Sashe 85
Kallon Kitse Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Ina shirin hawa adaidaita sahu na ji an shak'o hijabina na dawo baya, wazan gani in ba Umar faruk ba da hijabi na a hannu, Saif da Marwan sune masu sanyin ciki sune suka ce ya sake min hijabi tunda ni ma fa ba kara zube ni ke ba ina da aure, saki na ya yi amma Abbas yace "Wallahi ko kije ki fad'a mu su k'arya ki ke ko kuma mu kwana anan mu da ke."
Ahmad ne yace "Ai ba maganar mu kwana anan bane, magana ce ta muje gidanta a matsayin samarinta ma su son ta."
😂 *Ahmad ko bala'i*
Jin haka ya sa na ce su yi hak'uri mu tafi na fad'a mu su gaskiya dan ina son *beby na* ni ma, haka suka tasoni a gaba na zo na fad'a mu su kawai dan raha ne, saida magana ta fara lafawa sai kawai muryar Usman naji yace "Abokai ku taimaka ku tafar min da matar nan dan Allah, dan nima ta d'an fara damu na, sam bata bari mutum ya yi sirri da matarsa."
Murgud'a masa baki na yi na ce " To babu in da zanje sai na k'arashe labarin har k'arshe sannan."
Cikin fad'a Usman yace "To zan gani idan gidanki ne ko nawa."
"Gidanka ne amma babu in da zata je har sai ta k'arasa abin da ta fara." Cewar Khadija, turo baki yayi kamar zaiyi kuka amma bai ce komai ba, nima cewa na yi "Zan tafi yanzu dai saboda na gaji, amma zanyi sammakon zuwa gobe da safe."
Dukansu hannu suka d'aga min suna min bye bye da cewa "Saida safe Meranmu."
Haka na bar wurin cike da kewar *jarumai na* ko ba komai ina jin dad'in zama tare da su, da haka suma su ka ci gaba da walimar su har aka yanka panke dare ya yi sosai kafin Usman ya samawa kowa makwanci mai rai da lafiya ya kwanta dan huta gajiya, haka duka ma'auratan suka kwanta suna soyayyarsu dan har yanzu akwai wanda basu san sun girma ba.
*Asuba ta gari*
Daga lokacin suka fara jego cike da gata da kulawa, a yanzu idan kaga zaman na gidan Usman saiya baka mamaki, duk da har yanzu suna jin kishi amma dai ba kamar baya ba, haka suke tasa Usman gaba su dinga masa k'iriniya shi kuma yana biye musu, rayuwar ta musu dad'i yanzu kuma sun fahimci zama lafiya yafi zama d'an sarki, a haka rayuwa da lokaci ke tafiya girma na k'ara zuwa musu, Haseenah k'iba take tayi abinta saboda kwanciyar hankali da hutu, amma Khadija har yanzu tana nan yanda take bata rage ba bata k'ara ba, a haka sherau su ka je sosai har shekara *goma sha biyar*.
A wannan shekarun abubuwa da dama sun faru masu dad'i da marasa dad'i, daga ciki akwai rasuwar su malam da Hajia, haka ma mamar Khadija ta rasu sakamakon rashin lafiya, haka mahaifin Haseenah ma ya rasu sai maman su wacce tsufa yasa ko yayanta bata ganewa, da haka kusan dukansu suka zama marayu suna kuma kula da junansu sosai, abun farin ciki kuma akwai haihuwa har biyar da Haseenah ta k'ara bayan Aisha, kuma dukansu mata ne sai auta shi kad'ai ne namiji wanda ya ci sunan *Ali* amma suna kiranshi *Khalifa*, kuma wacce yake biwa ita aka wa Khadija kara aka sawa sunan mahaifiyarta *Sadiya* ita ma suna kiranta da *Nawwal*, hakama hajia an mata takwara *Hawa'u* wacce akewa alkunya da *Noor*, sannan daga ciki akwai kammala karatu da bilal ya yi a k'asar *Canada*, amma har yanzu Khadija bata sake haihuwa ba daga Humaira, amma kaf yaran Haseenah ita ke kula da su kamar ita ta haifesu, a haka Bilal ya dawo ya zama cikakken saurayi son kowa k'in wanda rasa, matashin saurayi kyakyawa kuma miskilin yaro mai d'auke da shekaru *ashirin da bakwai*, hakan yasa Usman damka duk ragamar gidan hannu Bilal, a cewar shi aure zai mi shi nan da d'an lokaci kad'an, wannan damar da Bilal ya samu tasa yake juya komai na gidan har iyayen mata, shi ya sa yanzu kullum gidan cikin hayaniya suke saboda Bilal dai baisan yawan surutu, yau ma kamar kusan kullum Aisha da Humaira ne suka shirya dan auwa bikin k'awar su, masha Allah yan matan Khadija kenan, tabbas shak'uwa dake tsakaninsu tasa har suke kama sosai ta fuska da yanayi, sai dai Humaira tafi haske sosai da dogon hanci sannan tafi cikar hallita da kumari, kayan jikinsu ma iri d'aya ne haka suka nufi d'akin Bilal dake sama dan karb'o makullin mota su bawa drebansu ya kaisu, da sallama suka tura k'ofar Humaira ce gaba.
Kwance yake ruf da ciki babu riga a jikinshi sai dogon wando dake d'aure da d'amara (belt), saida suka tsaya kanshi Humaira tace "Yah Bilal makullin mota za ka bamu mun shirya."
Shiru kamar baiji ba, Aisha ce ta kama hannun Humaira tace "Kinga mu fita wallahi bana so ya tashi ya mana tsinannan duka."
Fizge hannunta tayi tace "Ke wallahi kin cika tsoro, kawai saiya doke mu daga wannan maganar."
Kallonshi tayi ta sake cewa "Ya Bilal magana muke fa."
A hankali ya juyo tare da tashi zaune yana kallonsu, saida ya gama kallonsu yace "Ku rufe k'ofar d'akin sai ku zo ku karb'i makullin."
Kallon juna su ka yi saboda sun san me ya ke nufi da abin da ya fad'a, zare ido su ka fara yi kafin ya sake daka musu tsawa yace "Na ce ku rufe k'ofar ko."
Haba wa ai da gufu suka fita suna rige-rige, Allah ne ya saukesu k'asa lafiya basu zama ko ina ba sai falon Usman, kamar an turosu haka suka fad'a d'akin, kowace wajen ta ta uwar ta nufa wacce tasan zata tsaya mata, Humaira wajen Haseenah Aisha wajen Khadija, wata cakuma da Aisha tawa Khadija yasa d'an kwalinta fad'uwa kan kujera hakan ya bayyanar da yar furfurar dake kan ta wacce ba'a ganinta sosai ma, Khadija ce tace "Kai Aisha ho, wannan ba sai ki karyani ba, lafiya me ya faru?"
Haseenah da sai wani k'ara rumgume Humaira take ne tace "Ai da gani ba tambaya kinsan su da wannan yariman mai gida."
Khadija ce tace "Wallahi al'amarin nan ya fara isata fa, gaba d'aya yaron nan ya hana min yarinya sakewa a gida."
"Ai ba laifinshi bane, laifin wanda ya bashi muk'amin ne a gidan." Cewar Usman daya fito daga d'akin shi tare da sauran yaran sunata gurgurar chocolat, hakan ma yayi daidai da shigowar Bilal ya sanyo farar riga wacce ta kamashi, tabbas ko kad'an Bilal baiyi kama da mahaifinshi ba saboda k'irar jikinshi ma ta k'akk'arfan maza ce kusan zaka iya cewa ma kawunshi ne yayi Habeeb, saidai kyawun mahaifiyarshi da yayi kawai da manyan idanunta, belt d'in dake hannunshi ya nad'e ya yo kan Aisha zai tsala mata ta sake shigewa jikin Khadija, Khadija ce tace "Allah ka daketa sai ranka ya b'ace, kaji marar kunya kai, kai baka ji ance ko mutuwa tana kunyar idon mahaifi ba."
Juyawa yayi ya kalli Humaira hakan yasa Haseenah cewa "Karma ka fara matsowa nan kaji na fad'a maka."
Usman ne yace "Yarima meya faru? Laifin me su ka yi?" Cikin b'acin rai yace "Abba nasha fad'awa yaran nan su daina shigar min d'aki idan ban musu izinin shiga ba,yanzu fa haka kawai suka suka fad'a min d'aki ina kwance ba riga a jiki na."
Khadija ce ta katse da cewa "To shine zaka dake su? Ba sai ka sake musu nasiha ba, kaji sai kace wani gudan babban mutum, yaushe ne aka daina saka maka kaya."
Usman ne yace "Koma yau ne aka daina saka mi shi ai dai an daina saka mi shi saboda ya wuce munzalin, dan haka dole ya hukuntasu tunda sun k'i su san daidai da ba daidai ba."
Kallonshi Khadija tayi ta motsa bakinta hakan yasa Usman yace "Naji ki kamani amma bayan na mik'awa yarima na wannan yaran nan na bayanku."
Wata dariya Haseenah ta yi tace "Kana ganin zaka iya k'watar su a hannun mu ne?"
Wani kallo ya mata yace "Kin manta da k'ashi d'aya ne gareni, bugu d'aya zan mu ku kuji ku a makara."
Dariya Khadija tayi tace "To ina zaka zauna kai kuma?"
"A duniya mana." Ya fad'a ya na zama kusa da su, Haseenah ce tace "Kenan ka fara soyayya a waje bamu sani ba."
Shafa kanshi yayi da ya kusan cika da furfura yace "Ai wasu kyawawan yan mata na samu suka mak'ale min wai ni suke so, kuma na yi alk'awarin aurensu, ai yarima ma zai zama waliyi na."
Dariya suka saka a tare sai Khadija da tace "Komawa baya kenan, to idan zaka je d'aurin auren dai ka shafa gawayi a kanka danka rufe wannan farin abun na kan ka."
Sake shafa kan yayi yace "Alamar arzik'i ne ai, kuma naga kema akwaita a kanki."
Cike da k'aguwa Bilal yace "wai yanzu na zo da matsalata amma ku manta kun shiga sabgar gabanku, Allah ya shirya min ku iyayena, banda kamarku a duniyar nan."
Harya juya zai fita ya tsaya ya nuna su Humaira da yatsa yace "Kuma wallahi babu inda za ku je, na gaji da wannan yawan na ku kullum."
Khadija ce tace "To ni ka ban makullin tawa motar zan fita, ai dai kasan aro ne na baka jiya ko."
Kallon Usman yayi yace "Idan sarki ya bayar da izinin fita sai ku fad'a min zan kawo mu ku."
Cike da jin dad'i Usman ya aika mishi da sumbata yace "Allah ya maka albarka yarona, shi ya sa banda matsala da gidan nan ko bana nan nasan akwai original Usman a gidan, da ni ne da yanzu sun min fari da ido na basu makullan."
Fita yayi daga d'akin sai Usman daya kalli su Aisha yace "Ku kuma ki fito daga nan munafukai kawai, dama da kinga suna raba ido kinsan basu da gaskiya, kuma wallahi ku ka sake shigar masa d'aki ba neman izini da kaina zan hukuntaku."
Ahmad ne yace "Ai ba maganar mu kwana anan bane, magana ce ta muje gidanta a matsayin samarinta ma su son ta."
😂 *Ahmad ko bala'i*
Jin haka ya sa na ce su yi hak'uri mu tafi na fad'a mu su gaskiya dan ina son *beby na* ni ma, haka suka tasoni a gaba na zo na fad'a mu su kawai dan raha ne, saida magana ta fara lafawa sai kawai muryar Usman naji yace "Abokai ku taimaka ku tafar min da matar nan dan Allah, dan nima ta d'an fara damu na, sam bata bari mutum ya yi sirri da matarsa."
Murgud'a masa baki na yi na ce " To babu in da zanje sai na k'arashe labarin har k'arshe sannan."
Cikin fad'a Usman yace "To zan gani idan gidanki ne ko nawa."
"Gidanka ne amma babu in da zata je har sai ta k'arasa abin da ta fara." Cewar Khadija, turo baki yayi kamar zaiyi kuka amma bai ce komai ba, nima cewa na yi "Zan tafi yanzu dai saboda na gaji, amma zanyi sammakon zuwa gobe da safe."
Dukansu hannu suka d'aga min suna min bye bye da cewa "Saida safe Meranmu."
Haka na bar wurin cike da kewar *jarumai na* ko ba komai ina jin dad'in zama tare da su, da haka suma su ka ci gaba da walimar su har aka yanka panke dare ya yi sosai kafin Usman ya samawa kowa makwanci mai rai da lafiya ya kwanta dan huta gajiya, haka duka ma'auratan suka kwanta suna soyayyarsu dan har yanzu akwai wanda basu san sun girma ba.
*Asuba ta gari*
Daga lokacin suka fara jego cike da gata da kulawa, a yanzu idan kaga zaman na gidan Usman saiya baka mamaki, duk da har yanzu suna jin kishi amma dai ba kamar baya ba, haka suke tasa Usman gaba su dinga masa k'iriniya shi kuma yana biye musu, rayuwar ta musu dad'i yanzu kuma sun fahimci zama lafiya yafi zama d'an sarki, a haka rayuwa da lokaci ke tafiya girma na k'ara zuwa musu, Haseenah k'iba take tayi abinta saboda kwanciyar hankali da hutu, amma Khadija har yanzu tana nan yanda take bata rage ba bata k'ara ba, a haka sherau su ka je sosai har shekara *goma sha biyar*.
A wannan shekarun abubuwa da dama sun faru masu dad'i da marasa dad'i, daga ciki akwai rasuwar su malam da Hajia, haka ma mamar Khadija ta rasu sakamakon rashin lafiya, haka mahaifin Haseenah ma ya rasu sai maman su wacce tsufa yasa ko yayanta bata ganewa, da haka kusan dukansu suka zama marayu suna kuma kula da junansu sosai, abun farin ciki kuma akwai haihuwa har biyar da Haseenah ta k'ara bayan Aisha, kuma dukansu mata ne sai auta shi kad'ai ne namiji wanda ya ci sunan *Ali* amma suna kiranshi *Khalifa*, kuma wacce yake biwa ita aka wa Khadija kara aka sawa sunan mahaifiyarta *Sadiya* ita ma suna kiranta da *Nawwal*, hakama hajia an mata takwara *Hawa'u* wacce akewa alkunya da *Noor*, sannan daga ciki akwai kammala karatu da bilal ya yi a k'asar *Canada*, amma har yanzu Khadija bata sake haihuwa ba daga Humaira, amma kaf yaran Haseenah ita ke kula da su kamar ita ta haifesu, a haka Bilal ya dawo ya zama cikakken saurayi son kowa k'in wanda rasa, matashin saurayi kyakyawa kuma miskilin yaro mai d'auke da shekaru *ashirin da bakwai*, hakan yasa Usman damka duk ragamar gidan hannu Bilal, a cewar shi aure zai mi shi nan da d'an lokaci kad'an, wannan damar da Bilal ya samu tasa yake juya komai na gidan har iyayen mata, shi ya sa yanzu kullum gidan cikin hayaniya suke saboda Bilal dai baisan yawan surutu, yau ma kamar kusan kullum Aisha da Humaira ne suka shirya dan auwa bikin k'awar su, masha Allah yan matan Khadija kenan, tabbas shak'uwa dake tsakaninsu tasa har suke kama sosai ta fuska da yanayi, sai dai Humaira tafi haske sosai da dogon hanci sannan tafi cikar hallita da kumari, kayan jikinsu ma iri d'aya ne haka suka nufi d'akin Bilal dake sama dan karb'o makullin mota su bawa drebansu ya kaisu, da sallama suka tura k'ofar Humaira ce gaba.
Kwance yake ruf da ciki babu riga a jikinshi sai dogon wando dake d'aure da d'amara (belt), saida suka tsaya kanshi Humaira tace "Yah Bilal makullin mota za ka bamu mun shirya."
Shiru kamar baiji ba, Aisha ce ta kama hannun Humaira tace "Kinga mu fita wallahi bana so ya tashi ya mana tsinannan duka."
Fizge hannunta tayi tace "Ke wallahi kin cika tsoro, kawai saiya doke mu daga wannan maganar."
Kallonshi tayi ta sake cewa "Ya Bilal magana muke fa."
A hankali ya juyo tare da tashi zaune yana kallonsu, saida ya gama kallonsu yace "Ku rufe k'ofar d'akin sai ku zo ku karb'i makullin."
Kallon juna su ka yi saboda sun san me ya ke nufi da abin da ya fad'a, zare ido su ka fara yi kafin ya sake daka musu tsawa yace "Na ce ku rufe k'ofar ko."
Haba wa ai da gufu suka fita suna rige-rige, Allah ne ya saukesu k'asa lafiya basu zama ko ina ba sai falon Usman, kamar an turosu haka suka fad'a d'akin, kowace wajen ta ta uwar ta nufa wacce tasan zata tsaya mata, Humaira wajen Haseenah Aisha wajen Khadija, wata cakuma da Aisha tawa Khadija yasa d'an kwalinta fad'uwa kan kujera hakan ya bayyanar da yar furfurar dake kan ta wacce ba'a ganinta sosai ma, Khadija ce tace "Kai Aisha ho, wannan ba sai ki karyani ba, lafiya me ya faru?"
Haseenah da sai wani k'ara rumgume Humaira take ne tace "Ai da gani ba tambaya kinsan su da wannan yariman mai gida."
Khadija ce tace "Wallahi al'amarin nan ya fara isata fa, gaba d'aya yaron nan ya hana min yarinya sakewa a gida."
"Ai ba laifinshi bane, laifin wanda ya bashi muk'amin ne a gidan." Cewar Usman daya fito daga d'akin shi tare da sauran yaran sunata gurgurar chocolat, hakan ma yayi daidai da shigowar Bilal ya sanyo farar riga wacce ta kamashi, tabbas ko kad'an Bilal baiyi kama da mahaifinshi ba saboda k'irar jikinshi ma ta k'akk'arfan maza ce kusan zaka iya cewa ma kawunshi ne yayi Habeeb, saidai kyawun mahaifiyarshi da yayi kawai da manyan idanunta, belt d'in dake hannunshi ya nad'e ya yo kan Aisha zai tsala mata ta sake shigewa jikin Khadija, Khadija ce tace "Allah ka daketa sai ranka ya b'ace, kaji marar kunya kai, kai baka ji ance ko mutuwa tana kunyar idon mahaifi ba."
Juyawa yayi ya kalli Humaira hakan yasa Haseenah cewa "Karma ka fara matsowa nan kaji na fad'a maka."
Usman ne yace "Yarima meya faru? Laifin me su ka yi?" Cikin b'acin rai yace "Abba nasha fad'awa yaran nan su daina shigar min d'aki idan ban musu izinin shiga ba,yanzu fa haka kawai suka suka fad'a min d'aki ina kwance ba riga a jiki na."
Khadija ce ta katse da cewa "To shine zaka dake su? Ba sai ka sake musu nasiha ba, kaji sai kace wani gudan babban mutum, yaushe ne aka daina saka maka kaya."
Usman ne yace "Koma yau ne aka daina saka mi shi ai dai an daina saka mi shi saboda ya wuce munzalin, dan haka dole ya hukuntasu tunda sun k'i su san daidai da ba daidai ba."
Kallonshi Khadija tayi ta motsa bakinta hakan yasa Usman yace "Naji ki kamani amma bayan na mik'awa yarima na wannan yaran nan na bayanku."
Wata dariya Haseenah ta yi tace "Kana ganin zaka iya k'watar su a hannun mu ne?"
Wani kallo ya mata yace "Kin manta da k'ashi d'aya ne gareni, bugu d'aya zan mu ku kuji ku a makara."
Dariya Khadija tayi tace "To ina zaka zauna kai kuma?"
"A duniya mana." Ya fad'a ya na zama kusa da su, Haseenah ce tace "Kenan ka fara soyayya a waje bamu sani ba."
Shafa kanshi yayi da ya kusan cika da furfura yace "Ai wasu kyawawan yan mata na samu suka mak'ale min wai ni suke so, kuma na yi alk'awarin aurensu, ai yarima ma zai zama waliyi na."
Dariya suka saka a tare sai Khadija da tace "Komawa baya kenan, to idan zaka je d'aurin auren dai ka shafa gawayi a kanka danka rufe wannan farin abun na kan ka."
Sake shafa kan yayi yace "Alamar arzik'i ne ai, kuma naga kema akwaita a kanki."
Cike da k'aguwa Bilal yace "wai yanzu na zo da matsalata amma ku manta kun shiga sabgar gabanku, Allah ya shirya min ku iyayena, banda kamarku a duniyar nan."
Harya juya zai fita ya tsaya ya nuna su Humaira da yatsa yace "Kuma wallahi babu inda za ku je, na gaji da wannan yawan na ku kullum."
Khadija ce tace "To ni ka ban makullin tawa motar zan fita, ai dai kasan aro ne na baka jiya ko."
Kallon Usman yayi yace "Idan sarki ya bayar da izinin fita sai ku fad'a min zan kawo mu ku."
Cike da jin dad'i Usman ya aika mishi da sumbata yace "Allah ya maka albarka yarona, shi ya sa banda matsala da gidan nan ko bana nan nasan akwai original Usman a gidan, da ni ne da yanzu sun min fari da ido na basu makullan."
Fita yayi daga d'akin sai Usman daya kalli su Aisha yace "Ku kuma ki fito daga nan munafukai kawai, dama da kinga suna raba ido kinsan basu da gaskiya, kuma wallahi ku ka sake shigar masa d'aki ba neman izini da kaina zan hukuntaku."