Sashe 35
Kirjin Mai Hankali Part 2 Complete Hausa Novel · about 8 min read
A gefe guda, Hajiya Zaytunah na zaune da kai a kasa, zuciyarta cike da tunani. Shekaru da yawa da suka shude, ta san ba za ta iya komawa gidan Alhaji Uzairu ba a tunanintaa, kuma yanzu da aka buɗe sabon shafi a rayuwarta, dole ta yanke shawarar da ta dace. Nabeeha da Hammad kuwa suna zaune kusa da ita, suna kallon kowa da kowa a falon, ba tare da sanin abin da ke tafe ba.
Gwaggo Hafsatu ce ta katse shiru da wata kakkausar murya,
“wannan hutun mai dogon zango. Inshaa Allah a birnin mawii zamuyi shi.”
Kowa ya kalleta. Major general yadan gyara zamansa, yana jiran jin dalilinta.
"Dawuda yana da katafaren gida a can, gida ne da zai iya daukar su Zaytunah da ‘ya’yanta cikin kwanciyar hankali. Babu wanda zai takura musu ko ya binciko su, babu wanda zai dinga bibiyar rayuwarsu. Idan muna so su sami sabuwar rayuwa, to Mawii shine mafita.”
" hakan zai fi dacewa,” ya fada a hankali. “Ni kaina ba na so su zauna a nan, saboda idan SIRRIN ya tonu, za mu shiga matsala.”
Hajiya zaytunah ta dago kai a hankali.
"Gwaggo, kina nufin mu bar noka gaba daya?”
“Eh, Zaytunah,” Gwaggo Hafsatu ta fada da karfin gwiwa. “Dole mu fice, saboda noka ba wurin da zai ba ki kariya bane. Na gama magana da Dawuda, ya shirya mana komai.”
Nabeeha ta kalli mahaifiyarta da mamaki. Komawa wani gari daban? Wata sabuwar rayuwa? Ta kalli Hammad, shima yana kallon ta, tamkar yana jiran jin ra’ayinta.
"Tohm gwaggo abunda kika yanke shi za'ai. Allah dai ya Saka muku da alkhairi. Yasa komawar tamu canne mabudin alkhairan mu gaba daya Amin"
"Aameen" suka hada baki wajen amsa ta.
___-----____
Bayan kwana biyu da tunani da shawarwari, Major General Dawud ya yanke shawarar kira Alhaji Amiru domin su yi wata muhimmiyar ganawa. A lokacin yana zaune a cikin ofishinsa, cikin tsanaki ya dauki wayarsa ya danna lambobin Alhaji Amiru.
Da alama yana jiran kiran, domin kuwa cikin ‘yan kara-kaushe Alhaji Amiru ya daga wayar.
"Salamu alaikum, Major General." Muryarsa da karfin gwiwa kamar yadda aka santa, sai dai akwai dan nutsuwa cikin ta.
"Wa’alaikumus salam, Alhaji Amiru. Ina fata kana lafiya?"
"Alhamdulillah. Yaya aiki?"
"Alhamdulillah. Akwai magana da nake so mu yi, idan baka da wani uzuri, acikin tsukukun nan. Zan neme ka"
Shiru na dan lokaci ya biyo baya. Alhaji Amiru ya fahimci cewa maganar dole ce, kuma ba zai yi mata rikon sakainar kashi ba.
"Babu matsala, Major General. in Allah Ya yarda."
"Shikenan.sai ka jini."
Bayan kammala kiran, Major General Dawud ya sauke numfashi. Yana da tabbacin cewa wannan ganawar za ta tsayar da shawarwarin da suka dauka a gida game da Zaytunah da ‘ya’yanta.
....
A yini biyu da suka gabata, an yi zaman shawarwari mai tsawo a gidan Major General Dawud. Gwaggo Hafsatu ce ta sake kira zaman, inda ta bukaci a zauna a sake tattauna batun komawar Hajiya Zaytunah da iyalanta zuwa wani wuri mafi tsaro da kwanciyar hankali.
"Na dade ina addu’ar Allah Ya yi mana jagora," cewar Gwaggo Hafsatu, tana kallon Major General Dawud da Hajiya Zaytunah. "Duk da haka, ba zan yanke hukunci ba sai da amincewarki, Zaytunah."
Hajiya Zaytunah ta sauke numfashi, tana dan gyara zamanta. "Gwaggo, ni babu abin da nake so sama da kwanciyar hankali ga ‘ya’yana. Amma har yanzu ba zan iya komawa gidan Alhaji Uzairu ba. Komai yana nan yadda na bari."
"Mun fahimta," Major General Dawud ya katse shurun da ya biyo bayan maganarta. "Akwai wani wuri da muke son mu kaisu, Birnin Mawii. Gida ne da aka tanada tun tuni kamar yadda aka fada a baya, amma yanzu ne zai fi dacewa da su."
Hajiya Zaytunah ta daga ido tana kallonsa. "Birnin Mawii?"
"Eh. Gida ne mai tsaro da kwanciyar hankali. Ba kowa zai iya gane su can ba, kuma za su sami damar sake farawa da sabuwar rayuwa."
Shiru ya sake ratsa dakin, kafin daga bisani Hajiya Zaytunah ta gyada kai a hankali. "Idan hakan ne mafi alheri gare mu, to na amince."
Washegari kuwa, aka fara shiri don fice wa cikin SIRRI da kwanciyar hankali.
🎀🎀🎀
Major General Dawud mutum ne mai kamun kai, wanda ya fi so abubuwa su tafi yadda ya tsara su. Bai cika barin wayarsa a ko’ina ba, domin yana da matukar kula da SIRRIN SA. Amma yau, kwatsam, yana dawowa daga sashen mahaifiyarsa, Gwaggo Hafsatu, ya shiga dakinsa ne ba tare da tsammani ba, sai ya ci karo da wani abin da ya kada masa gwiwa.
A kusa da gadonsa, Hajiya Hawwa Maijiddah na zaune da wayarsa a hannunta. Ba wai tana kallonta ba ne kawai, a’a, Tana rubuta wata lamba a nata wayar!
Da farko, bai ce komai ba. Ya tsaya a bakin kofa, yana nazarin lamarin. Ya lura yadda ta mayar da hankali sosai, tana ta dannawa cikin hanzari kamar wacce ke tsaka da wata gaggawar aiki.
Da sauri ya kutsa cikin dakin, zuciyarsa na bugawa. "Hawwa!" Ya kira da murya mai karfi, amma ba tare da hayaniya ba.
Da sauri ta daga kai, idonta cike da firgici. Kafin ta samu damar ɓoye abin da take yi, ya karaso ya kwace wayarta.
"Meye haka?" Ya tambaya da karfi, yana kallon wayarta.
Tana kokarin mayar da nutsuwa, amma jikinta ya nuna cewa an kamata. "Uh… Ni dai kawai… na duba wani abu ne."
"Duba wani abu?" Ya maimaita, yana duba fuskar wayarta. ya duba fuskar wayar Hajiya Hawwa Maijiddah, idonsa ya tsime kan jerin sakonni da ta tura. Bai tsaya bata lokaci ba, ya danna kiran baya (recent messages). Cikin ikon Allah, sakon da ta tura bai riga ya goge ba.
A yayin da ya karanta, fuskar sa ta nuna tsananin bacin rai. Har gaban zuciyarsa yaji wani irin daci.
"Wannan shine babban shirin su. Za a mayar da ita da ‘ya’yanta wani area dake garin ku na mawi.. Gida ne na SIRRI da aka tanada tun tuni, amma yanzu ne za a kaisu. Za a yi tafiya cikin SIRRI."
Hannunsa ya fara matse wayar da karfi, idanuwansa suka kada.
Ya dago kai a hankali, yana kallon Hajiya Hawwa Maijiddah da take kokarin boye firgicinta.
"Hawwa, wa kike tura wa wannan sakon?"
Muryarsa cike da tsawa, da wata irin natsuwa mai hade da fushin da ba kasafai ake ganin shi da shi ba.
"Ni… Ni… Wallahi… Ba wani abu bane" Ta fara kokarin magana, amma muryarta na rawa.
"Ba wani abu bane? Kina fadawa wani SIRRIn da ni da Gwagggo muka dauki tsawon lokaci muna kiyaye shi, sannan kice ba wani abu bane?!"
Ya nuna mata wayarta da ke hannunsa, yana mai nuna mata sakon da ta tura.
"Daga ina kika samu wannan number.. shinma Wa kike turawa, Two face?? Fuska biyu hauwa?!"
Tayi shiru. Jikinta har rawa yake yi. Idanuwanta sun cika da ruɗani. A yadda ta san shi, idan yana cikin fushi irin wannan, babu mai iya hanashi daukar mataki.
Ya dauki tsawon lokaci yana kallonta, zuciyarsa na tafasa. Wata zuciyar tana gaya masa ya mata tambayoyi da ladabi, wata kuma tana gaya masa cewa babu sauran lokacin sassauci.
Ya kai hannu ya dauki wayarsa, yana dubawa don ganin ko ta duba wasu bayanai a cikinta. Bai jima ba, ya gano cewa ta shiga cikin saƙon wayarsa, tana duba sakonninsa da kuma lambobin da suka shafi Zaytunah da iyalanta.
"Whattttttt!" Ya furta a hankali, amma muryarsa ta kara tsananta.
Yayi kokarin bin lambobin da ke cikin wayarta, yana nazari kan wanda take tura wa wadannan sakonni. Amma hakan bai samu ba cikin sauki. Amma abu daya ya bayyana, wannan lambar ba sabuwa bace. Wani mutum ne da take da alaƙa da shi tun baya.
Da sauri ya kalle ta, yana kokarin gano amsar tambayoyin da zuciyarsa ke yi.
"Waye wannan? Waye kike turawa wannan bayanai?"
Hajiya Hawwa Maijiddah ta sunkuyar da kanta, tana kokarin kaucewa kallon idanunsa.
"Daga yau, kada ki kuskura ki kara taba wayata!" Ya furta da kakkausar murya, yana jefar da wayarta akan gadonta.
"Duk wani abu da kike shiryawa, na tabbatar ba zai yiwu ba."
Ya juya, zuciyarsa cike da tunani. Wannan abu ba zai wuce haka kawai ba. Zai bincika komai ko da kuwa hakan yana nufin zai bankado wani SIRRI mafi muni fiye da wanda ya gani yanzu. Shi ya Saka ma ba zai dauki hukunci ba anan take. Sai ya gama bincike ya futarda sakamakon bincikensa...
ADVERT👇
YERWA INCENSE AND MORE
YERWA INCENSE AND MORE
YERWA INCENSE AND MORE
(THE SCENTS WITH DIFFERENT ESSENCE FOR YOU AND YOUR HOME)
(MASARAUTAR KAYAYYAKIN KAMSHI)
INA MA'ABOTA TURARE!
Shin kuna son gida mai ƙamshi da nutsuwa? Kaya masu ɗaukar hankalin kowa? YERWA INCENSE AND MORE ta kawo muku kayayyakin turaruka masu kyau, ingantattu, da tsada mai rahusa!
🌟 Mene ne za ku samu?
Turarukan wuta don gida, kaya, da tsugunno.
Khumrahs masu kamshi irin na Borno, Chadi, da Sudan.
Oil perfumes masu daɗin kamshi mai ɗorewa.
Turaren wanka, mopping, da wanki don dukkan sassan gida.
Man gashi mai gyara da fesa kamshi mai dadi.
Kayayyakin gyaran jiki na musamman don lafiya da ƙamshi mai ɗorewa.
📍 Adireshi:
Kano, amma muna tura kayayyakin mu duk fadin Najeriya da ƙetare.
📞 Tuntuɓe mu:
WhatsApp ko kira: 08095215215 / 09044191709 / 09134848107
Instagram: @yerwaincense_and_more
Facebook: @yerwacollection
Twitter:Hafsaaat00
🌐 Don ƙarin bayani da hotunan kayayyakin mu: Ku ziyarta mu a TikTok:
@besturarenwutainkano
https://www.tiktok.com/@besturarenwutainkano?_t=ZM-8s89xrbgS3x&_r=1
🎉 DON RAGI NA MUSAMMAN: Idan za ku siya, ku faɗi cewa daga ZAFAFA ne!
🌹 Ku more gida da jiki mai kamshi, nutsuwa, da farin ciki. Sai dai kayan turaren YERWA INCENSE AND MORE!
*KIRJIN MAI HANKALI*
_(Akwatin sirrin sa)_
_🧳👩❤️👨🌺_
*_The Vault Of His Secrets_*
_®️NANA HAFSATU (MX)_
_©️ZAFAFA BIYAR WRITERS_
*_BOOK TWO_*
_PAGE:32_
Major General Dawud ya yi numfashi mai nauyi, zuciyarsa na tafasa da tunani. Bai taba zaton Hajiya Hawwa Maijiddah zata iya aikata irin wannan ba. Ya san cewa ba ta cika jin dadin zaman Zaytunah a gidan ba, amma bai yi tsammanin cewa za ta kai ga tona SIRRIN da aka dauki lokaci ana boyewa ba.
Gwaggo Hafsatu ce ta katse shiru da wata kakkausar murya,
“wannan hutun mai dogon zango. Inshaa Allah a birnin mawii zamuyi shi.”
Kowa ya kalleta. Major general yadan gyara zamansa, yana jiran jin dalilinta.
"Dawuda yana da katafaren gida a can, gida ne da zai iya daukar su Zaytunah da ‘ya’yanta cikin kwanciyar hankali. Babu wanda zai takura musu ko ya binciko su, babu wanda zai dinga bibiyar rayuwarsu. Idan muna so su sami sabuwar rayuwa, to Mawii shine mafita.”
" hakan zai fi dacewa,” ya fada a hankali. “Ni kaina ba na so su zauna a nan, saboda idan SIRRIN ya tonu, za mu shiga matsala.”
Hajiya zaytunah ta dago kai a hankali.
"Gwaggo, kina nufin mu bar noka gaba daya?”
“Eh, Zaytunah,” Gwaggo Hafsatu ta fada da karfin gwiwa. “Dole mu fice, saboda noka ba wurin da zai ba ki kariya bane. Na gama magana da Dawuda, ya shirya mana komai.”
Nabeeha ta kalli mahaifiyarta da mamaki. Komawa wani gari daban? Wata sabuwar rayuwa? Ta kalli Hammad, shima yana kallon ta, tamkar yana jiran jin ra’ayinta.
"Tohm gwaggo abunda kika yanke shi za'ai. Allah dai ya Saka muku da alkhairi. Yasa komawar tamu canne mabudin alkhairan mu gaba daya Amin"
"Aameen" suka hada baki wajen amsa ta.
___-----____
Bayan kwana biyu da tunani da shawarwari, Major General Dawud ya yanke shawarar kira Alhaji Amiru domin su yi wata muhimmiyar ganawa. A lokacin yana zaune a cikin ofishinsa, cikin tsanaki ya dauki wayarsa ya danna lambobin Alhaji Amiru.
Da alama yana jiran kiran, domin kuwa cikin ‘yan kara-kaushe Alhaji Amiru ya daga wayar.
"Salamu alaikum, Major General." Muryarsa da karfin gwiwa kamar yadda aka santa, sai dai akwai dan nutsuwa cikin ta.
"Wa’alaikumus salam, Alhaji Amiru. Ina fata kana lafiya?"
"Alhamdulillah. Yaya aiki?"
"Alhamdulillah. Akwai magana da nake so mu yi, idan baka da wani uzuri, acikin tsukukun nan. Zan neme ka"
Shiru na dan lokaci ya biyo baya. Alhaji Amiru ya fahimci cewa maganar dole ce, kuma ba zai yi mata rikon sakainar kashi ba.
"Babu matsala, Major General. in Allah Ya yarda."
"Shikenan.sai ka jini."
Bayan kammala kiran, Major General Dawud ya sauke numfashi. Yana da tabbacin cewa wannan ganawar za ta tsayar da shawarwarin da suka dauka a gida game da Zaytunah da ‘ya’yanta.
....
A yini biyu da suka gabata, an yi zaman shawarwari mai tsawo a gidan Major General Dawud. Gwaggo Hafsatu ce ta sake kira zaman, inda ta bukaci a zauna a sake tattauna batun komawar Hajiya Zaytunah da iyalanta zuwa wani wuri mafi tsaro da kwanciyar hankali.
"Na dade ina addu’ar Allah Ya yi mana jagora," cewar Gwaggo Hafsatu, tana kallon Major General Dawud da Hajiya Zaytunah. "Duk da haka, ba zan yanke hukunci ba sai da amincewarki, Zaytunah."
Hajiya Zaytunah ta sauke numfashi, tana dan gyara zamanta. "Gwaggo, ni babu abin da nake so sama da kwanciyar hankali ga ‘ya’yana. Amma har yanzu ba zan iya komawa gidan Alhaji Uzairu ba. Komai yana nan yadda na bari."
"Mun fahimta," Major General Dawud ya katse shurun da ya biyo bayan maganarta. "Akwai wani wuri da muke son mu kaisu, Birnin Mawii. Gida ne da aka tanada tun tuni kamar yadda aka fada a baya, amma yanzu ne zai fi dacewa da su."
Hajiya Zaytunah ta daga ido tana kallonsa. "Birnin Mawii?"
"Eh. Gida ne mai tsaro da kwanciyar hankali. Ba kowa zai iya gane su can ba, kuma za su sami damar sake farawa da sabuwar rayuwa."
Shiru ya sake ratsa dakin, kafin daga bisani Hajiya Zaytunah ta gyada kai a hankali. "Idan hakan ne mafi alheri gare mu, to na amince."
Washegari kuwa, aka fara shiri don fice wa cikin SIRRI da kwanciyar hankali.
🎀🎀🎀
Major General Dawud mutum ne mai kamun kai, wanda ya fi so abubuwa su tafi yadda ya tsara su. Bai cika barin wayarsa a ko’ina ba, domin yana da matukar kula da SIRRIN SA. Amma yau, kwatsam, yana dawowa daga sashen mahaifiyarsa, Gwaggo Hafsatu, ya shiga dakinsa ne ba tare da tsammani ba, sai ya ci karo da wani abin da ya kada masa gwiwa.
A kusa da gadonsa, Hajiya Hawwa Maijiddah na zaune da wayarsa a hannunta. Ba wai tana kallonta ba ne kawai, a’a, Tana rubuta wata lamba a nata wayar!
Da farko, bai ce komai ba. Ya tsaya a bakin kofa, yana nazarin lamarin. Ya lura yadda ta mayar da hankali sosai, tana ta dannawa cikin hanzari kamar wacce ke tsaka da wata gaggawar aiki.
Da sauri ya kutsa cikin dakin, zuciyarsa na bugawa. "Hawwa!" Ya kira da murya mai karfi, amma ba tare da hayaniya ba.
Da sauri ta daga kai, idonta cike da firgici. Kafin ta samu damar ɓoye abin da take yi, ya karaso ya kwace wayarta.
"Meye haka?" Ya tambaya da karfi, yana kallon wayarta.
Tana kokarin mayar da nutsuwa, amma jikinta ya nuna cewa an kamata. "Uh… Ni dai kawai… na duba wani abu ne."
"Duba wani abu?" Ya maimaita, yana duba fuskar wayarta. ya duba fuskar wayar Hajiya Hawwa Maijiddah, idonsa ya tsime kan jerin sakonni da ta tura. Bai tsaya bata lokaci ba, ya danna kiran baya (recent messages). Cikin ikon Allah, sakon da ta tura bai riga ya goge ba.
A yayin da ya karanta, fuskar sa ta nuna tsananin bacin rai. Har gaban zuciyarsa yaji wani irin daci.
"Wannan shine babban shirin su. Za a mayar da ita da ‘ya’yanta wani area dake garin ku na mawi.. Gida ne na SIRRI da aka tanada tun tuni, amma yanzu ne za a kaisu. Za a yi tafiya cikin SIRRI."
Hannunsa ya fara matse wayar da karfi, idanuwansa suka kada.
Ya dago kai a hankali, yana kallon Hajiya Hawwa Maijiddah da take kokarin boye firgicinta.
"Hawwa, wa kike tura wa wannan sakon?"
Muryarsa cike da tsawa, da wata irin natsuwa mai hade da fushin da ba kasafai ake ganin shi da shi ba.
"Ni… Ni… Wallahi… Ba wani abu bane" Ta fara kokarin magana, amma muryarta na rawa.
"Ba wani abu bane? Kina fadawa wani SIRRIn da ni da Gwagggo muka dauki tsawon lokaci muna kiyaye shi, sannan kice ba wani abu bane?!"
Ya nuna mata wayarta da ke hannunsa, yana mai nuna mata sakon da ta tura.
"Daga ina kika samu wannan number.. shinma Wa kike turawa, Two face?? Fuska biyu hauwa?!"
Tayi shiru. Jikinta har rawa yake yi. Idanuwanta sun cika da ruɗani. A yadda ta san shi, idan yana cikin fushi irin wannan, babu mai iya hanashi daukar mataki.
Ya dauki tsawon lokaci yana kallonta, zuciyarsa na tafasa. Wata zuciyar tana gaya masa ya mata tambayoyi da ladabi, wata kuma tana gaya masa cewa babu sauran lokacin sassauci.
Ya kai hannu ya dauki wayarsa, yana dubawa don ganin ko ta duba wasu bayanai a cikinta. Bai jima ba, ya gano cewa ta shiga cikin saƙon wayarsa, tana duba sakonninsa da kuma lambobin da suka shafi Zaytunah da iyalanta.
"Whattttttt!" Ya furta a hankali, amma muryarsa ta kara tsananta.
Yayi kokarin bin lambobin da ke cikin wayarta, yana nazari kan wanda take tura wa wadannan sakonni. Amma hakan bai samu ba cikin sauki. Amma abu daya ya bayyana, wannan lambar ba sabuwa bace. Wani mutum ne da take da alaƙa da shi tun baya.
Da sauri ya kalle ta, yana kokarin gano amsar tambayoyin da zuciyarsa ke yi.
"Waye wannan? Waye kike turawa wannan bayanai?"
Hajiya Hawwa Maijiddah ta sunkuyar da kanta, tana kokarin kaucewa kallon idanunsa.
"Daga yau, kada ki kuskura ki kara taba wayata!" Ya furta da kakkausar murya, yana jefar da wayarta akan gadonta.
"Duk wani abu da kike shiryawa, na tabbatar ba zai yiwu ba."
Ya juya, zuciyarsa cike da tunani. Wannan abu ba zai wuce haka kawai ba. Zai bincika komai ko da kuwa hakan yana nufin zai bankado wani SIRRI mafi muni fiye da wanda ya gani yanzu. Shi ya Saka ma ba zai dauki hukunci ba anan take. Sai ya gama bincike ya futarda sakamakon bincikensa...
ADVERT👇
YERWA INCENSE AND MORE
YERWA INCENSE AND MORE
YERWA INCENSE AND MORE
(THE SCENTS WITH DIFFERENT ESSENCE FOR YOU AND YOUR HOME)
(MASARAUTAR KAYAYYAKIN KAMSHI)
INA MA'ABOTA TURARE!
Shin kuna son gida mai ƙamshi da nutsuwa? Kaya masu ɗaukar hankalin kowa? YERWA INCENSE AND MORE ta kawo muku kayayyakin turaruka masu kyau, ingantattu, da tsada mai rahusa!
🌟 Mene ne za ku samu?
Turarukan wuta don gida, kaya, da tsugunno.
Khumrahs masu kamshi irin na Borno, Chadi, da Sudan.
Oil perfumes masu daɗin kamshi mai ɗorewa.
Turaren wanka, mopping, da wanki don dukkan sassan gida.
Man gashi mai gyara da fesa kamshi mai dadi.
Kayayyakin gyaran jiki na musamman don lafiya da ƙamshi mai ɗorewa.
📍 Adireshi:
Kano, amma muna tura kayayyakin mu duk fadin Najeriya da ƙetare.
📞 Tuntuɓe mu:
WhatsApp ko kira: 08095215215 / 09044191709 / 09134848107
Instagram: @yerwaincense_and_more
Facebook: @yerwacollection
Twitter:Hafsaaat00
🌐 Don ƙarin bayani da hotunan kayayyakin mu: Ku ziyarta mu a TikTok:
@besturarenwutainkano
https://www.tiktok.com/@besturarenwutainkano?_t=ZM-8s89xrbgS3x&_r=1
🎉 DON RAGI NA MUSAMMAN: Idan za ku siya, ku faɗi cewa daga ZAFAFA ne!
🌹 Ku more gida da jiki mai kamshi, nutsuwa, da farin ciki. Sai dai kayan turaren YERWA INCENSE AND MORE!
*KIRJIN MAI HANKALI*
_(Akwatin sirrin sa)_
_🧳👩❤️👨🌺_
*_The Vault Of His Secrets_*
_®️NANA HAFSATU (MX)_
_©️ZAFAFA BIYAR WRITERS_
*_BOOK TWO_*
_PAGE:32_
Major General Dawud ya yi numfashi mai nauyi, zuciyarsa na tafasa da tunani. Bai taba zaton Hajiya Hawwa Maijiddah zata iya aikata irin wannan ba. Ya san cewa ba ta cika jin dadin zaman Zaytunah a gidan ba, amma bai yi tsammanin cewa za ta kai ga tona SIRRIN da aka dauki lokaci ana boyewa ba.