Sashe 4
Kallon Kitse Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Saida ta kalli maman su wacce ta ke da yak'inin za ta tsawatar mu su kafin tace "Kawai dai a gurin bikin mu ka had'u, kuma masha Allah wallahi ba ki ganta ba, kyakyawa da ita, musamman gilashin idon ta ya k'ara mata masifar kyau, gaskiya ta birgeni sosai saboda da ganin ta akwai fara'a da kuma kama jiki."
Wani bak'in ciki ne ya tokare Haseenah a wuya, amma sai ta dake tace "Ni dai yanzu ki ban abin da ki ka rage wajen siyayyar."
Hannu tasa a jaka da nufin fito da kud'in, hakan kuma ya yi daidai da tashin maman su ta shiga cikin d'aki, dan haka Mariya ta gyara zama murya k'asa k'asa tace "Haseenah kinsan wacece kishiyar ki kuwa?"
Cikin yamutse fuska tace "Ni kuma ina zan sani."
Gyara zama ta sake yi tace "Hum! Haseenah, wallahi sai kin tashi tsaye tsayin daka, dan kishiyar ki ba ta wasa ba ce, wai kinsan su wanene k'awayen ta?"
Cike da jin haushi tace "To wai ni dan Allah ina zan sani, haba, ki yi magana yin za ki yi kawai."
Sai da ta bubbuga k'afar ta tace "Khadija kishiyar ki, su *Hajia Turai Dubai* da *Hajia Salamatou k'urori* da *Barira nagoma* da *Hajia Natali*, sune manyan k'awayen ta, shin kinsan ma wacece aminiyar ta?"
"Sai kin fad'a." Cewar Haseenah.
Sai da ta sauke numfashi tace " *Hajia Kaltume*, Kaltume mai kayan dad'i."
D'orawa ta yi da " Haseenah, wallahi sai kin tashi tsaye, kinga matan nan da na lissafa mi ki, gogagggun wayayyu ne, manyan mata ne ma su ji da kan su, duk kishiyoyin matan nan in fad'a mi ki ba su da daraja a wajen majazensu, kinga Kaltume mai maganin mata, to in fad'a mi ki in ba ki cika cikakkiyar mace ba ma ba ki siyan maganin ta, dan k'aramin magani a wajen Kaltume shine na *jikka hamsin* (jaka hamsin), duk wata mace da ta k'oshi kuma ta ke mulki a gidan mijin ta to Kaltume ce sirrin farin cikin ta, dan wani shegen gyaran jikin idan ta mi ki shi, to wallahi tun a daren farkon ki kin gama da mijin ki kenan, duk wata mace da za ta raba ki da shi, to sai dai fa in ta sihiri ne, amma d'and'anon ku ba ya tab'a zama d'aya a wajen shi."
Gaba d'aya jikin Haseenah ne ya yi sanyi da jin wannan al'amari, ganin haka ya sa Mariya cewa "Akwai mafita d'aya da ta rage mi ki."
"Wace iri?" Cewar Haseenah da saurin ta, d'orawa ta yi da "Nasan kishiyar ki a tsume take da had'in Kaltume, kuma tunda ita ce aminiyar ta kinga kenan ba za ki tab'a cin mata ba , amma abu d'aya shine, kema ki samo kud'ad'e a hannun Usee, sai kawai muje mu ga Kaltumen, sannan akwai wata ma da ke kawo min kayan mata, ita ma sai ta had'a mana da nata, koya ki ka gani?"
"Hakan ma ya yi, kuma kinga dama shi mutum ne mai kyauta, ba sai ka tambaye shi ba ya ke yi."
"Dan haka sai ki samo mana kud'i a hannun shi, amma fa duk da haka sai mun d'an k'ara da malamai, ko ba komai su tayaki da addu'a dan ki samu bakali a wajen shi."
Tashi ta yi tsaye tace "Shikenan aunty Mariya, yanzu wannan kud'in ma ki rik'e a fara wani abun da su, yau ko gobe zan sa ya zo sai na samu kud'in, amma kar ki bari mama ta ji, kinsan halin ta yanzu sai tace ba ta yarda ba."
"Ni? Ina zan fad'a mata, ba ki ga sai da ta tashi ba ma na fad'a mi ki."
"To ni zan tafi su Zeinab na jira na."
"Sai kun dawo." Ta fad'a ta na bin ta da kallo.
*Allah ya fidda _Delu_😂 daga rogo.*
⏩⏩⏩⏩⏩⏩
Khadija kam a wajen bikin suna can har yamma, sai da su ka gama zubin da suke na k'awaye kafin su ka fito tare da Kaltume, motar ta su ka shiga ta bata wasu harkokin, kamar yanda ta san Khadija farin sani, ba ta anfani da kowane irin garin magani, musamman wanda za ace ayi matsi da shi, ta na sallamar ta ta fita daga motar ta rufe tace "Sai kin zo k'awata."
Kaltume ce tace "A'a k'awata, gaskiya ba na so na zo gidan ki yanzu, na fi so sai an fara shagulgulan bikin nan, lokacin na k'ara had'o mi ki wasu kayan."
Dariya Khadija ta yi tace "Ke fa muguwa ce, wato kullum burin ki kiga bawan Allah nan ya na gasa min aya a hannu ko? To daga wannan da na karb'a sai amarya ta zo ta haihu, idan za ta yi arba'in sai mu shirya tare."
Cikin d'aga murya Kaltume tace "Ina, ana babbak'ar gwiwa wa ke jiyo k'aurin zomo, ai dole yarinya ta gane da banbanci wallahi, wanda ya sa ta shigo gidan Khadija ta Usee, shi zai sa ta gane Khadija ta mata nisa na har abada."
Cikin dariya Khadija tace "Dan Allah k'awata ki ragawa yarinyar nan, har yanzu fa ba mu san ta ba bare mu san da me za ta shigo gidan ita ma."
Cike da gadara da tabbatarwa tace "Ai ko ni Kaltume za ta d'aura a k'ugun ta taje dani gidan, wallahi na riga da na bawa Khadija sirrin da za ta mata rata mai tsayin gaske."
"Na yarda, yanzu dai sai anjima, sai munyi waya ko?"
"To ba damuwa k'awata, ina k'ara fad'a mi ki dai, dan Allah banda nuna kishi a fili, ayi komai cikin kissa k'awata, ban da matsala da ke ta wannan fannin , amma kishi masifa ne wallahi."
"Hakane k'awata, kuma insha Allah zan kiyaye, nagode sosai."
"To, ki kula da kan ki."
"Kema haka."
Da haka ita ma ta shiga ta ta motar ta bar wajen, Khadija kuma ta na zuwa gida ta samu wannan kayan arzik'i, gidan su ta kira ta fad'a mu su, zuwa bayan sallah magrib kam sai ga maman ta da matan yayyun ta sun zo ganin kayan, hotunan su ta d'auka ta turawa k'awayen ta dan su gani suma ba sai sun zo ba, anan ne ma har su ka yi magana da maman ta a kan kayan d'aki da za ta canza, mahaifiyar da kan ta ta d'auki alhakin yi mata odar su daga k'asar waje, dan itama ta na so ta kece raini.
Sun fito dan tafiya Usmane ya shigo gidan, da gudu Bilal ya k'arasa ya rumgume shi, har k'asa ya duk'a ya gaishe da mama, mama ce tace "Kai yanzu da girman ka har ka ke wani mak'ale shi kamar yaro."
Hararan wasa Bilal ya aika mata yace "Kaji tsohuwar nan, ke ma fa idan na je gidan ki har d'auka ta ki ke."
Dafe k'irji ta yi tace "Kaji min sarkin sharri, ni kuma ina zan iya d'aukar ka? Ka fad'i abin da hankali zai d'auka mana."
"To ai dai Abba na ne ko." Ya fad'a ya na k'ara sarkafe wuyan Usman da har yanzu ke durk'ushe, ita ma kuma cewa ta yi "Ni ma kuma d'ana ne ba, kaga kuwa ba zan bari nima ka karya min yaro ba."
A hankali Usman ya kalli Bilal ya d'an janye shi daga jikin shi yace "Mama ta fika gaskiya, kowace uwa d'an ta ta sani, dan haka kowa ya je wajen maman sa, kai ma jeka ga ta ka can."
Kallon shi Bilal ya yi yace "Lallai ma Abba, za ka nemi ne ai har in da na ke, kafi kowa sanin cewa ni ne bugun zuciyar ka."
Wajen Khadija ya nufa ta d'auke shi saboda k'arfin hali duk da girman shi, mama kuma kallon Usman ta yi ta k'ara da "Mun ga kaya fa, a gaskiya sunyi sosai, sai dai kuma kayan kamar sunyi yawa, Allah ya k'ara bud'i na alkairi."
Ba tare da ya d'ago ba yace "Ameen ameen Hajia, ai ni ne da godiya, Allah ya saka da alkairi, Allah ya k'ara girma da lafiya."
"Ameen ameen." Mama ta amsa kafin Khadija ta d'ora da "Tofa, yanzu za ka fara godiyar ko?"
D'ago kai ya yi ya kalle ta yace "Ke kuma ba kya so ina godiyar ko?"
Hannaye ta d'aga tace "Allah ba ka hak'uri, ga ka ga su."
Mama kam wucewa su ka yi suna fad'in "Sai da safen ku."
Bilal da ke bayan Khadija ne ya d'aga musu hannu yace "Sauka lafiya, ko k'ofa ba zan raka ki ba bare ki sa ran samun na adaidaita."
Usman ne ya juyo ya kalle shi yace "Haihuwa maganin takaicin duniya, sai da ta haife ni kafin kai ma ka zo, dan haka da kai na zanyi dakon mahaifiyar ta har makwancin ta."
Dariya kawai su ke har su ka isa k'ofar gidan, cikin shagwab'a Khadija tace "Amma fa kar ku jima, ku yi sauri ku dawo."
Kafad'a ya mak'ale yace "Na k'i d'in."
Hararan shi ta yi tace "Za ka dawo ai ka same ni, zan kama ka a hannu."
Ba tare da ya bari mama ta gani ba ya mata gwalo yace "Ki kama ni d'in, ba zan shigo ba sai kinyi bacci."
"Bayan na rufe gida na ba." Ta fad'a kamar mai son tabbatar masa da za ta iya, haka dai ya d'auke su su ka wuce, mama ta so ya yi zaman shi su k'arasa titi su hau adaidaita, dan dama ko da *Naseer* ya kawo su sun fad'a mi shi za su koma da kansu, amma bai bari ba sai da ya kai su har k'ofar gida ya dire su, nan ma sai da ya fito daga motar ya sake mu su sallama kafin ya yi gaba, ya na kan hanyar shi kuma kiran amarya Haseenah ya shigo wayar shi, kashe kiran ya yi sannan ya sake kira da kan shi, ta na d'auka cikin ladabi tace "Amincin Allah ya tabbata a gare ka adali na."
Cikin jin dad'i yace "Kema haka, ya amarya ta take?"
Cikin siririyar murya tace "Da dad'i ba dad'i, amma daga yanda na ji karsashin muryar ka sai ya sa na ji wata tabbatacciyar lafiya na shiga jiki na."
Wani bak'in ciki ne ya tokare Haseenah a wuya, amma sai ta dake tace "Ni dai yanzu ki ban abin da ki ka rage wajen siyayyar."
Hannu tasa a jaka da nufin fito da kud'in, hakan kuma ya yi daidai da tashin maman su ta shiga cikin d'aki, dan haka Mariya ta gyara zama murya k'asa k'asa tace "Haseenah kinsan wacece kishiyar ki kuwa?"
Cikin yamutse fuska tace "Ni kuma ina zan sani."
Gyara zama ta sake yi tace "Hum! Haseenah, wallahi sai kin tashi tsaye tsayin daka, dan kishiyar ki ba ta wasa ba ce, wai kinsan su wanene k'awayen ta?"
Cike da jin haushi tace "To wai ni dan Allah ina zan sani, haba, ki yi magana yin za ki yi kawai."
Sai da ta bubbuga k'afar ta tace "Khadija kishiyar ki, su *Hajia Turai Dubai* da *Hajia Salamatou k'urori* da *Barira nagoma* da *Hajia Natali*, sune manyan k'awayen ta, shin kinsan ma wacece aminiyar ta?"
"Sai kin fad'a." Cewar Haseenah.
Sai da ta sauke numfashi tace " *Hajia Kaltume*, Kaltume mai kayan dad'i."
D'orawa ta yi da " Haseenah, wallahi sai kin tashi tsaye, kinga matan nan da na lissafa mi ki, gogagggun wayayyu ne, manyan mata ne ma su ji da kan su, duk kishiyoyin matan nan in fad'a mi ki ba su da daraja a wajen majazensu, kinga Kaltume mai maganin mata, to in fad'a mi ki in ba ki cika cikakkiyar mace ba ma ba ki siyan maganin ta, dan k'aramin magani a wajen Kaltume shine na *jikka hamsin* (jaka hamsin), duk wata mace da ta k'oshi kuma ta ke mulki a gidan mijin ta to Kaltume ce sirrin farin cikin ta, dan wani shegen gyaran jikin idan ta mi ki shi, to wallahi tun a daren farkon ki kin gama da mijin ki kenan, duk wata mace da za ta raba ki da shi, to sai dai fa in ta sihiri ne, amma d'and'anon ku ba ya tab'a zama d'aya a wajen shi."
Gaba d'aya jikin Haseenah ne ya yi sanyi da jin wannan al'amari, ganin haka ya sa Mariya cewa "Akwai mafita d'aya da ta rage mi ki."
"Wace iri?" Cewar Haseenah da saurin ta, d'orawa ta yi da "Nasan kishiyar ki a tsume take da had'in Kaltume, kuma tunda ita ce aminiyar ta kinga kenan ba za ki tab'a cin mata ba , amma abu d'aya shine, kema ki samo kud'ad'e a hannun Usee, sai kawai muje mu ga Kaltumen, sannan akwai wata ma da ke kawo min kayan mata, ita ma sai ta had'a mana da nata, koya ki ka gani?"
"Hakan ma ya yi, kuma kinga dama shi mutum ne mai kyauta, ba sai ka tambaye shi ba ya ke yi."
"Dan haka sai ki samo mana kud'i a hannun shi, amma fa duk da haka sai mun d'an k'ara da malamai, ko ba komai su tayaki da addu'a dan ki samu bakali a wajen shi."
Tashi ta yi tsaye tace "Shikenan aunty Mariya, yanzu wannan kud'in ma ki rik'e a fara wani abun da su, yau ko gobe zan sa ya zo sai na samu kud'in, amma kar ki bari mama ta ji, kinsan halin ta yanzu sai tace ba ta yarda ba."
"Ni? Ina zan fad'a mata, ba ki ga sai da ta tashi ba ma na fad'a mi ki."
"To ni zan tafi su Zeinab na jira na."
"Sai kun dawo." Ta fad'a ta na bin ta da kallo.
*Allah ya fidda _Delu_😂 daga rogo.*
⏩⏩⏩⏩⏩⏩
Khadija kam a wajen bikin suna can har yamma, sai da su ka gama zubin da suke na k'awaye kafin su ka fito tare da Kaltume, motar ta su ka shiga ta bata wasu harkokin, kamar yanda ta san Khadija farin sani, ba ta anfani da kowane irin garin magani, musamman wanda za ace ayi matsi da shi, ta na sallamar ta ta fita daga motar ta rufe tace "Sai kin zo k'awata."
Kaltume ce tace "A'a k'awata, gaskiya ba na so na zo gidan ki yanzu, na fi so sai an fara shagulgulan bikin nan, lokacin na k'ara had'o mi ki wasu kayan."
Dariya Khadija ta yi tace "Ke fa muguwa ce, wato kullum burin ki kiga bawan Allah nan ya na gasa min aya a hannu ko? To daga wannan da na karb'a sai amarya ta zo ta haihu, idan za ta yi arba'in sai mu shirya tare."
Cikin d'aga murya Kaltume tace "Ina, ana babbak'ar gwiwa wa ke jiyo k'aurin zomo, ai dole yarinya ta gane da banbanci wallahi, wanda ya sa ta shigo gidan Khadija ta Usee, shi zai sa ta gane Khadija ta mata nisa na har abada."
Cikin dariya Khadija tace "Dan Allah k'awata ki ragawa yarinyar nan, har yanzu fa ba mu san ta ba bare mu san da me za ta shigo gidan ita ma."
Cike da gadara da tabbatarwa tace "Ai ko ni Kaltume za ta d'aura a k'ugun ta taje dani gidan, wallahi na riga da na bawa Khadija sirrin da za ta mata rata mai tsayin gaske."
"Na yarda, yanzu dai sai anjima, sai munyi waya ko?"
"To ba damuwa k'awata, ina k'ara fad'a mi ki dai, dan Allah banda nuna kishi a fili, ayi komai cikin kissa k'awata, ban da matsala da ke ta wannan fannin , amma kishi masifa ne wallahi."
"Hakane k'awata, kuma insha Allah zan kiyaye, nagode sosai."
"To, ki kula da kan ki."
"Kema haka."
Da haka ita ma ta shiga ta ta motar ta bar wajen, Khadija kuma ta na zuwa gida ta samu wannan kayan arzik'i, gidan su ta kira ta fad'a mu su, zuwa bayan sallah magrib kam sai ga maman ta da matan yayyun ta sun zo ganin kayan, hotunan su ta d'auka ta turawa k'awayen ta dan su gani suma ba sai sun zo ba, anan ne ma har su ka yi magana da maman ta a kan kayan d'aki da za ta canza, mahaifiyar da kan ta ta d'auki alhakin yi mata odar su daga k'asar waje, dan itama ta na so ta kece raini.
Sun fito dan tafiya Usmane ya shigo gidan, da gudu Bilal ya k'arasa ya rumgume shi, har k'asa ya duk'a ya gaishe da mama, mama ce tace "Kai yanzu da girman ka har ka ke wani mak'ale shi kamar yaro."
Hararan wasa Bilal ya aika mata yace "Kaji tsohuwar nan, ke ma fa idan na je gidan ki har d'auka ta ki ke."
Dafe k'irji ta yi tace "Kaji min sarkin sharri, ni kuma ina zan iya d'aukar ka? Ka fad'i abin da hankali zai d'auka mana."
"To ai dai Abba na ne ko." Ya fad'a ya na k'ara sarkafe wuyan Usman da har yanzu ke durk'ushe, ita ma kuma cewa ta yi "Ni ma kuma d'ana ne ba, kaga kuwa ba zan bari nima ka karya min yaro ba."
A hankali Usman ya kalli Bilal ya d'an janye shi daga jikin shi yace "Mama ta fika gaskiya, kowace uwa d'an ta ta sani, dan haka kowa ya je wajen maman sa, kai ma jeka ga ta ka can."
Kallon shi Bilal ya yi yace "Lallai ma Abba, za ka nemi ne ai har in da na ke, kafi kowa sanin cewa ni ne bugun zuciyar ka."
Wajen Khadija ya nufa ta d'auke shi saboda k'arfin hali duk da girman shi, mama kuma kallon Usman ta yi ta k'ara da "Mun ga kaya fa, a gaskiya sunyi sosai, sai dai kuma kayan kamar sunyi yawa, Allah ya k'ara bud'i na alkairi."
Ba tare da ya d'ago ba yace "Ameen ameen Hajia, ai ni ne da godiya, Allah ya saka da alkairi, Allah ya k'ara girma da lafiya."
"Ameen ameen." Mama ta amsa kafin Khadija ta d'ora da "Tofa, yanzu za ka fara godiyar ko?"
D'ago kai ya yi ya kalle ta yace "Ke kuma ba kya so ina godiyar ko?"
Hannaye ta d'aga tace "Allah ba ka hak'uri, ga ka ga su."
Mama kam wucewa su ka yi suna fad'in "Sai da safen ku."
Bilal da ke bayan Khadija ne ya d'aga musu hannu yace "Sauka lafiya, ko k'ofa ba zan raka ki ba bare ki sa ran samun na adaidaita."
Usman ne ya juyo ya kalle shi yace "Haihuwa maganin takaicin duniya, sai da ta haife ni kafin kai ma ka zo, dan haka da kai na zanyi dakon mahaifiyar ta har makwancin ta."
Dariya kawai su ke har su ka isa k'ofar gidan, cikin shagwab'a Khadija tace "Amma fa kar ku jima, ku yi sauri ku dawo."
Kafad'a ya mak'ale yace "Na k'i d'in."
Hararan shi ta yi tace "Za ka dawo ai ka same ni, zan kama ka a hannu."
Ba tare da ya bari mama ta gani ba ya mata gwalo yace "Ki kama ni d'in, ba zan shigo ba sai kinyi bacci."
"Bayan na rufe gida na ba." Ta fad'a kamar mai son tabbatar masa da za ta iya, haka dai ya d'auke su su ka wuce, mama ta so ya yi zaman shi su k'arasa titi su hau adaidaita, dan dama ko da *Naseer* ya kawo su sun fad'a mi shi za su koma da kansu, amma bai bari ba sai da ya kai su har k'ofar gida ya dire su, nan ma sai da ya fito daga motar ya sake mu su sallama kafin ya yi gaba, ya na kan hanyar shi kuma kiran amarya Haseenah ya shigo wayar shi, kashe kiran ya yi sannan ya sake kira da kan shi, ta na d'auka cikin ladabi tace "Amincin Allah ya tabbata a gare ka adali na."
Cikin jin dad'i yace "Kema haka, ya amarya ta take?"
Cikin siririyar murya tace "Da dad'i ba dad'i, amma daga yanda na ji karsashin muryar ka sai ya sa na ji wata tabbatacciyar lafiya na shiga jiki na."