Sashe 14
Kallon Kitse Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Shigewa kawai ta yi ta bar shi nan, saida ya ga shigar ta ya hau moton shi ya wuce shi ma, daga shi har ita babu mai jin wani bak'on alamari a game da d'an uwan na shi, tana shiga ciki ta samu yan uwanta su ka baje suna hirarsu kamar yanda su ka saba kullum, Khadija ce ta fara tashi ta je ta kwanta, har za su tashi sauran Ashir ya dakatar da su, bayan ya mu su bayani akan abin da ya gani ne ya d'ora da "Nasan Usman sosai, dan mun yi aji d'aya da shi, har yanzu baiyi aure ba saboda abin da ya sa a gaban shi, ganin shi tare da yer uwar mu alkairi, dan gaskiya na yarda da tarbiyar shi da kuma dattakon iyayensu, sai dai Usman ba kamar sauran maza bane, zai iya nuna cewa kamar Khadija ba tsararsa bace irin tafi k'arfin shi, ni kuma a gani na Khadija ce za ta yi sa'ar samun miji kamar shi, sannan burin mu anan dukanmu bai wuce mu bawa Khadija mijin daya dace da ita ba, sannan mun wa mahaifin mu alk'awarin kula da ita har zuwa lokacin da za mu damk'a ragamar kula da ita a hannun mijin da ya dace, da wannan nake neman shawararku da idan kun amince, sai mu je har gidansu Usman sannan mu nema wa yer uwar mu auren nagartattacen mutum, ba fad'uwa mu ka yi, kuma ba abun kunya bane dan mu muka fara zuwa da maganar, hakan ba yana nufin mun arhantar da ita bane, sai dai ma k'ok'arin kare mutumcinta, ko ya ku ka gani?"
Bashir ne yace "Tunda dai har ka yarda da shi ai ina ganin ba wani abu, kawai ayi d'in, burinmu shine ganin Khadija ta dawwama cikin farin ciki."
Kallon mama Ashir ya yi yace "Mama ba ki ce komai ba?"
Murmushi ta yi tace "Me zance ni, bayan iyayenta kuma yan uwanta sun gama magana, babu abin da zance sai dai addu'a da kuma fatan Allah sanya alkairi."
"Ameen mama." Suka amsa a tare, Ashir ne yace "Yanzu tunda dukan mu mun amince, gobe zan je na samu kawu *Kabir* na fad'a ma sa, in ya so sai muje tare, amma ku sani dukanmu za mu tafi neman auren nan."
Naseer ne yace "Kar ka damu ai, ni ne ma gaba saboda munfi kusa da ita."
Habeeb ne yace "Kai dallah can malam, kowa a gidan nan ai yasan Khadija tafi shak'uwa dani."
Wani wawan tsaki Ashir ya yi yace "Aikin banza, ai sai kuyi kuma, amma da yanzu za'a tambaye ta na tabbata ni ne farko."
Bashir ne yace "Hum! Kun manta sunan da ta ke kira na da shi ne?"
Dariya su ka yi sai Mansur ne yace "Dan ta kira ka da hannayenta sai me?"
"Sai ya na nufin mahimmanci na a gareta." Ya fad'a har da juya baki, dariya Mama ta yi ta Mik'e tace "Sai da safenku."
"Sai da safe mama." Su ka amsa.
*Wannan* k'aramar magana ita ce ta girmama har aka fara shigar da maganar aure tsakaninsu, sai da komai ya daidaita ana shirin kawo akwatina kad'ai yan uwan su ka sanar da Khadija a tunaninsu sun mata (surprise) za ta yi murna, Khadija ta girgiza, amma jin dalilinsu na yin haka domin farin cikin ta ne kawai, a lokacin kukan da take bawai na farin ciki bane, amma saita share ta nuna musu na dad'i ne take, dukansu ta had'a ta rumgume tace "Na yi sa'ar samunku a matsayin yan uwa."
A wajen Usman kuma har ya fara bore ya na nuna baya so, ya fad'a mu su kuskuren fahimta ne kawai, amma ko zaiyi aure yanzu ba yarinya kamar Khadija ya ke so ba, sai mahaifiyar shi ce ta zaunar da shi ta nusar da shi alfanu da alkairan da zasu iya tasowa sakamakon auren shi da Khadija, amma duk da haka sai da yace "Hajia, wallahi na tabbata ita ma yarinyar nan bata so na, zaifi kyau ku bar kowa ya zab'i wanda ya masa, amma kar ku ce za ku had'a mu saboda rashin fahimtar da Ashir ya yi."
Sosai ta tank'wara shi har ya samu ya sauko ya amince, amma yace saboda sune kawai, ita kuma mahaifiyar ce tace "In dai kuma har saboda mu kayi, to ka sani ba kai ba nadama har abada, insha Allahu wannan auren zai zamar maka alkairi, ba za ka tab'a kuka da zab'in mu ba."
Magana ta kankama sosai, amma ango da amarya babu wani mai shiri ko farin ciki, an saka wata *hud'u* mai zuwa, yan uwan amarya da mahaifiyar ta sun dage wajen shirin bikin autar su, gaisuwa kad'ai ke had'a Usman da Khadija a waya, su na gaisawa zata aje wayar ko shi ya aje, kuma kamar an k'yasta ashana sai gashi an cinye wannan lokacin da aka saka, ba dan Usman ya so ba ya baro harkokinshi ya zo sabgar bikin shi, fad'an irin tartsatsin da aka yi a bikin ma b'ata lokaci ne, dan yan uwa biyar sun yi bajinta sosai wajen k'ayatar da yer uwarsu, sai dai kamar yanda Usman ya ke ganin baiyi wani bajinta ba sosai, hakan ya sa yace ba ya buk'atar komai daga gare su shi ma sai amaryar kawai, hakan kuma ya birge mutane da dama, haka akayi wannan walima aka kai amarya d'akin mijinta, kuma duka yan uwa biyar d'in su suka saka k'anwar su tsaka suka iza k'eyar ta har ta shiga d'akin ta.
Gidan malam Ali da shima ya gada a wajen na shi tsohon, matsakaicin fili ne sai d'aki ciki da falo, sai ban d'aki a farfajiyar gidan da kuma k'aramar runfar da aka yi ta tôle aka aje kayan abinci ya zama wajen girki, d'akin nan tamtsam aka mi shi da kaya na gani na fad'a, bayan yan kai amarya su tafiyar su aka bar ango da amarya, shima fita ya yi kafin dare ya k'ara yi ya dawo gidan.
Zaune ya same ta akan gado fuskarta rufe, k'arasowa ya yi tare da "Amincin Allah ya tabbata a gare ki."
Wayu ta had'e ta rintse ido gabanta na fad'uwa tace "..
*Allah ka mana kyakyawan k'arshe.*
14/01/2020 à 14:03 - 💋😘💋: 💑💑💑💑💑💑💑💑💑💑
*KALLON KITSE*
_(Ake wa rogo)_
💑💑💑💑💑💑💑💑💑💑
_SAMIRA HAROUNA_
*Littatafan marubuciyar*
*1* _KAUSSAR_
*2* _D'AUKAR FANSA_
*3* _BA SO BANE_
*4* _AUREN HAD'I_
*5* _SANIN MASOYI_
*6* _JIHADI_
*7* _K'ANGIN RAYUWA_
*8* _ITACE K'ADDARARMU_
*9* _KAWU NA NE_
*10* _MAATA_
*11* _KALLON KITSE..._
*SADAUKARWA GA*
_MATAN FARKO_🧕🏼 *(UWAYEN GIDA)*
🇸🇦 *ZAMAN AMANA WRITER'S*
_(Gidan zaman lafiya da amana insha Allah)_🤜🤛
```Fatan alkairi masoya```
_Bismillahir rahamanir rahim_
*11*
"Kai ma haka."
A hankali ya zauna bakin gadon ya aje ledojin hannun shi, kallonta ya yi ya d'anyi shiru, dama dai fuskarta a rufe take, dan haka ita ma ta yi shiru, kowa da abin da yake sak'awa a ran shi, kusan minti sha biyar su ka d'auka a haka kafin ya sake kallonta ya d'anyi gyaran murya yace "Ko za ki iya bud'e fuskar ki."
Shiru ta yi kamar ba ta ji ba kuma bata bud'e ba, numfashi ya sauke cike da nuna kasala ya zuro hannayenshi ya yaye mayafin, fad'uwar gabanta ne ya nunku, shi kuma ya kafe fuskarta da babu ko d'igon kwalli da ido, sai dai lumshe ido ya yi saboda matsowar da ya yi kusanta k'amshin turaruka ne suka bigi hancin shi, ajiyar zuciya ya sauke yace "Ya kamata muje mu yi alwala ko?"
Ba tare da tace komai ba ta fito da k'afafun ta daga tank'warewar da ta mu su ta sauka daga kan gadon, bin bayanta ya yi su ka samu buta su ka yi alwala su ka dawo, hijab ta saka ta shinfid'a sallaya ya shiga gaba ya kabbara sallah, raka'a biyu su ka yi su ka sallame, juyowa ya yi ya na fuskantarta ya zuro hannunshi zai dafa kanta dan yin addu'a, zabura ta yi taja baya sosai, da sauri ya janye hannun shi yace "Lafiya?"
Girgiza kai ta yi alamar ba komai, shima girgiza kan ya yi yace "Kar ki damu, ba abinda zan miki, addu'a zan mana."
Gyara zamanta ta yi shi kuma ya rik'e kanta ya yi addu'a kamar haka _"Allahuma inni as'aluka khairuha wa khaira ma jabaltaha alaihi, wa a'uzu bika min sharriha wa sharri ma jabaltaha alaihi."_ Sakin ta ya yi ya juya ya janyo ledar gabanshi ya bud'e, har zata tashi yace "Zauna."
Yanda ta ji muryar shi ya sa ta zauna ba musu, gasassar kazar ya d'auka yakalle ta yace "Bismillah, ki ci."
Murya na rawa tace "Na k'oshi."
Da mamaki ya kalle ta yace "Kamar ya kin k'oshi? Nasan ki na jin yunwa, ga cikin ki nan ma ya nuna."
Da sauri ta k'ara k'udundune cikinta cikin hijabi ta na kallon k'asa, juyin duniya Usman ya yi amma tace ba ta cita k'oshi, abu d'aya ya fahimta shine tsoron shi take, sai dai tsoron me bai sani ba, saboda yanda had'uwar su ta kasance ne ko kuma tunanin zai mata wani abu a daren nan? Idan har hakane zaifi ta kwantar da hankalinta, ba ya da tunanin tauye hakk'in ta ko d'aya, sai dai ba zai kusance ta da wuri ba, dan haka ya mik'e yace "Zan fita waje, ki samu ki ci ko kad'an ne, idan kin gama za ki iya kwanciyar ki, ni zan kwanta a falo."
Ko d'agowa ba ta yi ba bare ta kalle shi, ta na ganin ya fita ta mik'e ta tura k'ofar d'akin ta rufe ba tare da ta saka makulli ba, rufe ledar kazar ta yi sannanta canza kayan jikin ta ta kashe fitila ta kwanta, ba tare da ta cire gilashinta ba ta shiga duniyar tunanin irin zaman da za ta yi da mutumin da ba ta so, da wannan tunanin bacci ya d'auke ta ba tare da ta cire gilashin ba, shi ma a falo ya zauna tunani iri-iri a zuciyar shi, daga bisani ya gaji ya kwanta bacci ya d'auke shi.
*Kiran sallah farko* Khadija ta farka, bayan ta yi salati tare da addu'ar tashi daga bacci _"Alhamdulillahi-lazi ahayana, ba'ada ma amatana, wa'ilaihi-nushur."_
Bashir ne yace "Tunda dai har ka yarda da shi ai ina ganin ba wani abu, kawai ayi d'in, burinmu shine ganin Khadija ta dawwama cikin farin ciki."
Kallon mama Ashir ya yi yace "Mama ba ki ce komai ba?"
Murmushi ta yi tace "Me zance ni, bayan iyayenta kuma yan uwanta sun gama magana, babu abin da zance sai dai addu'a da kuma fatan Allah sanya alkairi."
"Ameen mama." Suka amsa a tare, Ashir ne yace "Yanzu tunda dukan mu mun amince, gobe zan je na samu kawu *Kabir* na fad'a ma sa, in ya so sai muje tare, amma ku sani dukanmu za mu tafi neman auren nan."
Naseer ne yace "Kar ka damu ai, ni ne ma gaba saboda munfi kusa da ita."
Habeeb ne yace "Kai dallah can malam, kowa a gidan nan ai yasan Khadija tafi shak'uwa dani."
Wani wawan tsaki Ashir ya yi yace "Aikin banza, ai sai kuyi kuma, amma da yanzu za'a tambaye ta na tabbata ni ne farko."
Bashir ne yace "Hum! Kun manta sunan da ta ke kira na da shi ne?"
Dariya su ka yi sai Mansur ne yace "Dan ta kira ka da hannayenta sai me?"
"Sai ya na nufin mahimmanci na a gareta." Ya fad'a har da juya baki, dariya Mama ta yi ta Mik'e tace "Sai da safenku."
"Sai da safe mama." Su ka amsa.
*Wannan* k'aramar magana ita ce ta girmama har aka fara shigar da maganar aure tsakaninsu, sai da komai ya daidaita ana shirin kawo akwatina kad'ai yan uwan su ka sanar da Khadija a tunaninsu sun mata (surprise) za ta yi murna, Khadija ta girgiza, amma jin dalilinsu na yin haka domin farin cikin ta ne kawai, a lokacin kukan da take bawai na farin ciki bane, amma saita share ta nuna musu na dad'i ne take, dukansu ta had'a ta rumgume tace "Na yi sa'ar samunku a matsayin yan uwa."
A wajen Usman kuma har ya fara bore ya na nuna baya so, ya fad'a mu su kuskuren fahimta ne kawai, amma ko zaiyi aure yanzu ba yarinya kamar Khadija ya ke so ba, sai mahaifiyar shi ce ta zaunar da shi ta nusar da shi alfanu da alkairan da zasu iya tasowa sakamakon auren shi da Khadija, amma duk da haka sai da yace "Hajia, wallahi na tabbata ita ma yarinyar nan bata so na, zaifi kyau ku bar kowa ya zab'i wanda ya masa, amma kar ku ce za ku had'a mu saboda rashin fahimtar da Ashir ya yi."
Sosai ta tank'wara shi har ya samu ya sauko ya amince, amma yace saboda sune kawai, ita kuma mahaifiyar ce tace "In dai kuma har saboda mu kayi, to ka sani ba kai ba nadama har abada, insha Allahu wannan auren zai zamar maka alkairi, ba za ka tab'a kuka da zab'in mu ba."
Magana ta kankama sosai, amma ango da amarya babu wani mai shiri ko farin ciki, an saka wata *hud'u* mai zuwa, yan uwan amarya da mahaifiyar ta sun dage wajen shirin bikin autar su, gaisuwa kad'ai ke had'a Usman da Khadija a waya, su na gaisawa zata aje wayar ko shi ya aje, kuma kamar an k'yasta ashana sai gashi an cinye wannan lokacin da aka saka, ba dan Usman ya so ba ya baro harkokinshi ya zo sabgar bikin shi, fad'an irin tartsatsin da aka yi a bikin ma b'ata lokaci ne, dan yan uwa biyar sun yi bajinta sosai wajen k'ayatar da yer uwarsu, sai dai kamar yanda Usman ya ke ganin baiyi wani bajinta ba sosai, hakan ya sa yace ba ya buk'atar komai daga gare su shi ma sai amaryar kawai, hakan kuma ya birge mutane da dama, haka akayi wannan walima aka kai amarya d'akin mijinta, kuma duka yan uwa biyar d'in su suka saka k'anwar su tsaka suka iza k'eyar ta har ta shiga d'akin ta.
Gidan malam Ali da shima ya gada a wajen na shi tsohon, matsakaicin fili ne sai d'aki ciki da falo, sai ban d'aki a farfajiyar gidan da kuma k'aramar runfar da aka yi ta tôle aka aje kayan abinci ya zama wajen girki, d'akin nan tamtsam aka mi shi da kaya na gani na fad'a, bayan yan kai amarya su tafiyar su aka bar ango da amarya, shima fita ya yi kafin dare ya k'ara yi ya dawo gidan.
Zaune ya same ta akan gado fuskarta rufe, k'arasowa ya yi tare da "Amincin Allah ya tabbata a gare ki."
Wayu ta had'e ta rintse ido gabanta na fad'uwa tace "..
*Allah ka mana kyakyawan k'arshe.*
14/01/2020 à 14:03 - 💋😘💋: 💑💑💑💑💑💑💑💑💑💑
*KALLON KITSE*
_(Ake wa rogo)_
💑💑💑💑💑💑💑💑💑💑
_SAMIRA HAROUNA_
*Littatafan marubuciyar*
*1* _KAUSSAR_
*2* _D'AUKAR FANSA_
*3* _BA SO BANE_
*4* _AUREN HAD'I_
*5* _SANIN MASOYI_
*6* _JIHADI_
*7* _K'ANGIN RAYUWA_
*8* _ITACE K'ADDARARMU_
*9* _KAWU NA NE_
*10* _MAATA_
*11* _KALLON KITSE..._
*SADAUKARWA GA*
_MATAN FARKO_🧕🏼 *(UWAYEN GIDA)*
🇸🇦 *ZAMAN AMANA WRITER'S*
_(Gidan zaman lafiya da amana insha Allah)_🤜🤛
```Fatan alkairi masoya```
_Bismillahir rahamanir rahim_
*11*
"Kai ma haka."
A hankali ya zauna bakin gadon ya aje ledojin hannun shi, kallonta ya yi ya d'anyi shiru, dama dai fuskarta a rufe take, dan haka ita ma ta yi shiru, kowa da abin da yake sak'awa a ran shi, kusan minti sha biyar su ka d'auka a haka kafin ya sake kallonta ya d'anyi gyaran murya yace "Ko za ki iya bud'e fuskar ki."
Shiru ta yi kamar ba ta ji ba kuma bata bud'e ba, numfashi ya sauke cike da nuna kasala ya zuro hannayenshi ya yaye mayafin, fad'uwar gabanta ne ya nunku, shi kuma ya kafe fuskarta da babu ko d'igon kwalli da ido, sai dai lumshe ido ya yi saboda matsowar da ya yi kusanta k'amshin turaruka ne suka bigi hancin shi, ajiyar zuciya ya sauke yace "Ya kamata muje mu yi alwala ko?"
Ba tare da tace komai ba ta fito da k'afafun ta daga tank'warewar da ta mu su ta sauka daga kan gadon, bin bayanta ya yi su ka samu buta su ka yi alwala su ka dawo, hijab ta saka ta shinfid'a sallaya ya shiga gaba ya kabbara sallah, raka'a biyu su ka yi su ka sallame, juyowa ya yi ya na fuskantarta ya zuro hannunshi zai dafa kanta dan yin addu'a, zabura ta yi taja baya sosai, da sauri ya janye hannun shi yace "Lafiya?"
Girgiza kai ta yi alamar ba komai, shima girgiza kan ya yi yace "Kar ki damu, ba abinda zan miki, addu'a zan mana."
Gyara zamanta ta yi shi kuma ya rik'e kanta ya yi addu'a kamar haka _"Allahuma inni as'aluka khairuha wa khaira ma jabaltaha alaihi, wa a'uzu bika min sharriha wa sharri ma jabaltaha alaihi."_ Sakin ta ya yi ya juya ya janyo ledar gabanshi ya bud'e, har zata tashi yace "Zauna."
Yanda ta ji muryar shi ya sa ta zauna ba musu, gasassar kazar ya d'auka yakalle ta yace "Bismillah, ki ci."
Murya na rawa tace "Na k'oshi."
Da mamaki ya kalle ta yace "Kamar ya kin k'oshi? Nasan ki na jin yunwa, ga cikin ki nan ma ya nuna."
Da sauri ta k'ara k'udundune cikinta cikin hijabi ta na kallon k'asa, juyin duniya Usman ya yi amma tace ba ta cita k'oshi, abu d'aya ya fahimta shine tsoron shi take, sai dai tsoron me bai sani ba, saboda yanda had'uwar su ta kasance ne ko kuma tunanin zai mata wani abu a daren nan? Idan har hakane zaifi ta kwantar da hankalinta, ba ya da tunanin tauye hakk'in ta ko d'aya, sai dai ba zai kusance ta da wuri ba, dan haka ya mik'e yace "Zan fita waje, ki samu ki ci ko kad'an ne, idan kin gama za ki iya kwanciyar ki, ni zan kwanta a falo."
Ko d'agowa ba ta yi ba bare ta kalle shi, ta na ganin ya fita ta mik'e ta tura k'ofar d'akin ta rufe ba tare da ta saka makulli ba, rufe ledar kazar ta yi sannanta canza kayan jikin ta ta kashe fitila ta kwanta, ba tare da ta cire gilashinta ba ta shiga duniyar tunanin irin zaman da za ta yi da mutumin da ba ta so, da wannan tunanin bacci ya d'auke ta ba tare da ta cire gilashin ba, shi ma a falo ya zauna tunani iri-iri a zuciyar shi, daga bisani ya gaji ya kwanta bacci ya d'auke shi.
*Kiran sallah farko* Khadija ta farka, bayan ta yi salati tare da addu'ar tashi daga bacci _"Alhamdulillahi-lazi ahayana, ba'ada ma amatana, wa'ilaihi-nushur."_