cikin ido.
Ta dan yi murmushi kadan, sannan ta ce, "Kadan dai."
Sai da suka soma tafiya kafin Nabeeha ta iya furta wani abu.
Fawaaz bai ce komai ba. Amma a zuciyarsa, ya san cewa zai iya yin komai don ganin cewa ba ta sake fuskantar irin wannan hatsari ba har abada.
Zuciyar Fawaaz tana daka da sauri fiye da yadda ya saba ji. Hannunsa yana rike da nata, amma har yanzu ba ya jin hakan ya wadatar. Idanunsa na tafiya a fuskarta, yana nazarin ta, yana neman wani alamun ciwo ko wahala.
"Ina jin akwai wani abu da zan gano." Ta furta a hankali.
Dole ne ta fahimci SIRRIN Rumanah, ta gano dalilin kiyayyar da take yi musu. Kuma kafin ta dauki mataki, dole ta tabbatar da cewa komai a fayace.
Ta numfasa da kyar, ta juyo ta kalli su Gora da suka gama sanar da ita SIRRIN da suka samu. Ta yi shiru na dan lokaci, sannan ta ce da su cikin murya mai tsanani,
"Kun ce min Rumanah ce ta dauke ku aiki?"
Gora ya gyada kai cikin girmamawa. "Eh, Hajiya. Ita ce ta biya mu, ta ce mu tabbata mun bata miki rai. Ta ce mu yi duk mai yiwuwa domin mu tabbatar da cewa kin yi nadamar rayuwa."
Wani takaici ya sake turnuke zuciyar Hajiya Zaytunah. Ta numfasa a hankali, sannan ta ce:
"Ba damuwa. Na gode da gaskiyar da kuka gaya min."
Ta juya tana kallon kofar da ke gabanta, zuciyarta na cike da sabbin tunani. Wannan abu ba zai kare haka ba. Dole ne ta dauki mataki.
_1-KALBIM:MAMUH GEE_
_2-KIRJIN MAI HANKALI (AKWATIN SIRRIN SA):MSS XOXO_
_3-ADUNIYATAH :HUGUMAH_
_4-AJIYA A DUHU: BILYN ABDULL_
°°
_1-BOOK DAYA:DARI BIYAR_
_2-BOOKS BIYU:DUBU DAYA_
_3-BOOKS UKU: DUBU DAYA DA DARI BIYAR_
_4-BOOKS HUDU :DUBU BIYU_
_5_YAN NIJAR: 1000CF: 89825722 NOUSAIBA LAWALI MARADI_
_ku tura receipt zuwa ga 09033181070_
*IDAN KATI NE A TURO TA WANNAN NUMBER:*
*09032345899.. SHEDAR KATIN MA NAN ZAA TURA. KATIN MTN!!MTN!!*
____
**KIRJIN MAI HANKALI*
_(Akwatin sirrin sa)_
_🧳👩❤️👨🌺_
*_The Vault Of His Secrets_*
_®️NANA HAFSATU (MX)_
_©️ZAFAFA BIYAR WRITERS_
*_BOOK TWO_*
_PAGE: 14_
Captain Fawaaz ya jinjina kai, bai ce komai ba. Idanunsa sun sauka kan na’urar tracking da ke gabansa, ya tuno da sakonnin daya turawa Nabeeha, Wannan yana nufin cewa a wannan lokacin layinta yana bisa sabis, kuma hakan na iya basu damar gano inda suke.
Ya matsa wani maballi a kan na'urar, ya duba taswirar da ke gabansa. Hanyar da suka bi tana da wahala, sai dai a haka ma ba zai yi kasa a gwiwa ba. Yana jin bugun zuciyarsa yana karuwa. Ko da yake ya saba da irin wannan aiki, wannan yana da bambanci , Yana nufin ceto most beloved love of his life, Wato Nabeeha.
"Kayi tracking ɗin network ɗin nata?" Lieutenant Ibrahim ya tambaya.
"Eh," Fawaaz ya amsa, yana duba wani karamin screen a gefen dashboard. Ya kara danna wasu maballan sannan ya ce,
"Anan sakon ya shiga, daga nan zuwa wani wuri a kusa da gabar rafin Chida."
"To, akwai wata gada kusa da wannan rafi, amma an ce tana da matsala, babu wanda ke amfani da ita," Warrant Officer Suleiman ya kara da furtawa, yana duba bayanai a cikin wata ƙaramar kwamfuta.
"To lallai sun bi waccan hanyar," Fawaaz ya yanke hukunci.
Sai ya kara gudun motarsa a hankali, yana bin alamar da suka samu. Sauran motocin biyu da ke biye da su suma suka kara saurin tafiya, dukkansu cikin shiri. Su na ci gaba da tafiya cikin dajin, tayoyin motocin su na dannan ciyayi da ƙurar dajin.
Kusan mintuna talatin suna tafiya, sai na’urar tracking ɗin ta soma nuna wani matsayi kusa da su. Zuciyar Fawaaz ta buga da sauri.
"Alhamdulillah suna nan kusa," ya furta da wata murya mai ƙarfi.
Yana tsayar da motarsa a hankali, sauran motocin suma suka tsaya. Dukkaninsu suka kama bindigoginsu suna shirin fuskantar duk wani haɗari.
"Mu fita a hankali. Kar mu yi saurin motsi har sai mun tabbatar da yanayin da muke ciki," Fawaaz ya umarta, yana kokarin danne tsananin kwadayin da yake ji na ganin Nabeeha.
Sai suka rarrafa cikin dajin da taka-tsantsan, kowannensu yana duban gefen daji. Bayan kusan minti goma da shiru-shiru, sai suka jiyo wata murya daga baya,
"Da alama su ne can!"
Fawaaz ya zura zooming tool. Ya na ware ido, zuciyarsa na dukan uku-uku. A cikin wata ruguwar kwantaccen ciyayi da wasu tsofaffin bishiyoyi, ya hangi wasu mutane suna zaune kusa da wata karamar bukka. A tsakiyarsu, su Nabeehan sa ce!
Haj. Zaytunah tana zaune a gefe, tana rike da hannun Hammad da ke jin tsoro sosai. Nabeeha kuma tana a gefe, idonta cike da damuwa. Sai kuma wasu mutum biyu, Gora da Bala, waɗanda suke kallon gefe-gefe, suna jin wani irin damuwa.
Fawaaz ya dan zaro iska daga bakinsa, yana kokarin nutsuwa. Amma a zuciyarsa, yana jin wani irin ƙarfi da ƙwazo sun lullube shi.
"A shirya!" ya furta cikin sassanyar murya. "Zamu yi aiki mai tsabta. Nabeeha da sauran su na bukatar mu."
Babu wanda ya musa. Sun san cewa wannan aiki ne da ba za su bari ya gaza ba.
Fawaaz ya gyara rike bindigarsa, idonsa ya fi komawa kan Nabeeha. Ko da yake ba ta ganshi ba tukunna, amma ya san cewa cikin 'yan dakikoki, zai yi duk mai yiwuwa don ganin sun fita daga wannan wuri lafiya!
Fawaaz ya dan sunkuya yana lura da yanayin wurin. Binciken idanuwansa ya nuna masa cewa mutanen da suka yi garkuwa da su Nabeeha ba su da yawan makamai, amma hakan ba yana nufin ba su da hatsari ba. Ya san cewa su Gora da Bala mutane ne masu dabara, kuma ba zai yi ƙasa a gwiwa wajen yaƙar su ba.
Ya yi alama ga abokan aikinsa su zagaya ta bangarori daban-daban domin su mamaye yankin da dazukan uku da suka rage, kudu, gabas dana yamma, Lieutenant Ibrahim da Warrant Officer Suleiman sun kama hagu, yayin da sauran suka kama dama. Fawaaz ya cigaba da lurawa da yadda ake tafiyar da abubuwa daga inda suke..
Nabeeha tana zaune a gefen Hajiya Zaytunah, idanunta cike da damuwa. Hammad yana nan rike da hannunta, yana ta kallon gefe cike da tsoro. Gora yana tsaye kusa da Bala, yana magana da wani karamin walkie-talkie, yana kokarin tuntubar wani a waje.
"Hello...."
Daidai lokacin, Nabeeha ta ji zuciyarta tana wani irin bugawa. Ta rufe idanuwanta na wasu dakiku, tana jin kamar numfashinta zai dauke. Amma cikin wannan yanayi na tsoro, sai wani tunani ya fado mata… Fawaaz!
Bata ankara ba, sai kawai ta ji karar wani abu yana kara kusa da su ,kamar motsin mutane cikin daji. Idanunta suka kai kan Gora, wanda shima ya ji motsin.
"Me ke faruwa?" Bala ya tambaya yana kai hannu kan bindigarsa.
A daidai wannan lokacin, Fawaaz ya bayar da umarni cikin walkie-talkie,
"Roger that soldiers..Yanzu! Mu Shiga!"
Cikin gaggawa, sojojin suka fantsama daga bangarori daban-daban! Wani dan karamin fashewar hayaki ya biyo baya, wanda ya sa Bala da Gora suka rude, suna kokarin zaro makamai.
Fawaaz bai bata lokaci ba, ya shiga ta babban kofar bukkar cikin matsanancin sauri, bindigarsa a hannu, idanunsa suna kan Gora da Bala.
"Kada ku motsa!" ya daka musu tsawa.
Bala ya yi kokarin daga bindigarsa, amma kafin ya ankara, sai Lieutenant Ibrahim ya karbe bindigar daga hannunsa. Gora kuwa ya yi kokarin tserewa ta bayan bukkar, amma kafin ya iya, Warrant Officer Suleiman ya cafke shi da karfi, ya buga shi kasa.
Fawaaz bai damu da su ba, idanunsa sun sauka kai tsaye kan Nabeeha!
Zuciyarta ta buga da karfi, tana jin kamar numfashinta zai tsaya. A karo na farko, ta ji wani irin kwanciyar hankali da ta dade tana jira.
Fawaaz ya taka kusa da ita, yana kallonta ido cikin ido. Babu wanda ya ce uffan. Ya mika mata hannu a hankali, idanunsa cike da nutsuwa.
"Kin ji tsoro?" ya tambaye ta da murya mai laushi.
Nabeeha ta girgiza kai, amma idanuwanta sun nuna cewa ta ji tsoro fiye da yadda zata iya furtawa.
Ba tare da wata shakka ba, ya kama hannunta ya rike da kyau.
"Don't be...Ssshhh is okayy" ya furta.
A gefe guda, Hajiya Zaytunah ta runtse idanuwa, tana fitar da ajiyar zuciya. Hammad kuwa ya ruga ya rungume Captain Fawaaz da karfi, yana kuka da murna.
Fawaaz ya dan matsa daga gefe, yana tabbatar da cewa komai yana tafiya daidai. Sauran sojojin sun riga sun kama Gora da Bala, sun daure hannayensu da igiya, sannan suka rufe musu baki domin su guji yin hayaniya. A gefe guda, Lieutenant Ibrahim yana duba motar da masu garkuwar suka kawo, yana tabbatar da cewa babu wani abin fashewa ko tarkon da zai iya kawo hatsari.
Nabeeha har yanzu tana tsaye a wurin, zuciyarta na harbawa da karfi. Idanunta sun cika da ruwaye, ba wai saboda tsoro ba, amma saboda yawan damuwar da ta sha. Har yanzu tana jin yadda hannun Fawaaz ke rike da nata , rikon da ya tabbatar mata cewa yanzu tana cikin aminci.
Fawaaz ya dan sunkuya yana shafa kansa, sannan ya ce, "Su daina damunki, Zamu mika su hannun hukuma, za su fuskanci hukuncin da ya dace da su."
Hammad ya dan yi shiru na wasu dakiku, sai daga baya ya jinjina kai. "Mungode, Captain brother!"
Fawaaz bai ce komai ba, sai ya mike tsaye, ya nuna musu hanyar da za su bi zuwa motocin su. Sauran sojojin sun bi sawu, suna rike da Gora da Bala da aka daure su.
A daidai lokacin da suka fara tafiya, sai Fawaaz ya lura da yadda Nabeeha ke tafiya a hankali, kamar wacce ba ta da kwari sosai. Bai yi wata-wata ba, ya dan riko hannunta, yana tafiya tare da ita.
"Kin gaji?" ya tambaya, amma yana kallonta cikin ido.
Ta dan yi murmushi kadan, sannan ta ce, "Kadan dai."
Sai da suka soma tafiya kafin Nabeeha ta iya furta wani abu.
Fawaaz bai ce komai ba. Amma a zuciyarsa, ya san cewa zai iya yin komai don ganin cewa ba ta sake fuskantar irin wannan hatsari ba har abada.
Zuciyar Fawaaz tana daka da sauri fiye da yadda ya saba ji. Hannunsa yana rike da nata, amma har yanzu ba ya jin hakan ya wadatar. Idanunsa na tafiya a fuskarta, yana nazarin ta, yana neman wani alamun ciwo ko wahala.