← Book details Kallon Kitse Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 36 OF 86

Sashe 36

Kallon Kitse Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Wani murmushi ya yi kamar mai ciwon baki kafin ya ja hannun ta zuwa ban d'akin, sosai Khadija ta fahimci akwai sabon al'amari a tare da shi, dan har ta gama mi shi wankan nan ba su yi wata magana ba, kamar yanda sai dai ya mata murmushin yak'e kawai, haka ta gama mi shi shiri su ka fito cin abinci, sun zauna kenan Haseenah ta fito ita ma, tunda ya kafe ta da ido bai d'auke ba har ta zauna, murmushi kawai ya ke sakar mata har Khadija ta gama zuba abinci.

Haka aka ci abinci babu wani nishad'i bare jin dad'i, su na gamawa ya nufi wajen Haseenah dan yi mata saida safe, ita ma Khadija shiga ta yi dan ta yi shirin bacci, amma har ta gama ta dawo bai dawo d'akin shi ba, abun mamaki shine har ta d'auki minti ashirin kwance kafin ya shigo, ya na can Haseenah na zuba shagwab'a wai zai tafi ya bar ta, ya na shigowa kashe wuta ya yi ya kwanta, zunbur Khadija ta mik'e da tafarfasar zuciya ta na kallon k'eyar shi tace "Me zan gani haka Abban Bilal?"

Juyowa ya yi a kasalance yace "Me fa?"

"Baya fa ka juya min, me na ma ka haka da zafi? Akan abin da ya faru ne? Dan Allah ka yi hak'uri in dai abin da ya faru ne zai sa ka juya min baya."

Yanda ta yi maganar cikin muryar kuka ya sa k'wak'walwar shi hasko mi shi wacece ita, tashi ya yi zaune ya rumgumo ta jikin shi yace "Shikenan to ya wuce, ki yi hak'uri kar ki min kuka, ba na yi bane da gangan, kawai ba na jin dad'i ne."

Da kuzari ta kwantar da shi akan gadon tace "Kwanta to na ma ka tausa."

Cire mi shi rigar shi ta yi a hankali ta fara shafar bayan shi, yanda ta gama kashe mi shi jiki ya sa ya juyo ya sauke idon shi akan ta, da k'arfi ya fizgo ta ta fad'a jikin shi ya had'e labb'an su...saida safe.

Kwana biyun da ya yi a wajen Khadija ya zo da al'ajabi, dan sosai ta ke gani bak'in al'amura daga gare shi, shi kan shi ya na jin wannan canji a tare da shi, amma tasirin wani abu ne ya ke mi shi togaciya ga abin da ya ke ji, asabar da yamma Haseenah ta karb'i girki, a daren ranar da ta yi anfani da maganin nan a marar ta ko da Usman ya kusanceta ya ji duk fad'in duniya babu maccen da ya ke son kasancewa da ita sama da ita, ba ma wannan bane yafi d'aga hankali kamar yanda ya ke jin kamar ita ce ma macen da ta fara gamsar da shi a shinfid'a, gaba d'aya ya nemi tasirin wata mace ya rasa, tun a daren ya fara ririta Haseenah kamar yau ya fara ganin ta ko sanin ta.

Washe gari ma bayan ya fita ta sa aka samo mata fura ta dama, sosai ta had'a furar kafin ta zuba maganin na k'arshe a ciki, da kan shi ya zo cin abinci bayan ya kammala ta kawo mi shi furar cikin kofin tangaran mai kyau, kallon ta ya yi yace "Fita na ke so na yi fa, idan kuma na sha furar nan jiki na zai mutu na yu bacci."

Cike da shagwab'a tace "Uhum uhum, wallahi ni dai ban yarda ba sai kasha, saboda kai fa na had'a."

Take ya ji sak'on ya kai zuciyar ya ji ai tafi k'arfin ma ya yi gardama da ita, amsa ya yi tare da kurb'ar furar har ya shanye, mik'ewa ya yi ya shiga wanka ya na fitowa ko riga bai saka ba ya kwanta sai bacci.

Da da magriba ta tashe shi ya yi alwala ya tafi masallaci, bai shigo gidan ba har ya yi sallah isha'i, ya na idawa ya d'auko hanyar dawowa a lokacin kuma Naseer ya dawo da Bilal gida, sun jima a k'ofar gidan su na kafin Naseer ya tafi shi ya shigo ciki, kai tsaye tare da Bilal suka shigo b'angaren Khadija, tunda ya hangi Khadija akan kujera ya ji wani bala'i ya taso mi shi tare da sarawar kan shi, da gudu Bilal ya k'araso ya rumgume ta, rumgume shi ta yi cike da k'aunar d'an na ta tace "Yarima kai da wa?"

D'agowa ya yi ya na cire jakar bayan shi ya na fad'in "Tonton Naseer ne."

Gira ta d'aga sama tace "Uhum! Wato dai kun zama abokai ko?"

Dariya ya yi yace "Mummy bara kiga abin da ya siyo min, kuma Hajia ma ta siyo min wani abu."

Murmushi ta yi ta mayar da hankalin ta kan Usman tace "Sannu da shigowa Babban mutum."

Wani irin amo ya ji muryar ta na mi shi cikin kunne marar dad'in ji da sauti, juyawa kawai ya yi ya fita ta k'ofar da ya shigo ya nufi na shi falon, ya na fita ya ji wani sak'at a zuciyar shi saboda ba ya ganin Khadija, Khadija kam abun ya bata mamaki sai dai hayaniyar Bilal da kayan da ya ke fito da su ya na nuna mata ya sa ba ta wani saka a kai ba, shi kam ya jima zaune sai ya d'auko tunani kamar akan bak'on al'amarin nan, amma kuma sai ya ji k'walwar shi ta yi wani jugum kamar babu komai a ciki, hakan ya sa ya yi tsaki sama da dubu kafin Haseenah ta shigo ta same shi.

Dare ya yi dare Khadija ta kasa bacci ta na tsammanin jiran shigowar Usman amma babu shi babu labarin shi, tun Bilal na mata hira na abubuwan da suka faru a gida har bacci ya d'auke shi, haka ita ma baccin ya d'auke ta daga wurin ba ta ankara ba, haka har akayi sallaha asuba gari ya waye bai lek'o ba, shi kuma ya na can ko ya ji a ran shi ya zo sai kuma ran shi ya b'ace haka kawai, har Haseenah ta masa magana ya zo ya mu su sallama ya share kawai, dad'i ta ji a zuciyar ta amma a zahiri ta nuna bai dace ba.

Washe gari da safe haka kawai Usman ya ji ba ya son fita ya yi nesa da Haseenah, ko k'ofar gida bai fita ba in ba sallah ya je yi ba, bayan sallah la'asar Aziza ta zo gidan tare da rakiyar k'awar ta, kai tsaye b'angare Khadija suka fara nufa saboda nan kad'ai k'ofar a bud'e, Khadija da a lokacin abun duniya ya isheta na rashin ganin Usman bayan kuma ta na da tabbacin ya na gidan, amsa sallamar ta yi a dak'ile tare da kallon su a raunane, har su ka zauna babu wanda ya sake magana, kallon Uwani ta yi dake gefe tace "Uwani kawo mu su abun sha ko."

To." Ta fad'a ta na mik'ewa, k'ala Khadija ba ta sake cewa komai ba har Uwani ta dawo da abun sha, sai lokacin Aziza tace "Aunty Khadija wai ina Bilal? Ban gan shi ba."

Kallon ta Khadija ta yi cike da rainin wayo saboda tunawa da ta yi ranar da taji Aziza da bakin ta tana kiran d'an ta shege, a kaikaice ta sake kallon ta tace "...

*Allah ka bawa dukanin musulmi lafiya.*
06/02/2020 à 22:23 - 💋😘💋: 💑💑💑💑💑💑💑💑💑💑
*KALLON KITSE*
_(Ake wa rogo)_
💑💑💑💑💑💑💑💑💑💑

_SAMIRA HAROUNA_

*Littatafan marubuciyar*

*1* _KAUSSAR_
*2* _D'AUKAR FANSA_
*3* _BA SO BANE_
*4* _AUREN HAD'I_
*5* _SANIN MASOYI_
*6* _JIHADI_
*7* _K'ANGIN RAYUWA_
*8* _ITACE K'ADDARARMU_
*9* _KAWU NA NE_
*10* _MAATA_
*11* _KALLON KITSE..._

*SADAUKARWA GA*

_MATAN FARKO_🧕🏼 *(UWAYEN GIDA)*

🇸🇦 *ZAMAN AMANA WRITER'S*
_(Gidan zaman lafiya da amana insha Allah)_🤜🤛

```Fatan alkairi masoya```

*🇸🇦ZAMAN AMANA WRITER'S*
(GIDAN ZAMAN LAFIYA DA AMANA INSHA ALLAH)🤜🤛

*SANARWA! SANARWA!! SANARWA!!!*

*INA JIGA JIGAN MASOYAN 🇸🇦ZAMAN AMANA WRITER'S WAD'ANDA BASU DA TAMKA A WAJENMU????? DUK WANDA YAKE TARE DAMU A CIKIN GROUPS D'INMU TO MUN TABBATAR K'AUNARMU CE TASA KUKA KASANCE TARE DAMU, MUNA YABAWA KUMA HAR ABADA BAMU DA KAMARKU WALLAHI,👍 DUK DA HAKA DAI GA LOKACI YAZO, KUMA DAMA TA SAMU NA TABBATAR MANA DA KUMA NUNA MANA HAK'IK'ANIN K'AUNAR DA KUKE MANA,👇*

Kunsan cewa k'ungiyarmu *🇸🇦ZAMAN AMANA WRITER'S* suna cikin gagarumin gasa na samun award Wanda *women24 TV WhatsApp group* suka shirya kuma zasu gudanar?

A wannan gasar ne za'a samu k'ungiyar da tafi kowacce k'ungiya yawan fans da Kuma bin k'a'idar rubutu

Dan ki samu damar zabar k'ungiyarmu *🇸🇦ZAMAN AMANA WRITER'S ASSOCIATION* zaki iya tuntub'ar wannan lambar 09030159301 Dan su saki a *WOMEN24 TV WHATSAPP GROUP* anan ne za'ayi zab'en k'ungiyar da tafi kowacce k'ungiya yawan masoya

*Women24 Tv*
Ba zabe kad'ai zakiyi ba

Zaki k'aru da abubuwa da yawa kamar haka

*Yanda ake girke girke*
*yanda zaki gyara jikinki*
*yanda zakiyi makeup*
*yanda zaki daura Dan kwali*

Kuma suna shirye shiryen nan na *arewa24 tv* kamar su

*TARKON KAUNA*
*DADIN KOWA*
*KWANA CHASA'IN*
*JAMAI RAJA*
*SAPNE SUHANE*
*GIDAN BADAMASI*
*RUDIN ZUCIYA*
*BAGHYA LAKSHMI*
*AKUSHI DA RUFI*
*AUDIO NOVEL*
*HAUSA NOVELS*

Kada ki manta da ranar zabe inkin shiga group d'in ki zaba *🇸🇦ZAMAN AMANA WRITER'S* tanan ne zaki iya nuna mana irin sonda kuke ma k'ungiyarmu da littattafammu, kuma a ko'ina ko a kowace k'asa masoyanmu suke sunada damar zab'enmu ba sai 'yan nigeria kad'ai ba.

Allah yabar zumunci🤝😍🥰💋

_Bismillahir rahamanir rahim_

*20*

"Bilal ya na nan, kinyi kewar shi ne har haka?"

Wata 'yar dariya ta yi tace "Ban gan shi bane ba ai."

"Uhum." Cewar Khadija can k'asan mak'oshi, jim kad'an Khadija ta kalle su tace "Ku wuce ciki mana ai suna nan, dan nasan wajen su ku ka zo."

Cike da kunya Aziza ta d'anyi jim kamar ba za ta tashi ba, a hankali su ka tashi tace "Bara mu gaishe ta sai mu wuce."
Chapter 36 · 0% Book details