Sashe 25
Kallon Kitse Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
"Lafiya lau." Ya fad'a ya na saukowa daga k'afafun Usman, fita ya yi daga d'akin Usman bai hana shu saboda ya na so ya yi magana da ita, ya na ganin fitar shi ya kalle ta da kyau lokacin da take shirin zaunawa, riga da siket ne na kanti wanda su ka kama jikin ta sosai, siket d'in ko k'asa bai gama sauka ba, sannan babu d'an kwali a kan ta, sai da ta zauna yace "Haseenah, yanzu ki na ji a jikin ki wannan kayan sun dace ki saka su a yanzu kuma har ki fito da su?"
Da mamaki tace "Ban gane ba? Me wannan kayan su ka yi?"
Murmushi ya yi yace "Ba fa mu kad'ai bane a gidan nan, wannan kayan da ya dace ki saka ne da dare lokacin da mu ka rage daga ni sai ke."
Cike da tsiwa irin ta yan zamani tace "Matsala, wannan ita ce matsalar da ake magana in dai har ka auri me mata, ba ka isa ka sake ka wataya yanda ka ke so ba, yanzu dan Allah me wannan kayan su ka yi? Na ga kai miji na ne, me ye dan na saka wannan kayan a gida na?"
Har kas'an zuciya maganar ta ta tsaya mi shi a rai, amma sai ya kawar da kai kawai ya mik'e yace "Zan fita ni sai anjima."
Binshi kawai ta yi da harara, dan yau ita zuciyar ta fal take da tarin k'unci, wani faranti ta janyo gaban ta ta bud'a kwanukan, sai da taja numfashi saboda k'amshin da ya daki hancin ta, ai kuwa zubawa ta yi sosai ta kuma ci ta k'oshi ta ma manta waya girka, dan har ga Allah abincin ya mata bala'in dad'i, ko dan ta na jin yunwa ne oho.
Khadija ma na gama shiryawa sai da ta yi sallah kafin ta cika cikin ta da kayan marmari da yan dubaru, daga nan kuma bacci ta shiga dan a huta ma rai.
Kiran sallah ne ya tashe su duka gidan, Bilal masallaci ya nufa kafin ya dawo ya shirya zuwa makaranta, Usman da kan shi ya zo ya d'auke shi su ka tafi lokacin Haseenah har ta shiga girkin dare.
*Mummyn Sultan*
*Mamienmu*
*My sweet Hawwer*
*My lovely Hawwer*
*Mummyn Ameer & Khairat*
*Sis Alawiyya*
*Sis Fusseina*
*Momyn Rasil*
_Da duk wanda baiji sunan sa ba, zaiji anan gaba insha Allah._
23/01/2020 à 13:43 - 💋😘💋: 💑💑💑💑💑💑💑💑💑💑
*KALLON KITSE*
_(Ake wa rogo)_
💑💑💑💑💑💑💑💑💑💑
_SAMIRA HAROUNA_
*Littatafan marubuciyar*
*1* _KAUSSAR_
*2* _D'AUKAR FANSA_
*3* _BA SO BANE_
*4* _AUREN HAD'I_
*5* _SANIN MASOYI_
*6* _JIHADI_
*7* _K'ANGIN RAYUWA_
*8* _ITACE K'ADDARARMU_
*9* _KAWU NA NE_
*10* _MAATA_
*11* _KALLON KITSE..._
*SADAUKARWA GA*
_MATAN FARKO_🧕🏼 *(UWAYEN GIDA)*
🇸🇦 *ZAMAN AMANA WRITER'S*
_(Gidan zaman lafiya da amana insha Allah)_🤜🤛
```Fatan alkairi masoya```
_Bismillahir rahamanir rahim_
*15*
Haseenah dai a shirye take da samu zuciyar mijinta ita ma, hakan ya sa yau ma abinci ware mu su na su ta yi ta kai falon ta, sannan ta zuba maganin saboda ta na so yau ya ci na uku kenan, Bilal ta k'walawa kira tun daga madafar, hankalin shi ya tafi kan kallon da ya ke a *mbc action*, Khadija da ta fito daga d'aki cikin doguwar riga ta shadda ne tace "Bilal ba ka ji auntyn ka na kiran ka ne?"
Da sauri ya mik'e ya nufi k'ofar ya na fad'in "Banji ba Mummy." Ganin ya nufi k'ofar falon ta ya sa tace "Ta na madafa ina jin."
Da sauri ya nufi can, ya na zuwa ta mik'o mi shi kular abinci tace "Abincin ku kai da maman ka."
Jiki a sanyaye ya karb'a ya na kallon ta da mamaki, haka ya juyo ya fito ya kawo abincin maman shi na zaune, aje kwanan ya yi gaban ta ya d'ago ya fad'a kusan k'afafun ta yace "Mummy abincin mu ne wai inji aunty."
"Abinci kuma?" Cewar Khadija ta na yamutsa fuska, "Eh." Cewar shima Bilal d'in, gyara zamanta ta yi kamar wata hamshak'iya matar shugaba akan kujerar tace "Ka kaiwa mai gadi shi."
Ba musu ya d'auki kwanon ya fita da shi, ya na zuwa ma har ya samu ya na cin na shi abincin, cike da ladabi ya aje kwanon gaban shi yace "Baba *Garba* ga abincin ka."
Da mamaki ya kalle shi yace "Abinci na kuma d'an Alhaji? Ai gashi nan har na kusan kai shi k'arshe ma, ko dai makuwa ka yi."
Da dariya Bilal yace "A'a Baba, wannan Mummy e tace na kawo ma ka."
Jim ya d'anyi kafin ya janyo kwanon gaban shi ya na fad'in "Allah sarki, Hajia ta d'auka ba a aiko min da shi bane ina ga? To ka ce angode ka ji ko, ai ba'a maida abinci ba, ko almajirai na bawa tun da na koshi ma."
Juyawa Bilal ya yi Garba ya bi shi da "Sai da safe d'an Alhaji." Duk abin da ya faru akan idon Haseenah wacce ke shirin rufe madafar, k'wafa ta yi tare da mirmushi ta rufe kafin ta wuce d'akin ta, sai da ta gama shirinta tsaf cikin riga da wando masu shegen kyau kafin ta zauna zaman jiran shi.
Kamar yanda ya zamar masa jiki haka yau ma, ya na dawowa da matsananciyar yunwa kai tsaye falon Khadija ya nufa, da sallama d'auke a bakin shi, da gudu Bilal ya tare shi ya na fad'in "Sannu da zuwa Abba."
Cike da rangaji ya d'an rumgume shi yace "Sannu yarima, ya ka ke?"
Mik'ewa Khadija ta yi ta d'auko ruwa da kofi lokacin ya zauna in da ta tashi ya cire hular kan shi, durk'usawa ta yi gwiwarta d'aya a k'asa ta fara tsiyaya ma sa ruwan ta na fad'in "Ko ba ka fad'a ba alamun sun nuna a gajiye ka ke, sannan ka na tare da matsananciyar yunwa wacce ke neman jigata min kai, amma yanzu ka fara da ruwa ma su sanyi." Ta fad'a hakane lokacin da ta mik'o masa kofin ruwan.
Da tattausan murmushi a fuskar shi ya karb'a ya kafa a baki, sai da ya shanye duka ruwan kafin ya sauke numfashi mai k'arfi ya mik'a mata ta karb'a, aje wa ta yi gefe ta janyo k'afar shi ta soma cire masa takalman sa k'afa ciki, zaunawa ta yi kusan shi ta na kallon shi, ido lumshe ya ke kallonta yace "Uwar gida na sarautar mata."
Da wani tsadadden murmushi ta amsa da "Labbaika."
Cike da kasala yace "Wanka na ke so na yi, amma kuma yunwa ba za ta barni ba, yanzu ki zab'a min wanda zai fara yi."
Sai da ta d'an saci kallon Bilal da ya ke tsaye gaban telebijin ya na kallo sannan ta kalle shi tace "Ka k'arasa shiga mana wajen amaryarka, ita ce za ta zab'a ma ka, ko ka manta har yanzu kwananta ka ke?"
Wata doguwar hamma ya yi kafin ya kalle ta yace "Wai ni ban tambaye ki ba ma, yaushe ne kwananki zai zo ne?"
"Me ya sa ka tambaya?" Ta fad'a ta na shafa wuyanta, saida ya rufe ido yace "Ina so na san ranar da zan dawo hannunki ne kawai."
Shiru ta yi ba tace komai ba shi kuma ya mik'e yace "Zan shiga ciki na yi wanka, amma ki tabbatar kun shigo akan lokaci dan mu ci abinci."
Da kallo kawai ta bishi har ya shige ciki, takalman shi ta d'auka ta shiga da su d'akin ta, ya na shiga can ma wata tarairayar ya samu wajen Haseenah har sai da ya yi wanka ya canza kaya kafin su ka zo kan teburi, kallon ta ya yi yace "Ki saka hijab sai ki kirasu su zo mu ci abinci."
D'an jim ta yi kafin ta zagayo kujerar shi ta zauna akan k'afar shi ta na shafa d'an gajeran gemunshi tace "Hubbi na, ban san ko tunanin da na yi zai gamsar da kai ba, amma ina fatan ba zai zama kuskure a gare ka ba, ka ga ni amarya ce, kuma kowace amarya ta na so taga ta more amarcinta babu takura da matsi, wallahi har zuciya ta ba na jin aunty Khadija da Bilal a matsayin takura a gareni, sai dai ina so na sati d'ayan nan mu dinga cin abinci tare da kai, amma kuma na san hakan ba zai yiwu ba saboda ka saba cin abinci da iyalinka, amma gaskiya idan ba ka min wannan alfarmar ba zai sa na ji kamar ba ka d'auke ni a matsayin..."
Da sauri ya rufe mata baki yace "Wa ya fad'a mi ki ke ba iyali na bace? Ai tun ranar da aka d'aura mana aure mu ka zama iyali ni da ke, dan haka kar ki sake fad'in haka, yanzu ba dai maganar cin abinci tare bane?"
Kai ta d'aga cike da shagwab'a alamar eh, d'orawa ya yi da "Angama da wannan buk'atar, sai kuma wata idan akwai, zan wa Ummyn Bilal magana za ta fahimta, sai dai yanzu ki zuba mu su na su abincin sai ki kai mu su, ko ya ki ka gani? Tun da ai ba sa zauna da yunwa ba."
Shiru ta yi kamar za ta fashe da kuka ta kalle shi tace "Ban san me ya sa ba, amma dai da ido na naga Bilal ya kaiwa mai gadi abincin da na ba shi su ci, watak'ila bai mu su dad'i bane."
Shiru ya d'anyi kafin ya kalle ta yace "Shikenan, zuba mana abincin."
Zubwa ta yi amma kuma sam ta k'i yarda ta ci wai ita ta k'oshi, ba dan ran shi na so ba ya ci sai dan kar ta ji ba dad'i, amma har ga Allah abincin bai masa ba, domin kuwa yau ma dai shinkafa ce da jar miya, shi kuma bai fiya cin shinkafa ba da dare, sannan kuma ga ya ji da abincin ma ya yi, da k'yar ya d'an tuttura ba tare da ya nuna mata ba, su na kammalawa yace su je falon Khadija, cikin shagwab'a tace "Wanka fa zan shiga yanzu na yi shirin bacci."
Murmushi ya mata yace "To a shirya da kyau kafin na dawo."
Cikin kwarkwasa tace "To amma fa kar ka jima sosai, wallahi idan ka jima ni bacci na zanyi."
Da mamaki tace "Ban gane ba? Me wannan kayan su ka yi?"
Murmushi ya yi yace "Ba fa mu kad'ai bane a gidan nan, wannan kayan da ya dace ki saka ne da dare lokacin da mu ka rage daga ni sai ke."
Cike da tsiwa irin ta yan zamani tace "Matsala, wannan ita ce matsalar da ake magana in dai har ka auri me mata, ba ka isa ka sake ka wataya yanda ka ke so ba, yanzu dan Allah me wannan kayan su ka yi? Na ga kai miji na ne, me ye dan na saka wannan kayan a gida na?"
Har kas'an zuciya maganar ta ta tsaya mi shi a rai, amma sai ya kawar da kai kawai ya mik'e yace "Zan fita ni sai anjima."
Binshi kawai ta yi da harara, dan yau ita zuciyar ta fal take da tarin k'unci, wani faranti ta janyo gaban ta ta bud'a kwanukan, sai da taja numfashi saboda k'amshin da ya daki hancin ta, ai kuwa zubawa ta yi sosai ta kuma ci ta k'oshi ta ma manta waya girka, dan har ga Allah abincin ya mata bala'in dad'i, ko dan ta na jin yunwa ne oho.
Khadija ma na gama shiryawa sai da ta yi sallah kafin ta cika cikin ta da kayan marmari da yan dubaru, daga nan kuma bacci ta shiga dan a huta ma rai.
Kiran sallah ne ya tashe su duka gidan, Bilal masallaci ya nufa kafin ya dawo ya shirya zuwa makaranta, Usman da kan shi ya zo ya d'auke shi su ka tafi lokacin Haseenah har ta shiga girkin dare.
*Mummyn Sultan*
*Mamienmu*
*My sweet Hawwer*
*My lovely Hawwer*
*Mummyn Ameer & Khairat*
*Sis Alawiyya*
*Sis Fusseina*
*Momyn Rasil*
_Da duk wanda baiji sunan sa ba, zaiji anan gaba insha Allah._
23/01/2020 à 13:43 - 💋😘💋: 💑💑💑💑💑💑💑💑💑💑
*KALLON KITSE*
_(Ake wa rogo)_
💑💑💑💑💑💑💑💑💑💑
_SAMIRA HAROUNA_
*Littatafan marubuciyar*
*1* _KAUSSAR_
*2* _D'AUKAR FANSA_
*3* _BA SO BANE_
*4* _AUREN HAD'I_
*5* _SANIN MASOYI_
*6* _JIHADI_
*7* _K'ANGIN RAYUWA_
*8* _ITACE K'ADDARARMU_
*9* _KAWU NA NE_
*10* _MAATA_
*11* _KALLON KITSE..._
*SADAUKARWA GA*
_MATAN FARKO_🧕🏼 *(UWAYEN GIDA)*
🇸🇦 *ZAMAN AMANA WRITER'S*
_(Gidan zaman lafiya da amana insha Allah)_🤜🤛
```Fatan alkairi masoya```
_Bismillahir rahamanir rahim_
*15*
Haseenah dai a shirye take da samu zuciyar mijinta ita ma, hakan ya sa yau ma abinci ware mu su na su ta yi ta kai falon ta, sannan ta zuba maganin saboda ta na so yau ya ci na uku kenan, Bilal ta k'walawa kira tun daga madafar, hankalin shi ya tafi kan kallon da ya ke a *mbc action*, Khadija da ta fito daga d'aki cikin doguwar riga ta shadda ne tace "Bilal ba ka ji auntyn ka na kiran ka ne?"
Da sauri ya mik'e ya nufi k'ofar ya na fad'in "Banji ba Mummy." Ganin ya nufi k'ofar falon ta ya sa tace "Ta na madafa ina jin."
Da sauri ya nufi can, ya na zuwa ta mik'o mi shi kular abinci tace "Abincin ku kai da maman ka."
Jiki a sanyaye ya karb'a ya na kallon ta da mamaki, haka ya juyo ya fito ya kawo abincin maman shi na zaune, aje kwanan ya yi gaban ta ya d'ago ya fad'a kusan k'afafun ta yace "Mummy abincin mu ne wai inji aunty."
"Abinci kuma?" Cewar Khadija ta na yamutsa fuska, "Eh." Cewar shima Bilal d'in, gyara zamanta ta yi kamar wata hamshak'iya matar shugaba akan kujerar tace "Ka kaiwa mai gadi shi."
Ba musu ya d'auki kwanon ya fita da shi, ya na zuwa ma har ya samu ya na cin na shi abincin, cike da ladabi ya aje kwanon gaban shi yace "Baba *Garba* ga abincin ka."
Da mamaki ya kalle shi yace "Abinci na kuma d'an Alhaji? Ai gashi nan har na kusan kai shi k'arshe ma, ko dai makuwa ka yi."
Da dariya Bilal yace "A'a Baba, wannan Mummy e tace na kawo ma ka."
Jim ya d'anyi kafin ya janyo kwanon gaban shi ya na fad'in "Allah sarki, Hajia ta d'auka ba a aiko min da shi bane ina ga? To ka ce angode ka ji ko, ai ba'a maida abinci ba, ko almajirai na bawa tun da na koshi ma."
Juyawa Bilal ya yi Garba ya bi shi da "Sai da safe d'an Alhaji." Duk abin da ya faru akan idon Haseenah wacce ke shirin rufe madafar, k'wafa ta yi tare da mirmushi ta rufe kafin ta wuce d'akin ta, sai da ta gama shirinta tsaf cikin riga da wando masu shegen kyau kafin ta zauna zaman jiran shi.
Kamar yanda ya zamar masa jiki haka yau ma, ya na dawowa da matsananciyar yunwa kai tsaye falon Khadija ya nufa, da sallama d'auke a bakin shi, da gudu Bilal ya tare shi ya na fad'in "Sannu da zuwa Abba."
Cike da rangaji ya d'an rumgume shi yace "Sannu yarima, ya ka ke?"
Mik'ewa Khadija ta yi ta d'auko ruwa da kofi lokacin ya zauna in da ta tashi ya cire hular kan shi, durk'usawa ta yi gwiwarta d'aya a k'asa ta fara tsiyaya ma sa ruwan ta na fad'in "Ko ba ka fad'a ba alamun sun nuna a gajiye ka ke, sannan ka na tare da matsananciyar yunwa wacce ke neman jigata min kai, amma yanzu ka fara da ruwa ma su sanyi." Ta fad'a hakane lokacin da ta mik'o masa kofin ruwan.
Da tattausan murmushi a fuskar shi ya karb'a ya kafa a baki, sai da ya shanye duka ruwan kafin ya sauke numfashi mai k'arfi ya mik'a mata ta karb'a, aje wa ta yi gefe ta janyo k'afar shi ta soma cire masa takalman sa k'afa ciki, zaunawa ta yi kusan shi ta na kallon shi, ido lumshe ya ke kallonta yace "Uwar gida na sarautar mata."
Da wani tsadadden murmushi ta amsa da "Labbaika."
Cike da kasala yace "Wanka na ke so na yi, amma kuma yunwa ba za ta barni ba, yanzu ki zab'a min wanda zai fara yi."
Sai da ta d'an saci kallon Bilal da ya ke tsaye gaban telebijin ya na kallo sannan ta kalle shi tace "Ka k'arasa shiga mana wajen amaryarka, ita ce za ta zab'a ma ka, ko ka manta har yanzu kwananta ka ke?"
Wata doguwar hamma ya yi kafin ya kalle ta yace "Wai ni ban tambaye ki ba ma, yaushe ne kwananki zai zo ne?"
"Me ya sa ka tambaya?" Ta fad'a ta na shafa wuyanta, saida ya rufe ido yace "Ina so na san ranar da zan dawo hannunki ne kawai."
Shiru ta yi ba tace komai ba shi kuma ya mik'e yace "Zan shiga ciki na yi wanka, amma ki tabbatar kun shigo akan lokaci dan mu ci abinci."
Da kallo kawai ta bishi har ya shige ciki, takalman shi ta d'auka ta shiga da su d'akin ta, ya na shiga can ma wata tarairayar ya samu wajen Haseenah har sai da ya yi wanka ya canza kaya kafin su ka zo kan teburi, kallon ta ya yi yace "Ki saka hijab sai ki kirasu su zo mu ci abinci."
D'an jim ta yi kafin ta zagayo kujerar shi ta zauna akan k'afar shi ta na shafa d'an gajeran gemunshi tace "Hubbi na, ban san ko tunanin da na yi zai gamsar da kai ba, amma ina fatan ba zai zama kuskure a gare ka ba, ka ga ni amarya ce, kuma kowace amarya ta na so taga ta more amarcinta babu takura da matsi, wallahi har zuciya ta ba na jin aunty Khadija da Bilal a matsayin takura a gareni, sai dai ina so na sati d'ayan nan mu dinga cin abinci tare da kai, amma kuma na san hakan ba zai yiwu ba saboda ka saba cin abinci da iyalinka, amma gaskiya idan ba ka min wannan alfarmar ba zai sa na ji kamar ba ka d'auke ni a matsayin..."
Da sauri ya rufe mata baki yace "Wa ya fad'a mi ki ke ba iyali na bace? Ai tun ranar da aka d'aura mana aure mu ka zama iyali ni da ke, dan haka kar ki sake fad'in haka, yanzu ba dai maganar cin abinci tare bane?"
Kai ta d'aga cike da shagwab'a alamar eh, d'orawa ya yi da "Angama da wannan buk'atar, sai kuma wata idan akwai, zan wa Ummyn Bilal magana za ta fahimta, sai dai yanzu ki zuba mu su na su abincin sai ki kai mu su, ko ya ki ka gani? Tun da ai ba sa zauna da yunwa ba."
Shiru ta yi kamar za ta fashe da kuka ta kalle shi tace "Ban san me ya sa ba, amma dai da ido na naga Bilal ya kaiwa mai gadi abincin da na ba shi su ci, watak'ila bai mu su dad'i bane."
Shiru ya d'anyi kafin ya kalle ta yace "Shikenan, zuba mana abincin."
Zubwa ta yi amma kuma sam ta k'i yarda ta ci wai ita ta k'oshi, ba dan ran shi na so ba ya ci sai dan kar ta ji ba dad'i, amma har ga Allah abincin bai masa ba, domin kuwa yau ma dai shinkafa ce da jar miya, shi kuma bai fiya cin shinkafa ba da dare, sannan kuma ga ya ji da abincin ma ya yi, da k'yar ya d'an tuttura ba tare da ya nuna mata ba, su na kammalawa yace su je falon Khadija, cikin shagwab'a tace "Wanka fa zan shiga yanzu na yi shirin bacci."
Murmushi ya mata yace "To a shirya da kyau kafin na dawo."
Cikin kwarkwasa tace "To amma fa kar ka jima sosai, wallahi idan ka jima ni bacci na zanyi."