Sashe 83
Kallon Kitse Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
B'angare d'aya kuma su Kaltume na sama suna gyara wajen da za'a gabatar da walimar dare wacce su ka shirya ma Usee, a haka har dare ya riske su lokacin mutane sun watse sai masu aiki da aka samu suna share gidan, nan fa aka sake sabon shiri in da Khadija ta sake d'aukar wata sabuwar kwalliya wacce ta ci kud'i sosai, Aisha da Humaira ma shiryasu akayi cikin kaya iri d'aya kuma kalar na iyayen su da Bilal, Haseenah da Khadija ma cikin wanda Usman ya d'inka mu su suka saka kala d'aya, nan suka kira Usman a waya wai ya zo gida ba lafiya, a gigice ya tambayi me ya faru? Sai kawai su ka kashe wayar suna dariya, Usman dama walima ya yi sosai shima haka ya tsallako abokan shi ya taho gidan a sukwane, d'akin shi ya nufa ya na shiga ya same su zaune sai hira suke, matsowa ya yi ya na fad'in "Lafiya? me ya faru ne?"
Tare su ka taso Haseenah na cire mi shi hula Khadija kuma riga tace "Ba komai, wanka za ka yi ka yi sabuwar kwalliya."
Duka da mamaki ya kalle su yace "Kwalliya kuma, kamar wata mace? Kwalliyar me?"
Khadija ce ta d'ora mi shi hannu a yatsa tace "Shiiiii, ba magana."
Iska ya furzar yace "Wallahi kun d'auki alhaki na, haka kawai kun tayar min da hankali."
Kallon shi Khadija ta yi cike da shagwab'a tace "Ka yafe mana to." Turo baki ya yi gaba yace "Na k'i d'in."
B'ata rai ta yi ta tisa k'eyar shi ta kalli Haseenah tace "Shiga da shi ciki ki wanke min shi tas, kafin ku fito zan fito mi shi da kaya."
Ba musu suka shiga ban d'aki ta taya shi wanka, ita kuma kaya ta fito mi shi da su kalar na su sai dai ba iri d'aya ba, haka suka fito suka shirya shi kamar wani sarki ko kuma yaro, tsaf su ka yi da su kafin suka fito dan hallara wajen taron wanda a wannan lokacin ya samu halartar manyan bak'in da aka gayyata har daga mak'ota *nigeria* ma, Humaira na hannun Aishatu in da Aisha ke hannun Mariya, haka suka haura sama cikin shiga ta alfarma gwanin birgewa, sai lokacin Usman ya saki baki ya na kallon ikon Allah, tuni hankalin shi ya koma kan wani rubutu da akayi da manyan bak'i aka saka *HAPPY BIRHTDAY GARKUWAR MU*, sunkuyawa ya yi wajen Khadija yace "Aikin ki ne ko?"
Ita ma matso da kanta ta yi tace "Ba ruwa na ni, nima gani kawai na yi."
Tun kafin su isa wajen zamansu Khadija ta hango manyan bak'in da ta gayyata, nima dai baza ido na yi sosai saboda ganin wurin ya cika da mazan hajiyoyi sosai, mamaki ne ya kamani ganin wasu manyan mutane a gefe, haba ai saina bar bin bayan su Khadija na tafi da sauri wani tebur, domin tabbatarwa kaina da gaskiyar abin da na ke gani yasa na k'arasa na tsaya na ce " *Kaussar*." (jarumar littafin *Kaussar*).
Ai kam da sauri ta juyo ta kalle ni, da farin ciki ta mik'e tsaye ta rumgume ni tace "Aunty Meera, ke ce? Me kika zo yi anan?"
Kafin na yi magana daga bayan Kaussar aka ce "Me fa ta zo yi daya wuce d'aukar shegen rahoton nan nata da ta saba yi na jaraba, ko gajiya ba ta yi ta na bi gida-gida ta na wa ma'aurata bin k'wak'waffi."
Wa zan gani in ba *Ahmad* ba, k'ara waro ido na yi saboda ganin ya k'ara k'iba, sai dai ya k'ara haske sosai abinka ga jan buzu kuma balarabe, sai uban k'asumbar nan sai walk'iya take bak'i k'irin, tab'e baki na yi na dalla mi shi harara na ce "Can ta matse ma ka dai, kuma in da ba na d'auko labarin ai da ban d'auko na ku ba."
Shima cikin hararan ta yace "To kin d'auka gata ne ki ka mana, bayan kin gama kalle min mata."
Sama da k'asa na harare shi na ce "Ikon Allah." Kallon Kaussar na yi na ce "Wai yaushe bagwarin mijin nan naki ma ya iya haussa ne haka?"
Dariya Kaussar ta yi ta koma ta zauna kafin tace wani abu yace "Ranar da ki ka zaunar da ni ki ka koya min."
Nuna shi na yi da hannu na ce "Allah ka kiyaye ni ko na sa a k'wace matar ta ka sannan ka koma inda ka fito."
Dariya ya yi wacce ta k'ara bayyanar da tsantsar kyawun shi yace "Bismillah idan kin isa, ke ki na ganin kin isa ki datse wannan auren? To yanzu haka yaro ta baro gida wanda take bawa nono, kinga kuwa ni da ita ba rabuwa sai mutuwa."
Sama da k'asa na sake hararan shi na yi gaba ina kallon Kaussar na ce "Za mu yi magana idan mijin nan na ki ya yi bacci."
Da dariya ya bini da kallo ya na fad'in "Sakaran ina ne ni zanyi bacci a wannan taron, bayan akwai irin su *Najib* (jarumin littafin *D'aukar fansa*)a wurin nan."
Da sauri Kaussar ta rufe mi shi baki saboda su na kusa da su Najib, ni kuma sake ware ido na yi dan naga ina ya ke, ai kam baifi tako hud'u ba na iso ga teburin shi, kallon shi na ke sosai tare da kyawawan matan da su ka saka shi tsakiya su biyu, da murmushi a fuska na ce "Alhaji Najib barka da dare."
Wani mummunan fad'uwa gaba na ya yi saboda kallon da ya watso min kamar kumurci, d'auke kan shi ya yi k'ala baice min ba dan haka na kalli *zarah* na ce "My Zarah sannu ko?"
Da murmushi sosai tace "Sannu aunty Meera, ya ki ke? Me ki ke anan? Ke ma aunty Khadija ta gayyace ki ne?"
"Eh...t..." Ban k'arasa ba Najib yace "Har sai kin tambaye ta me ta ke anan? Gulma mana ta kawo ta, ko kin manta anyi drima a gidan Usee watannin baya da su ka wuce?"
Murmushi kawai Zarah ta yi sai *Yasmine* da tace "Ko da gulma ce ta kawo ta ai kam ta yi anfani, dan nasan akwai dayawa masu irin halin Haseenah wanda za su gyara."
Kashe mata ido na yi na ce "Da kyau tawaje na kin gane, ba zan tsaya b'ata lokaci da wannan mijin na ku ba mai k'aton ciki kamar kun aza mi shi randa."
Da k'arfi ya juyo zaiyi magana Zarah ta rik'e tace "Haba beby ya isa mana, rabu da ita dan Allah."
K'wafa ya yi ya zauna ya na huci, ni kam ko a jiki na sai ma gaba da na yi na bar shi da masifar shi, kamar daga sama na ji na yi karo da k'afar wani, da sauri naja baya ina fad'in "Ayyah sannu ko, yi hak'uri dan Allah ban..."
Bai k'arasa ba saboda ganin *Saif* (jarumin littafin *Ba so bane*) sai dokan uban murmushi yake ya na kallo na, ajiyar zuciya na sauke dan nasan ba matsala, da dai sauran mazan hajjajan ne da ban san me zai faru ba, kafin ya yi magana *Zeinab* tace "Lah aunty Meera ke ce? Me ki ke anan?"
Izuwa yanzu kam na fara gajiya wannan tambayar da kowa ke min ta me ya kawo ni, amma sai na dake na ce "Ni ma na zo bikin Khadija ne."
Da wannan murmushi Saif yace "Ko kuma suma idon ki ka saka mu su ba kamar yanda ki ke wa kowa."
Kallon shi na yi na ce "Haba Saif ya za ka ce haka, kaine fa na ke gani mai hankali a cikin sauran."
Waro ido ya yi yace "Au! Wai ki na nufin sauran duk mahaukata ne?"
Kau da kai na yi na ce "Ka ga ni dai bance ba kar ka ja min sharri."
Juyawa ya yi bayan shi yace " Bara na ga ina zanga aboki na na fad'a mi shi kin ce mahaukata ne su."
Da sauri na bar wajen ina fad'in "Shi ma dai ya lalace kamar sauran, nasan kuma ba zai rasa nasaba da wannan bigaggen *Salman* (jarumin littafin *Auren had'i*) d'..."
Ai dole naja birki domin kuwa karo na yi da Salman d'in, wani kallo ya min yace "Ni ne ma bigaggen?"
Murmushin dole na yi na ce "Ah haba dai, ni na isa na kira ka da bigagge, dama da Saif na ke."
Dafe k'irji ya yi yace "Abokin nawa ne bigagge kenan?"
Zanyi magana naji andafa ni ta baya ance "Aunty Meranmu dan Allah rabu da su, wahalar da ke kawai za su yi."
Baki na.saki saboda ganin *Ummi* ta zama wata babba kuma hamshak'iyar mace, kallon Salman na yi a raina ina raya koya yake ya na iya d'aukar ta ma yanzu? Hum, kallon ta na yi na ce "Ummi na ina 'yan biyu?"
Da murmushi a fuskarta tace "Yan biyu su na wajen su lamama, amma ya na gan ki anan? Me ki ke yi?"
Salman ne ya juya ya zauna kan kujerar da suka tashi ya na fad'in "Me fa zai kawota da ya wuce d'aukar rahoton da ta saba, ta na nan kullum ta k'i canzawa sai tsukewa take, Allah ya sa wayar taki ta fad'i sai mu ga ta tsiya."
Wata dariyar rainin hankali na mi shi na ce "Ka ji malam Salmanu, wato so ka ke na zuma b'ukekiya kamar matar ka, to ni mijina ba ya buk'atar na yi k'iba haka yake son gani na, sannan da ka ke fatan wayata ta fad'i to in fad'a ma ka ta na fad'uwa wallahi sai ka biya ni, in kuma ba haka ba zansa Ummi ta ma bore har sai an sake ma ka tiyata, ai dai ka gane tiyatar da na ke nufi ko?"
Ta fad'a ta na kashe mi shi ido d'aya, baki ya saki ya na kallo na har na wuce na bar shi, saida na b'acewa ganin shi ya kalli Ummi yace "Kuma ke sai kiyi idan ta saki?"
Tare su ka taso Haseenah na cire mi shi hula Khadija kuma riga tace "Ba komai, wanka za ka yi ka yi sabuwar kwalliya."
Duka da mamaki ya kalle su yace "Kwalliya kuma, kamar wata mace? Kwalliyar me?"
Khadija ce ta d'ora mi shi hannu a yatsa tace "Shiiiii, ba magana."
Iska ya furzar yace "Wallahi kun d'auki alhaki na, haka kawai kun tayar min da hankali."
Kallon shi Khadija ta yi cike da shagwab'a tace "Ka yafe mana to." Turo baki ya yi gaba yace "Na k'i d'in."
B'ata rai ta yi ta tisa k'eyar shi ta kalli Haseenah tace "Shiga da shi ciki ki wanke min shi tas, kafin ku fito zan fito mi shi da kaya."
Ba musu suka shiga ban d'aki ta taya shi wanka, ita kuma kaya ta fito mi shi da su kalar na su sai dai ba iri d'aya ba, haka suka fito suka shirya shi kamar wani sarki ko kuma yaro, tsaf su ka yi da su kafin suka fito dan hallara wajen taron wanda a wannan lokacin ya samu halartar manyan bak'in da aka gayyata har daga mak'ota *nigeria* ma, Humaira na hannun Aishatu in da Aisha ke hannun Mariya, haka suka haura sama cikin shiga ta alfarma gwanin birgewa, sai lokacin Usman ya saki baki ya na kallon ikon Allah, tuni hankalin shi ya koma kan wani rubutu da akayi da manyan bak'i aka saka *HAPPY BIRHTDAY GARKUWAR MU*, sunkuyawa ya yi wajen Khadija yace "Aikin ki ne ko?"
Ita ma matso da kanta ta yi tace "Ba ruwa na ni, nima gani kawai na yi."
Tun kafin su isa wajen zamansu Khadija ta hango manyan bak'in da ta gayyata, nima dai baza ido na yi sosai saboda ganin wurin ya cika da mazan hajiyoyi sosai, mamaki ne ya kamani ganin wasu manyan mutane a gefe, haba ai saina bar bin bayan su Khadija na tafi da sauri wani tebur, domin tabbatarwa kaina da gaskiyar abin da na ke gani yasa na k'arasa na tsaya na ce " *Kaussar*." (jarumar littafin *Kaussar*).
Ai kam da sauri ta juyo ta kalle ni, da farin ciki ta mik'e tsaye ta rumgume ni tace "Aunty Meera, ke ce? Me kika zo yi anan?"
Kafin na yi magana daga bayan Kaussar aka ce "Me fa ta zo yi daya wuce d'aukar shegen rahoton nan nata da ta saba yi na jaraba, ko gajiya ba ta yi ta na bi gida-gida ta na wa ma'aurata bin k'wak'waffi."
Wa zan gani in ba *Ahmad* ba, k'ara waro ido na yi saboda ganin ya k'ara k'iba, sai dai ya k'ara haske sosai abinka ga jan buzu kuma balarabe, sai uban k'asumbar nan sai walk'iya take bak'i k'irin, tab'e baki na yi na dalla mi shi harara na ce "Can ta matse ma ka dai, kuma in da ba na d'auko labarin ai da ban d'auko na ku ba."
Shima cikin hararan ta yace "To kin d'auka gata ne ki ka mana, bayan kin gama kalle min mata."
Sama da k'asa na harare shi na ce "Ikon Allah." Kallon Kaussar na yi na ce "Wai yaushe bagwarin mijin nan naki ma ya iya haussa ne haka?"
Dariya Kaussar ta yi ta koma ta zauna kafin tace wani abu yace "Ranar da ki ka zaunar da ni ki ka koya min."
Nuna shi na yi da hannu na ce "Allah ka kiyaye ni ko na sa a k'wace matar ta ka sannan ka koma inda ka fito."
Dariya ya yi wacce ta k'ara bayyanar da tsantsar kyawun shi yace "Bismillah idan kin isa, ke ki na ganin kin isa ki datse wannan auren? To yanzu haka yaro ta baro gida wanda take bawa nono, kinga kuwa ni da ita ba rabuwa sai mutuwa."
Sama da k'asa na sake hararan shi na yi gaba ina kallon Kaussar na ce "Za mu yi magana idan mijin nan na ki ya yi bacci."
Da dariya ya bini da kallo ya na fad'in "Sakaran ina ne ni zanyi bacci a wannan taron, bayan akwai irin su *Najib* (jarumin littafin *D'aukar fansa*)a wurin nan."
Da sauri Kaussar ta rufe mi shi baki saboda su na kusa da su Najib, ni kuma sake ware ido na yi dan naga ina ya ke, ai kam baifi tako hud'u ba na iso ga teburin shi, kallon shi na ke sosai tare da kyawawan matan da su ka saka shi tsakiya su biyu, da murmushi a fuska na ce "Alhaji Najib barka da dare."
Wani mummunan fad'uwa gaba na ya yi saboda kallon da ya watso min kamar kumurci, d'auke kan shi ya yi k'ala baice min ba dan haka na kalli *zarah* na ce "My Zarah sannu ko?"
Da murmushi sosai tace "Sannu aunty Meera, ya ki ke? Me ki ke anan? Ke ma aunty Khadija ta gayyace ki ne?"
"Eh...t..." Ban k'arasa ba Najib yace "Har sai kin tambaye ta me ta ke anan? Gulma mana ta kawo ta, ko kin manta anyi drima a gidan Usee watannin baya da su ka wuce?"
Murmushi kawai Zarah ta yi sai *Yasmine* da tace "Ko da gulma ce ta kawo ta ai kam ta yi anfani, dan nasan akwai dayawa masu irin halin Haseenah wanda za su gyara."
Kashe mata ido na yi na ce "Da kyau tawaje na kin gane, ba zan tsaya b'ata lokaci da wannan mijin na ku ba mai k'aton ciki kamar kun aza mi shi randa."
Da k'arfi ya juyo zaiyi magana Zarah ta rik'e tace "Haba beby ya isa mana, rabu da ita dan Allah."
K'wafa ya yi ya zauna ya na huci, ni kam ko a jiki na sai ma gaba da na yi na bar shi da masifar shi, kamar daga sama na ji na yi karo da k'afar wani, da sauri naja baya ina fad'in "Ayyah sannu ko, yi hak'uri dan Allah ban..."
Bai k'arasa ba saboda ganin *Saif* (jarumin littafin *Ba so bane*) sai dokan uban murmushi yake ya na kallo na, ajiyar zuciya na sauke dan nasan ba matsala, da dai sauran mazan hajjajan ne da ban san me zai faru ba, kafin ya yi magana *Zeinab* tace "Lah aunty Meera ke ce? Me ki ke anan?"
Izuwa yanzu kam na fara gajiya wannan tambayar da kowa ke min ta me ya kawo ni, amma sai na dake na ce "Ni ma na zo bikin Khadija ne."
Da wannan murmushi Saif yace "Ko kuma suma idon ki ka saka mu su ba kamar yanda ki ke wa kowa."
Kallon shi na yi na ce "Haba Saif ya za ka ce haka, kaine fa na ke gani mai hankali a cikin sauran."
Waro ido ya yi yace "Au! Wai ki na nufin sauran duk mahaukata ne?"
Kau da kai na yi na ce "Ka ga ni dai bance ba kar ka ja min sharri."
Juyawa ya yi bayan shi yace " Bara na ga ina zanga aboki na na fad'a mi shi kin ce mahaukata ne su."
Da sauri na bar wajen ina fad'in "Shi ma dai ya lalace kamar sauran, nasan kuma ba zai rasa nasaba da wannan bigaggen *Salman* (jarumin littafin *Auren had'i*) d'..."
Ai dole naja birki domin kuwa karo na yi da Salman d'in, wani kallo ya min yace "Ni ne ma bigaggen?"
Murmushin dole na yi na ce "Ah haba dai, ni na isa na kira ka da bigagge, dama da Saif na ke."
Dafe k'irji ya yi yace "Abokin nawa ne bigagge kenan?"
Zanyi magana naji andafa ni ta baya ance "Aunty Meranmu dan Allah rabu da su, wahalar da ke kawai za su yi."
Baki na.saki saboda ganin *Ummi* ta zama wata babba kuma hamshak'iyar mace, kallon Salman na yi a raina ina raya koya yake ya na iya d'aukar ta ma yanzu? Hum, kallon ta na yi na ce "Ummi na ina 'yan biyu?"
Da murmushi a fuskarta tace "Yan biyu su na wajen su lamama, amma ya na gan ki anan? Me ki ke yi?"
Salman ne ya juya ya zauna kan kujerar da suka tashi ya na fad'in "Me fa zai kawota da ya wuce d'aukar rahoton da ta saba, ta na nan kullum ta k'i canzawa sai tsukewa take, Allah ya sa wayar taki ta fad'i sai mu ga ta tsiya."
Wata dariyar rainin hankali na mi shi na ce "Ka ji malam Salmanu, wato so ka ke na zuma b'ukekiya kamar matar ka, to ni mijina ba ya buk'atar na yi k'iba haka yake son gani na, sannan da ka ke fatan wayata ta fad'i to in fad'a ma ka ta na fad'uwa wallahi sai ka biya ni, in kuma ba haka ba zansa Ummi ta ma bore har sai an sake ma ka tiyata, ai dai ka gane tiyatar da na ke nufi ko?"
Ta fad'a ta na kashe mi shi ido d'aya, baki ya saki ya na kallo na har na wuce na bar shi, saida na b'acewa ganin shi ya kalli Ummi yace "Kuma ke sai kiyi idan ta saki?"