← Book details Kallon Kitse Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 19 OF 86

Sashe 19

Kallon Kitse Part 1 Complete Hausa Novel · about 7 min read

*Wata biyu* da komawa makaranta Khadija ta kwanta rashin lafiyar da ta jijjigata sosai, dan sai da ta kwana hud'u asibiti ba ta cikin hayyacin ta, ta galabaita da mugun zazzab'i da ciwon kai, ga kuma ciwon ciki da ya murd'ata dole ta yi amai, allura kam tasha ta har ba adadi, haka K'arin ruwa har sai da hannayenta su ka kumbura saboda sukar da ya sha, duk da jikin ya yi dama amma sai da ta cika sati d'aya a asibiti kafin aka sallame ta, cikin ikon Allah kuma sai jiki ya yi kyau sosai, tun daga ranar kuma Khadija ba za tace ga ranar da ta sake kwantawa rashin lafiya ba, sai dai kawai abin da ba'a rasa ba irin su ciwon k'ugu, ciwon baya da d'aurewar mara, kullum Usman godiya ya ke wa Allah da Khadija da ta zama silar sauyawar rayuwar shi, bai tab'a tsammanin auren shi da ita abu neda zai kallo ba, duba da babu maganar soyayya tsakaninsu, sannan ita mai kud'i ce kuma matashiyar yarinya mai ji da kyau, amma ta aure shi babu kud'i babu kyau, kuma duk da haka ta zauna da shi da kyautatawa, wannan ya sa lokuta da dama ya kan fi kiran ta da Nana Khadija baiwar Allah, lokacin kuma arzik'i ya hab'ako sosai, sai kawai ya fara da iyayen shi ta hanyar canza mu su fasalin gida, in da ya gwangwaje su da bila (villa) mai kyau yar zamani, ya d'aukarwa mahaifiyar shi wacce za ta dinga girka mu su abinci sai dai su ci kawai, lokacin da cikin Khadija ya girma ne ya samu wani babban aiki, wata kwangila da aka mallaka mi shi milyoyin kud'i, a lokacin ne ya fara mu su sabon gini su ma, ginin da a lokacin ya amsa sunan gini, ta wani fannin kuma dije na zuwa makarantar ta hankali kwance.

Lokavin dacikin ta ya isa haihuwa ne wata tafiya ta taso mi shi zuwa Dubaï, shine karo na farko da zai fara zuwa, hakan ya sa a ranar Khadija ta wuni ta na kukan ba zai tafi ba, rarrashin duniya ya yi amma ta toshe kunne ta k'i fahimtar shi, a k'arshe dai dole ya yanke shawarar kaita gida ta zauna tare da su mama har ya dawo, ita kuma bud'ar bakin ta cewa ta yi "Aiko sai dai ka tarar na haihu wallahi, dan ba zan jira ka ni."

Dariya ya yi yace "Ba za ki haihu ba insha Allah har sai na dawo."

Haka ya kaita gida ya aje shi kuma ya wuce, tun a mota Murtala ya lura yanayin abokin shi ya canza sosai, cike da kulawa yace "Aboki na lafiya dai? Ya na ga ka yi wani iri ne?"

A hankali ya kalleshi ido sunyi jawur kamar zaiyi kuka yace "Khadija, ita na ke tausayi, sai ta haihu kafin na dawo, ba na jin za ta wuce sati ba ta haihu ba, dan duk alamu sun nuna haka, kwana hud'u ko bacci ba ta iya yi saboda ciwon baya da mara, mtss." Ya k'arashe da d'an guntun tsaki.

Murtala ne yace "To ya za ayi sai hak'uri? Kuma gashi ba ka fad'a mata gaskiyar magana ba cewa tafiyar nan za ta iya d'aukar ka wata d'aya ko fiye da haka."

Ajiyar zuciya ya sauke yace "Sati d'aya ma na fad'a mata amma ta damu sosai, ina ga na fad'a mata wata d'aya zanyi? Shi ya sa ma na riga na barwa Hajia komai su kula idan ta haihu, kuma na gode Allah da na iya fad'awa yan uwan ta adadin lokacin da zan iya yi."

"Hakan ma da ka yi ya yi daidai, kaga za su dinga kwantar mata da hankali."

A haka su ka isa kuma su ka rabu suma cike da kewar juna, a daren wannan ranar Khadija nak'uda ta taso mata, da su ka tafi asibi har sai da gari ya waye rana ta yi fatsal-fatsal kafin ta haihu, duk abin da ake Usman na da labari, lokacin da Husseina ta bawa Khadija waya ya mata magana da ta kasa, wata k'ara tare da kuka had'i da salati da ta yi sai da ya ji kamar ya bud'a ido ya ganshi gabanta, a k'arshe dai *bayan wuya* sai dad'i, ta haihu lafiya haka ma yaro, lokacin wani mugun bacci ne ke d'ibar Khadija amma sai Usman yace Hajia ta bata waya su yi magana, daga kwance ta karb'i wayar ta d'ora a kunne, shiru ta yi sai shine yace "Barka baiwar Allah, daga k'arshe dai Gashi kin haifo min yaro, Khadija ina cikin farin ciki sosai, godiya ko dukiya ba za su iya biyan ki ba, amma ina so ki fad'a min duk abin da ki ke so? Ni kuma zan baki shi a matsayin tukuicin wannan kyautar."

Cikin muryar jin bacci tace "Ina hushi da kai kafin minti ashirin da su ka gabata, saboda ka k'i zama tare da ni a lokacin da na ke buk'atar ta, da ka k'ara kwana d'aya tak da na haihu a gaban idon ka, amma bayan minti ashirin da ya wuce, lokacin da na d'ora ido na akan yaron ka, sai na ji komai ya yaye a zuciya ta, dan haka ka d'auka yaron nan shine tukuicinka gare ni."

Wata nauyayyar ajiyar zuciya ya sauke yace "Ki yi hak'uri Khadija, haka Allah ya so, kuma duk da kin ce ba jya buk'atar komai, amma akwai wani abu da zan ba ki, kinsan me ye?"

Cikin lumshe ido tace "A'a."

"Khadija, nine ya cancanci na yi wa yaron nan hud'uba, kuma gashi bana nan, dan haka babu wanda yafi cancanta sai ke, na d'ora mi ki wannan nauyin a kan ki, idan kin ma sa hud'uba sai ki rad'a masa sunan da ki ka ga ya dace kuma ki ke so."

"Da gaske ka yarda na saka mi shi suna da kai na?" Ta tambaya da fara'a.

"Sosai ma, wannan hukuncin na jima da yanke shi ai, ba kawai dan bana nan bane."

Shiru ta yi kamar mai bacci kafin tace " *Abban Bilal*., hakan ya yi?"

Da farin cikin jin sunan da ta sakawa yaron ya sa yace "Masha Allah, Bilal, sunan da ke birge ni, sunan da ya nake da burin sakawa yaro na shi, hakan fa ya na nuna k'arfin soyayyar da ke tsakanin mu ne."

Jin bcci na son surarta ya sa tace "Ka gafarce ni Abban Bilal, bacci na ke ji sosai a ido na, za mu yi magana anjima."

"Ayyah sannu momyn Bilal, zan barki haka to, amma anjima za mu yi magana, kin yarda?"

Cikin hamma tace "Na yi alk'awari."

Da haka su ka yi sallama, kamar yanda ya bar komai hannun Hajia haka ta dage sosai ta yi takamata, dan mawasu lokutan maman Khadija da yan biyar ba sa tsayawa komai da an nemi abu za su siyo su kawo, haka dai aka yi shagalin biki babu uban yaro, a lokacin Khadija ta fara damuwa da rashin dawowar Usman, da k'yar yan uwanta da mama suke kwantar mata da hankali, tun suna waya ya na cewa zai zo aiki ne ya rik'e shi har ya kai ya rasa me zai ce mata, sai kawai zuciyar shi ta bashi ya daina kiranta, ita kuma idan ta kira jar ya d'aga sai an kwana biyu, wannan dubarar ce ta jefa Khadija a wani hali na daban, da ta kwashe kwanaki ta na kira bai d'aga ba, damuwar ta ta nunku sosai, mama kuma sai take cewa tayi hak'uri mana da yanda Allah ya hukunta mata, hakan ya sa Khadija tunanin ko Usman ya mutu ne dai, kawai sai ta yanki jiki ta fad'i, sai da ta kwana asibiti, a ranr Usman bai shirya tahowa ba amma dole ya taho, dan cewa ya yi neman kud'i ba zai ja mi shi rasa matar shi ba wacce ya ke da yak'inin ba zai samu kamar ta ba a wannn k'arnin, sai lokacin kad'ai Khadija ta samu sauk'i ta kuma huce.

*Allah ka k'ara mana lafiya mai anfani.*
20/01/2020 à 12:38 - 💋😘💋: 💑💑💑💑💑💑💑💑💑💑
*KALLON KITSE*
_(Ake wa rogo)_
💑💑💑💑💑💑💑💑💑💑

_SAMIRA HAROUNA_

*Littatafan marubuciyar*

*1* _KAUSSAR_
*2* _D'AUKAR FANSA_
*3* _BA SO BANE_
*4* _AUREN HAD'I_
*5* _SANIN MASOYI_
*6* _JIHADI_
*7* _K'ANGIN RAYUWA_
*8* _ITACE K'ADDARARMU_
*9* _KAWU NA NE_
*10* _MAATA_
*11* _KALLON KITSE..._

*SADAUKARWA GA*

_MATAN FARKO_🧕🏼 *(UWAYEN GIDA)*

🇸🇦 *ZAMAN AMANA WRITER'S*
_(Gidan zaman lafiya da amana insha Allah)_🤜🤛

💕💕💕 *My Heenat, My BK, My Meelat*💞💞💞

_Alkhairin Allah ya lullub'e min ku, ina k'aunar ku._😘

```Fatan alkairi masoya```

*MOMYN DADY, KI JI DAD'IN KI WANNAN PAGE TA KI CE KYAUTA.* 😉

_Bismillahir rahamanir rahim_

*13*
Chapter 19 · 0% Book details