← Book details Kallon Kitse Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 34 OF 86

Sashe 34

Kallon Kitse Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Haka rayuwar gidan Usman ke tafiya da dad'i wasu lokutan kuma sai a sannu, sai dai yanzu Haseenah ta d'an shiga taitayin ta ba ta cika shiga harkar Khadija ba bare har ta fad'a mata magana, Khadija kuma dama rayuwar ta take yi babu ruwanta da ita, Bilal ma na wajen kakanin shi hankali kwance ya na zuwa islamiyyar shi, ranar talata da yamma Khadija ta saki aiki Haseenah ta kama, sosai Usman ya yarda Khadija ita ce ta san shi farin sani, bayan kwana biyu ita ma ta saki aiki a ranar alhamis ta saki aiki Khadija ta kama, a ranar kuma ta kama ranar sunan matar Issoufou, tunda rana Usman yace su tafi tare tunda Khadija na da mota, sannan ta san gidan sab'anin Haseenah da zuwan ta d'aya kuma cikin dare.

Tun Khadija na jiran ta kammala aiki su tafi dan ta samu ita ma ta dawo ta kama na ta aikin har ta gaji da jira, ganin ba kowa a gidan da zata aika ya sa ta sallama da kan ta har falon ta, Haseenah da ke uwar d'aka kwance ta amsa sallamar tare da fitowa, ta na ganin Khadija ta ja birki k'ofar d'akin ta na k'are mata kallo, da mamaki Khadija ta kalle ta ganin ko wanka ma ba ta yi ba, cikin dakiya tace "Wai Haseenah ba ki shirya bane?"

A kasalance ta amsa da "Ban shirya ba."

Jin ba ta sake cewa komai ba ya sa tace "To dan Allah ki gaggauta ki shirya mu wuce, wallahi ba dan ke ba ma ni ban tab'a kai wannan lokacin ba ban fita ba, musamman da nasan zanyi aiki."

"To." Haseenah ta fad'a ta juya kawai ta koma ciki, Khadija na ganin haka ta fito ta na mita, a k'alla ta sake b'ata minti talatin ba Haseenah ba labarin ta, ran ta ne ya kai matuk'a wajen b'aci kawai ta d'auki jakar ta ta fita, Haseenah na jin fitar Khadija ta fito ta rufe d'aki dan dama ta shirya tunda ta mata magana, kawai ba ta yi ra'ayin fitowa da wuri bane, har farfajiyar gidan ta fito ta samu mai gadi tace "Wai har ta tafi ne?"

Cikin girmamawa yace "Yanzun nan kam ta fita, dan ga motar can ko titi ba ta hau ba."

Wayar ta ta ciro cikin jaka ta dannawa Usman kira, ya na d'auka ta fad'a mi shi ya zo ya d'auke ta Khadija ta tafiyar ta, da mamaki yace "Wai dama har yanzu ba ki fita daga gidan ba?"

Cikin turo baki tace "Na shirya fa na ke ta jira aunty Khadija ta min magana, tunda ai ba zuwa zanyi ba na tisa ta a gaba har sai ta gama shirin ta, ina falo kawai sai fitar ta na ji."

Ba dan ya yarda da abin da ta fad'a ba yace ta jira shi ya zo ya d'auke ta, dan in dai Khadija za ta fita to bata kaiwa warhaka bata fita ba saboda taje ta dawo da wuri ta kama aikin gaban ta, hanya ya d'auko dan ya zo ya d'aukar ta ya kira Khadija a waya, bayan ta d'auka ne yace "K'anwar ki ta kira ni tace wai kin tafi kin barta, shine na ce ya akayi haka ta faru?"

Khadija da ke tuk'i ne tace "Ba ta fad'a ma ka na kai mak'ura bane wajen jiran ta? Ko kuma kawai ta fad'a ma ka abin da ta ga dama ne?"

Murmushi ya yi daga in da ya ke yace "Ran gimbiya ya huce, kawai dai ina tambaya ne."

Cike da rashin kulawa tace "Ka ga ina tuk'i fa, sai munyi magana."

Kasje wayar ta yi ta ci gaba da abin da take, shima kuma d'auko Haseenah ya yi sai dai bai fad'a mata yanda su ka yi da Khadija ba har suka isa ya sauke ta, da d'ar-d'ar ta shiga gidan bikin ta na sallama wata bayan wata, cikin sa'a ta hango su Hassana da Husseina da duk sauran yan uwan tare da Hajia sarakuwar su zaune, da azama ta isa can ta zauna su ka gaisa, Rabi'a ce ta fara tambayar ta da "...

*Ku yi hak'uri masoya abisa jinkiri na, hakan na faruwa ne sakamakon al'amura da su ke sha min kai na.*👏
04/02/2020 à 21:00 - 💋😘💋: 💑💑💑💑💑💑💑💑💑💑
*KALLON KITSE*
_(Ake wa rogo)_
💑💑💑💑💑💑💑💑💑💑

_SAMIRA HAROUNA_

*Littatafan marubuciyar*

*1* _KAUSSAR_
*2* _D'AUKAR FANSA_
*3* _BA SO BANE_
*4* _AUREN HAD'I_
*5* _SANIN MASOYI_
*6* _JIHADI_
*7* _K'ANGIN RAYUWA_
*8* _ITACE K'ADDARARMU_
*9* _KAWU NA NE_
*10* _MAATA_
*11* _KALLON KITSE..._

*SADAUKARWA GA*

_MATAN FARKO_🧕🏼 *(UWAYEN GIDA)*

🇸🇦 *ZAMAN AMANA WRITER'S*
_(Gidan zaman lafiya da amana insha Allah)_🤜🤛

```Fatan alkairi masoya```
*🇸🇦ZAMAN AMANA WRITER'S*
(GIDAN ZAMAN LAFIYA DA AMANA INSHA ALLAH)🤜🤛

*SANARWA! SANARWA!! SANARWA!!!*

*INA JIGA JIGAN MASOYAN 🇸🇦ZAMAN AMANA WRITER'S WAD'ANDA BASU DA TAMKA A WAJENMU????? DUK WANDA YAKE TARE DAMU A CIKIN GROUPS D'INMU TO MUN TABBATAR K'AUNARMU CE TASA KUKA KASANCE TARE DAMU, MUNA YABAWA KUMA HAR ABADA BAMU DA KAMARKU WALLAHI,👍 DUK DA HAKA DAI GA LOKACI YAZO, KUMA DAMA TA SAMU NA TABBATAR MANA DA KUMA NUNA MANA HAK'IK'ANIN K'AUNAR DA KUKE MANA,👇*

Kunsan cewa k'ungiyarmu *🇸🇦ZAMAN AMANA WRITER'S* suna cikin gagarumin gasa na samun award Wanda *women24 TV WhatsApp group* suka shirya kuma zasu gudanar?

A wannan gasar ne za'a samu k'ungiyar da tafi kowacce k'ungiya yawan fans da Kuma bin k'a'idar rubutu

Dan ki samu damar zabar k'ungiyarmu *🇸🇦ZAMAN AMANA WRITER'S ASSOCIATION* zaki iya tuntub'ar wannan lambar 09030159301 Dan su saki a *WOMEN24 TV WHATSAPP GROUP* anan ne za'ayi zab'en k'ungiyar da tafi kowacce k'ungiya yawan masoya

*Women24 Tv*
Ba zabe kad'ai zakiyi ba

Zaki k'aru da abubuwa da yawa kamar haka

*Yanda ake girke girke*
*yanda zaki gyara jikinki*
*yanda zakiyi makeup*
*yanda zaki daura Dan kwali*

Kuma suna shirye shiryen nan na *arewa24 tv* kamar su

*TARKON KAUNA*
*DADIN KOWA*
*KWANA CHASA'IN*
*JAMAI RAJA*
*SAPNE SUHANE*
*GIDAN BADAMASI*
*RUDIN ZUCIYA*
*BAGHYA LAKSHMI*
*AKUSHI DA RUFI*
*AUDIO NOVEL*
*HAUSA NOVELS*

Kada ki manta da ranar zabe inkin shiga group d'in ki zaba *🇸🇦ZAMAN AMANA WRITER'S* tanan ne zaki iya nuna mana irin sonda kuke ma k'ungiyarmu da littattafammu

Allah yabar zumunci🤝😍🥰💋

_Bismillahir rahamanir rahim_

*19*

"Haseenah ke kad'ai ki ka taho ne?"

Da kunya ta kalle ta tace "A'a, shi ya kawo ni ai, da tare da aunty Khadija zamu taho, to kuma bansan tafiyar ta ba."

Ai kuwa abin da ta fad'a ya samu shiga sosai, hakan ya sa Hassana cewa "Amma yasan za ku taho tare?"

"Eh ya sani, shi yace ma mu taho tare tunda safe."

Rabi'a ce tace "Amma kuma dan rashin mutumci shine ta taho ta baro ki? Lallai ma matar nan, kullum iskancin ta k'aruwa ya ke."

Husseina ce tace "To ba ita ke da mota ba, kinga kuwa dole ta yi yanda ta so."

"Hum." Cewar Hassana, cike da wauta Aziza tace "Wallahi kema kar ki yarda ya siya mi ki ko moto ne, dan ba za ki zauna ta na mulkar ki ba."

Hajia ce ta kalli Haseenah tace "Ki shiga wajen mai jegon mana ku gaisa."

"To Mama." Ta fad'a ta na mik'ewa, cike da dattako Hajia ta sake cewa "In ce dai ya baki abin da za ki kaiwa mai jegon?"

'Yar dariya ta yi tace "Eh Mama, tunda safe ma ba bamu dukan mu."

Hajia na ganin wucewar ta ta kalle su dukan su tace "Yanzu mi ye anfanin haka? Wannan yarinyar yaushe ta shigo cikin ahalin ku da har ku ka yarda da ita haka? Mi ye Khadija ba ta mu ku ba a rayuwa da har ku ka butulce ma ta haka? Dukan ku fa mata ne, kuma Rabi'a ce kad'ai ba ta da abokiyar zama a ciki, ke kan ki Aziza da ki ke wata banzar magana na ga saurayin da ki ke so ai mata gare shi, shin idan aka mu ku haka za ku ji dad'i? Nace za ku ji dad'i idan aka mu ku haka? Ba za ku ji ba kenan? Shine kuma ku ke wa wata rashin kunya wacce ta mu ku alkairin da ki shi d'an uwan na ku bai mu ku kamar shi ba, shi d'an uwan na ku kunsan yanda ya ke d'aukar ta da kuma matsayin ta a wajen shi? Ku kan ku da akwai mutumci ai Khadija tafi k'arfin komai a wurin ku, wallahi ta wuce cin mutumci da cin zarafi, ko ba komai mafi soyuwar abu a zuciyar d'an uwan ku shine d'an wannan matar da ku ka raina, sannan ina yak'ini akai ko tamtama babu cewar Khadija ma tafi soyuwa a zuciyar d'an uwan ku, idan kuma kun shirya rasa shi ne to dan Allah ku ci gaba da mata rashin kunya, ni dai na fad'a mu ku gaskiya a matsayi na na uwa, kuma ke Aziza."

Hajia ta fad'a ta na nuna Aziza da hannu kafin ta ci gaba da "Kar na sake jin bakin ki daga yau in har su na maganar su, tunda ke kinfi kowa butulcia cikin su, Aziza matar nan har kashi da fitsarin ki ta ci kamar yanda ni ma na ci, matar nan ta kwantar da ke a gaban k'irjin ta kamar 'yar da ta haifa, matar nan ta mi ki wanka da hannayen ta ta shirya ki, duk lokacin da mijin ta baya nan ke ce abokiyar rayuwar ta, har rayuwa ta canza mu su ta haifi nata yaron ba ta banbanta ki da shi ba, Aziza sai da aka kai k'adamin da ta ware mi ki d'aki a gidan ta, kinfi kowa sanin Khadija a cikin dangin mu, amma kash ke ce farko wajen juya mata baya, Allah ya kyauta."

Ta na fad'a mik'ewa ta yi daga kan kujerar ta koma wajen wasu tsofi ta zauna, su kam tabbas jikin su ya yi sanyi, sai dai a ganin su duk cikin sharrin Khadija ne, Husseina ce tace "Gaskiyar Hajia, wallahi duk ranar da yah Fodio ya ji maganar nan a bakin mu, to fa kashin mu ya bushe."
Chapter 34 · 0% Book details