Sashe 11
Kallon Kitse Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
D'an b'ata rai ya yi yace "Kai Bilal, mahaukaci ne ni da zan barka ka tafi a hanyar ababen hawan nan kai kad'ai akan moton ka, bana so, kuma na fad'a maka hawan moton ka kar ya wuce cikin unguwar nan, duk da cazashi ne ake amma ba na so, kar kuma ka kuskura na gan ka ko a bakin titi ne, dan ran ka zai b'ace."
Mik'ewa Bilal ya yi ya matsa kusan shi yace "Ka yi hak'uri Abba, ba zan sake ba."
Kan shi kawai ya shafa bai ce komai ba, jakar shi ya d'auka mai d'auke da littafanshi yace "Na gama."
Kallon shi ya yi yace "Ka tabbata ka k'oshi?"
Kai kawai ya d'agaalamar Eh, hannun shi ya kama yace "To muje."
Juyowa ya yi ya d'agawa mahaifiyar shi hannu yace "Sai na dawo sarauniya."
Murmushi ta masa tace "Allah ya tsare, a kula sosai ka ji ko?"
Usman ma kallon ta ya yi yace "Ni ma na tafi ba zan dawo ba."
Ba alamar wasa a tare da ita tace "Sai na bika duk in da ka ke ai."
Dariya ya yi yace "Kar ki damu sarauniya zan dawo ai, ke ce fa."
"Ah to, sai na ma riske ka duk in da kaje." Ta fad'a ta na tashi dan had'a kayan da su ka karya.
*Kafin mu ci gaba, za mu waiwaiya baya mu ji yanda wannan soyayyar ta fara ta Khadija da Usman.*
_Sai mun had'u a shafi na gaba._✋
10/01/2020 à 12:20 - 💋😘💋: 💑💑💑💑💑💑💑💑💑💑
*KALLON KITSE*
_(Ake wa rogo)_
💑💑💑💑💑💑💑💑💑💑
_SAMIRA HAROUNA_
*Littatafan marubuciyar*
*1* _KAUSSAR_
*2* _D'AUKAR FANSA_
*3* _BA SO BANE_
*4* _AUREN HAD'I_
*5* _SANIN MASOYI_
*6* _JIHADI_
*7* _K'ANGIN RAYUWA_
*8* _ITACE K'ADDARARMU_
*9* _KAWU NA NE_
*10* _MAATA_
*11* _KALLON KITSE..._
*SADAUKARWA GA*
_MATAN FARKO_🧕🏼 *(UWAYEN GIDA)*
🇸🇦 *ZAMAN AMANA WRITER'S*
_(Gidan zaman lafiya da amana insha Allah)_🤜🤛
```Fatan alkairi masoya```
_Bismillahir rahamanir rahim_
*9*
*Alhaji Ahmad*, dattijo mai dattako, mutum ne da Allah ya wadace shi da komai, dukiya, ilimi da 'ya'ya, matar shi d'aya *Hajia Sadiya*, suna zaune lafiya cikin farin ciki, mutum ne shi da bai da ra'ayin tara mata, hakan ya sa suke zaune daga Sadiya sai yayan ta, Allah ya azurta su da yaya maza guda biyar, *Ashir* shine babba, sai *Bashir* sai kuma *Habib* da *Mansur* da *Naseer*, Naseer na da shekara biyar aka samu cikin da ya wahalar da Sadiya, tun a lokacin su ke ji a jikin su cewa Allah zai musu sauyi ne, cikin ikon Allah kam bayan laulayin da ta sha sai gashi ta haifo kyakyawar yarinya mai kama da ita, *Nana Khadija*, yarinya ce da ta zama tamkar wata zinariya a cikin mutane, kowa soyayya ya ke nuna mata, lele kawai da gata take gani, su kan su yan uwanta suna matuk'ar k'aunar ta, dan har fad'a suke akan wanda ya fi sonta ko wanda zai d'auke ta, haka Khadija ta taso cikin gata da kulawar iyaye da yan uwa, sai dai tun da ta fara tafiya suka lura kamar tana da matsalar ido, basu b'ata lokaci ba wajen ziyartar likitoci, nan aka sanar da su tana da matsalar gani, bata iya gani da kyau sai dishi-dishi, sosai mahaifinta ya damu kuma yake yawon nema mata magani, amma sam ba'a dace ba har k'asar waje an fita da ita, haka dai suka hak'ura aka d'ora ta akan saka gilashi mai k'ara gani, wannan laurar sai tasa iyayenta da yan uwanta sake tausaya mata da k'ara k'aunar ta, sam larurarta bata tab'a damunta ba bare tasa damuwa, tana jin dad'in kasancewarta a yanda take, duba da wasu sam idon ne ma basa da su, tana da shekara *goma sha biyu* a duniya ranar wata alhamis da dare, suna zaune a farfajiyar gida su na ta hira Khadija na kan k'afafun mahaifin ta, da sauri ta juya ta kalli baban ta tace "Baba, ka ga wani ya shiga d'akin ka."
Da mamaki ya juya ya kalli k'ofar d'akin na shi ya gan shi rufe, murmushi ya yi ya kalle ta yace "Auta ni banga kowa ba, gashi ki na gani ma d'akin a rufe ya ke."
Naseer ne yace "Wallahi nima Baba sai na ga kamar giftawar mutum."
Sake juyawa ya yi ya kalli k'ofar yace "To wa zai shigo cikin gidan bayan ga k'ofar nan a gaban mu kuma ace ba mu ga shigowar shi ba."
Almajirinsu da ke zaune nesa da su ne ya na cin abinci ne yace "Baban Khadija wallahi nima na gan shi, wani dogo da fararen kaya, amma banga fuskar shi ba, kuma na so inyi magana saina kasa na ji tsoro."
_Wallahi wannan wani abun al'ajabi ne da ya faru da wata baiwar Allah da na sani, za mu iya cewa mala'ikan mutuwa ne_
Sadiya ce tace "Kai Ashir tashi ka duba mana."
Kallonta ya yi yace "Mama, ni kad'ai? Kawai ki bar shi idan ya ga ji zai fito ai mu gan shi."
Dariya aka saka sai Baba ne yace "Ki bar shi kawai, watak'ila fa gizo idon su ke musu, na ga ai ga k'ofar shigowa nan, babu wanda mu ka ga ya shigo."
Haka aka share wannan magana aka ci gaba da hira, Khadija ce bacci ya dauke ta a k'afafun shi, a hankali ya d'auke ta ya kai ta makwancin ta ya shafeta da addu'a, fitowa ya yi su Ashir ma har sun tashi, dawo da su ya yi suka zauna, ya jima ya na musu nasiha da su rik'e Khadija da kyau su zama gatanta ita kad'ai ce k'anwar su mace, har sha biyu na dare ta wuce kad'ai suka tashi, d'akin shi ya shiga ya yi shirin kwanciyar shi sannan ya d'auro alwala, raka'a biyu ya samu damar yi wani nauyayyen bacci ya sure shi akan sallayar, daga wannan bacci ne Allah ya karb'i abin shi.
Mutuwar nan ta girgiza mutane sosai, musamman Sadiya da ke kwance asibiti ba ta san me ake yi ba, Khadija ma yan uwan ta kad'ai take iya yarda da su, amma haka ko da lokaci ya tafi kowa ya manta, sai dai ciwon na nan a zuk'ata, dukansu mazan babu wanda bai da aikinyi mai kyau, hakan ya sa suke matuk'ar kula da k'anwar su, sosai suke shagwab'a ta, ga yarinya na girma amma gatan da take samu yasa kullum kamar yarinya.
Tun Khadija na da shekara sha biyar Ashir ya gwangwaje ta da moto, duk da sauran yan uwan kowa ya so ace shi ya siya mata, amma haka suka hak'ura tun da ya fisu zafin nama, wannan lokacin ne aka musu rabon gado, kowa ya tashi da na shi kason mai tsoka, na Khadija kuma tace a bawa Ashir da Mansur su ci gaba da juyawa dan sune suka fi sha'awar kasuwanci, mamansu ma dama ta na nata kasuwanci, dan haka ta ci gaba daga inda ta tsaya.
*Duk* wata ba'a daina abin da Alhaji Ahmad ya fara ba, ana yanka rago ayi sadaka, sannan akanyi waina ayi miya sai su aika inda mahaifinsu ke zama da yamma wajen abokanan shi, haka rayuwar ke tafiya har lokacin da Khadija ta ci jarabawarta kuma sakamako mai kyau, babbar walima yayyun ta suka shirya mata a bazata, kayan da suka shirya mata suka sata ta saka suka tafi da ita babban wajen cin abinci, k'awayenta da maza da dama ta samu wanda su ka yi karatu tare, ta ji dad'i sosai a ranar, anan ta yanka (😂bansan me zan kira cake da hausa ba, amma bara nace mu ku panke) saida ta bi duka yan uwanta biyar ta saka mu su a baki kafin k'awar ta *Kaltume* da *Salamatu*, haka aka gama shagali aka yi murna sosai aka watse.
*Komai na da mafari a rayuwa*, matar Ashir da Bashir da mama sun gama waina, sai dai babu mai kaiwa, Habib kad'ai ke gari kuma shi ma ya na wajen d'aurin auren abokin shi a wani k'auye *Dak'oro*, hakan ne ya tilasta mama cewa Khadija ta shirya sai ta kai a kan moton ta, shiryawa ta yi tare da Kaltume da su ke kusa da juna suka tafi, Kaltume ita ke rik'e da kwanukan abincin a baya, sun isa lafiya su ka kai abincin, cikin ladabi su ka gaishe da dattawan, da kansu su ka wanke babban faranti suka zuba mu su wainar sannan suka d'aure kwanukan su ka mu su sallama, kasancewar akwai rairai kafin su hau titi ya sa Kaltume ba ta hau ba ta na jiran Khadija ta fita daga rairain, cikin rashin sa'a wani tsoho ya taho zai shiga shagon d'inkin shi, tana murd'awa sai kuwa ta bige tsoho ya fad'i, dukan su suka fad'i k'asa da azama aka kawo mu su d'auki, duk da masuburbud'ar zafi (shagama inji salim, salansa inji mak'obtanmu) ta tab'a ba bai dame ta ba, tsohon mutane data bige shine a gabanta, kuka take ta na tambayar tsohon bai ji ciwo ba, duk da k'afar shi da ta buga yaji ta na masa ciwo haka ma gwiwar hannun shi daya fad'a samanta, amma sai ya nuna ba komai kawai ta tafi, cikin abokan mahaifin nata ne ya lura da hannun shi har jini ya d'an fara fitowa ta cikin riga, nan aka ce a kai shi likita Khadija tace ita ma za ta je, da k'yar suka lallab'a ta dan ta tafi gida, amma duk ta d'aga hankalinta sosai sai hawaye take, wani daga cikin dattawan ne yace "Kinga Khadija ki daina kuka, zai samu sauk'i, kinga ciwon ai kad'an ne, Allah ne ya aiko dole hakan ta faru, yanzu kije gida ki huta, zuwa gobe sai kije godanshi ki dubo shi ko, hakan ya yi?"
D'aga kai ta yi alamar eh, sai da ta hau moton Kaltume ma ta hau sannan tace "Ina ne gidan?"
"Gidan ya na nan yan banana wajen masallacin ladan."
Mik'ewa Bilal ya yi ya matsa kusan shi yace "Ka yi hak'uri Abba, ba zan sake ba."
Kan shi kawai ya shafa bai ce komai ba, jakar shi ya d'auka mai d'auke da littafanshi yace "Na gama."
Kallon shi ya yi yace "Ka tabbata ka k'oshi?"
Kai kawai ya d'agaalamar Eh, hannun shi ya kama yace "To muje."
Juyowa ya yi ya d'agawa mahaifiyar shi hannu yace "Sai na dawo sarauniya."
Murmushi ta masa tace "Allah ya tsare, a kula sosai ka ji ko?"
Usman ma kallon ta ya yi yace "Ni ma na tafi ba zan dawo ba."
Ba alamar wasa a tare da ita tace "Sai na bika duk in da ka ke ai."
Dariya ya yi yace "Kar ki damu sarauniya zan dawo ai, ke ce fa."
"Ah to, sai na ma riske ka duk in da kaje." Ta fad'a ta na tashi dan had'a kayan da su ka karya.
*Kafin mu ci gaba, za mu waiwaiya baya mu ji yanda wannan soyayyar ta fara ta Khadija da Usman.*
_Sai mun had'u a shafi na gaba._✋
10/01/2020 à 12:20 - 💋😘💋: 💑💑💑💑💑💑💑💑💑💑
*KALLON KITSE*
_(Ake wa rogo)_
💑💑💑💑💑💑💑💑💑💑
_SAMIRA HAROUNA_
*Littatafan marubuciyar*
*1* _KAUSSAR_
*2* _D'AUKAR FANSA_
*3* _BA SO BANE_
*4* _AUREN HAD'I_
*5* _SANIN MASOYI_
*6* _JIHADI_
*7* _K'ANGIN RAYUWA_
*8* _ITACE K'ADDARARMU_
*9* _KAWU NA NE_
*10* _MAATA_
*11* _KALLON KITSE..._
*SADAUKARWA GA*
_MATAN FARKO_🧕🏼 *(UWAYEN GIDA)*
🇸🇦 *ZAMAN AMANA WRITER'S*
_(Gidan zaman lafiya da amana insha Allah)_🤜🤛
```Fatan alkairi masoya```
_Bismillahir rahamanir rahim_
*9*
*Alhaji Ahmad*, dattijo mai dattako, mutum ne da Allah ya wadace shi da komai, dukiya, ilimi da 'ya'ya, matar shi d'aya *Hajia Sadiya*, suna zaune lafiya cikin farin ciki, mutum ne shi da bai da ra'ayin tara mata, hakan ya sa suke zaune daga Sadiya sai yayan ta, Allah ya azurta su da yaya maza guda biyar, *Ashir* shine babba, sai *Bashir* sai kuma *Habib* da *Mansur* da *Naseer*, Naseer na da shekara biyar aka samu cikin da ya wahalar da Sadiya, tun a lokacin su ke ji a jikin su cewa Allah zai musu sauyi ne, cikin ikon Allah kam bayan laulayin da ta sha sai gashi ta haifo kyakyawar yarinya mai kama da ita, *Nana Khadija*, yarinya ce da ta zama tamkar wata zinariya a cikin mutane, kowa soyayya ya ke nuna mata, lele kawai da gata take gani, su kan su yan uwanta suna matuk'ar k'aunar ta, dan har fad'a suke akan wanda ya fi sonta ko wanda zai d'auke ta, haka Khadija ta taso cikin gata da kulawar iyaye da yan uwa, sai dai tun da ta fara tafiya suka lura kamar tana da matsalar ido, basu b'ata lokaci ba wajen ziyartar likitoci, nan aka sanar da su tana da matsalar gani, bata iya gani da kyau sai dishi-dishi, sosai mahaifinta ya damu kuma yake yawon nema mata magani, amma sam ba'a dace ba har k'asar waje an fita da ita, haka dai suka hak'ura aka d'ora ta akan saka gilashi mai k'ara gani, wannan laurar sai tasa iyayenta da yan uwanta sake tausaya mata da k'ara k'aunar ta, sam larurarta bata tab'a damunta ba bare tasa damuwa, tana jin dad'in kasancewarta a yanda take, duba da wasu sam idon ne ma basa da su, tana da shekara *goma sha biyu* a duniya ranar wata alhamis da dare, suna zaune a farfajiyar gida su na ta hira Khadija na kan k'afafun mahaifin ta, da sauri ta juya ta kalli baban ta tace "Baba, ka ga wani ya shiga d'akin ka."
Da mamaki ya juya ya kalli k'ofar d'akin na shi ya gan shi rufe, murmushi ya yi ya kalle ta yace "Auta ni banga kowa ba, gashi ki na gani ma d'akin a rufe ya ke."
Naseer ne yace "Wallahi nima Baba sai na ga kamar giftawar mutum."
Sake juyawa ya yi ya kalli k'ofar yace "To wa zai shigo cikin gidan bayan ga k'ofar nan a gaban mu kuma ace ba mu ga shigowar shi ba."
Almajirinsu da ke zaune nesa da su ne ya na cin abinci ne yace "Baban Khadija wallahi nima na gan shi, wani dogo da fararen kaya, amma banga fuskar shi ba, kuma na so inyi magana saina kasa na ji tsoro."
_Wallahi wannan wani abun al'ajabi ne da ya faru da wata baiwar Allah da na sani, za mu iya cewa mala'ikan mutuwa ne_
Sadiya ce tace "Kai Ashir tashi ka duba mana."
Kallonta ya yi yace "Mama, ni kad'ai? Kawai ki bar shi idan ya ga ji zai fito ai mu gan shi."
Dariya aka saka sai Baba ne yace "Ki bar shi kawai, watak'ila fa gizo idon su ke musu, na ga ai ga k'ofar shigowa nan, babu wanda mu ka ga ya shigo."
Haka aka share wannan magana aka ci gaba da hira, Khadija ce bacci ya dauke ta a k'afafun shi, a hankali ya d'auke ta ya kai ta makwancin ta ya shafeta da addu'a, fitowa ya yi su Ashir ma har sun tashi, dawo da su ya yi suka zauna, ya jima ya na musu nasiha da su rik'e Khadija da kyau su zama gatanta ita kad'ai ce k'anwar su mace, har sha biyu na dare ta wuce kad'ai suka tashi, d'akin shi ya shiga ya yi shirin kwanciyar shi sannan ya d'auro alwala, raka'a biyu ya samu damar yi wani nauyayyen bacci ya sure shi akan sallayar, daga wannan bacci ne Allah ya karb'i abin shi.
Mutuwar nan ta girgiza mutane sosai, musamman Sadiya da ke kwance asibiti ba ta san me ake yi ba, Khadija ma yan uwan ta kad'ai take iya yarda da su, amma haka ko da lokaci ya tafi kowa ya manta, sai dai ciwon na nan a zuk'ata, dukansu mazan babu wanda bai da aikinyi mai kyau, hakan ya sa suke matuk'ar kula da k'anwar su, sosai suke shagwab'a ta, ga yarinya na girma amma gatan da take samu yasa kullum kamar yarinya.
Tun Khadija na da shekara sha biyar Ashir ya gwangwaje ta da moto, duk da sauran yan uwan kowa ya so ace shi ya siya mata, amma haka suka hak'ura tun da ya fisu zafin nama, wannan lokacin ne aka musu rabon gado, kowa ya tashi da na shi kason mai tsoka, na Khadija kuma tace a bawa Ashir da Mansur su ci gaba da juyawa dan sune suka fi sha'awar kasuwanci, mamansu ma dama ta na nata kasuwanci, dan haka ta ci gaba daga inda ta tsaya.
*Duk* wata ba'a daina abin da Alhaji Ahmad ya fara ba, ana yanka rago ayi sadaka, sannan akanyi waina ayi miya sai su aika inda mahaifinsu ke zama da yamma wajen abokanan shi, haka rayuwar ke tafiya har lokacin da Khadija ta ci jarabawarta kuma sakamako mai kyau, babbar walima yayyun ta suka shirya mata a bazata, kayan da suka shirya mata suka sata ta saka suka tafi da ita babban wajen cin abinci, k'awayenta da maza da dama ta samu wanda su ka yi karatu tare, ta ji dad'i sosai a ranar, anan ta yanka (😂bansan me zan kira cake da hausa ba, amma bara nace mu ku panke) saida ta bi duka yan uwanta biyar ta saka mu su a baki kafin k'awar ta *Kaltume* da *Salamatu*, haka aka gama shagali aka yi murna sosai aka watse.
*Komai na da mafari a rayuwa*, matar Ashir da Bashir da mama sun gama waina, sai dai babu mai kaiwa, Habib kad'ai ke gari kuma shi ma ya na wajen d'aurin auren abokin shi a wani k'auye *Dak'oro*, hakan ne ya tilasta mama cewa Khadija ta shirya sai ta kai a kan moton ta, shiryawa ta yi tare da Kaltume da su ke kusa da juna suka tafi, Kaltume ita ke rik'e da kwanukan abincin a baya, sun isa lafiya su ka kai abincin, cikin ladabi su ka gaishe da dattawan, da kansu su ka wanke babban faranti suka zuba mu su wainar sannan suka d'aure kwanukan su ka mu su sallama, kasancewar akwai rairai kafin su hau titi ya sa Kaltume ba ta hau ba ta na jiran Khadija ta fita daga rairain, cikin rashin sa'a wani tsoho ya taho zai shiga shagon d'inkin shi, tana murd'awa sai kuwa ta bige tsoho ya fad'i, dukan su suka fad'i k'asa da azama aka kawo mu su d'auki, duk da masuburbud'ar zafi (shagama inji salim, salansa inji mak'obtanmu) ta tab'a ba bai dame ta ba, tsohon mutane data bige shine a gabanta, kuka take ta na tambayar tsohon bai ji ciwo ba, duk da k'afar shi da ta buga yaji ta na masa ciwo haka ma gwiwar hannun shi daya fad'a samanta, amma sai ya nuna ba komai kawai ta tafi, cikin abokan mahaifin nata ne ya lura da hannun shi har jini ya d'an fara fitowa ta cikin riga, nan aka ce a kai shi likita Khadija tace ita ma za ta je, da k'yar suka lallab'a ta dan ta tafi gida, amma duk ta d'aga hankalinta sosai sai hawaye take, wani daga cikin dattawan ne yace "Kinga Khadija ki daina kuka, zai samu sauk'i, kinga ciwon ai kad'an ne, Allah ne ya aiko dole hakan ta faru, yanzu kije gida ki huta, zuwa gobe sai kije godanshi ki dubo shi ko, hakan ya yi?"
D'aga kai ta yi alamar eh, sai da ta hau moton Kaltume ma ta hau sannan tace "Ina ne gidan?"
"Gidan ya na nan yan banana wajen masallacin ladan."