← Book details Kallon Kitse Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 39 OF 86

Sashe 39

Kallon Kitse Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Mamaki ne ya bayyana a fuskar ta tace "Ka kai ta? Amma Abban Bilal kasan tsawon lokacin da na d'auka a d'akin nan ina jiran ta?" Ta k'arashe da nuni da k'ofar falon ta.

Tab'e baki ya yi yace "To sai me? Laifi na yi da na kai ta? Kinga bana son masifa, idan kema ki na so idan kon shirya ki yi magana sai na kai ki da kai na, shikenan?"

Saida ya harare ta sama da k'asa ya ja k'aramin tsaki ya wuce, jiki a sanyaye ta juyo ta dawo, ta na zuwa ta samu Haseenah ta kawo abincin rana bayan sallah la'asar, ko kallon abincin ba ta yi ba tace ma Uwani "Ki ci abincin idan ki na buk'ata."

Juyawa ta sake yi ta nufi madafa, aiki ta fara ba kama hannun yaro, saida Uwani ta gama cin abincin sai dai ba wani mai yawa ba, dan duk yunwar da take ji kasa cin abincin ta yi saboda ba za ta iya cewa ga abin da ya yi yawa ba, sai dai tabbas akwai abin da ya yi yawa a cikin girkin, nan suka shiga aikin su ita da Khadija kafin magriba su ka kammala, kula ya yi daidai da dawowar Bilal daga islamiyya, saida ta aje komai in da ya dace kafin ta shiga wanka ana kiran sallah, Bilal ma ko da ya dawo daga masallaci ta taimaka ma sa ya shirya dan tare za su tafi, Uwani ma saida ta sallame ta kafin suka fita tare ta aje gidan su suka wuce.

Hira sosai ta b'arke tsakanin malam da Bilal, dan jiki ya yi sauk'i sosai, anso sallamar shi amma likitocin sunce su na son jinin shi ya daidaita ne, dan da aka kawo shi jinin shi ya hau kad'an, misalin takwas da rabi suna shirin tafiya sai ga Usman tare da Haseenah, sam ba ta nuna komai ba haka su ka musu sallama su ka tafiyar su.

Sun koma gida, kuma tun Khadija na zuba idon dawowar Usman har ta gaji, shirin da tayi dan tarbar shi ya wartsake bacci na surarta, su kam suna can sun wuce wajen cin abinci daga nan su ka wuce 'yar kasuwa ya mata siyayya mai yawon gaske, wai ta cancanci fiye da haka ma a cewar shi, haka suka je ya siyo mata ice crime da sauran kayan k'walam da mak'ulashe, *11:56* na dare suka d'auki hanyar komawa gida.

Khadija na jin k'arar bud'a gida ta fito farfajiyar, har saida ya wa mitar mazauni ya fito, da kan shi ya bud'ewa Haseenah ta fito kafin ya d'auko ledojin a hannun shi, tuni ta ankare da Khadija hakan ya sa tace "Beby ka kawo na taya ka d'auka mana."

Kallon ta ya yi yace "Ke lafiyar ki k'alau? Wannan kayan ne zan baki ki d'auka salon ki ja min salalan tsiya, ba dani ba wallahi, to ma miye anfani na idan ban hidimta mi ki ba."

Juyowar da zaiyi da nufin kallon gaban shi ya sauke ido akan Khadija da ta rik'e k'ugu da hannu d'aya, ajiyar zuciya ta sauke shi kam ko a jikin shi, dan har ga Allah ba ya jin wai ya yi ba daidai ba, sai ma d'aure fuska da ya yi yace "Malama ya dai? Har yanzu ba ki kwanta ba kamar ki na jiran mu."

Ganin Haseenah ta nufi b'angaren ta ko a kwalar rigar ta ya sa shima ya bi bayan ta, ita ma wucewa ta yi ta je falon shi ta zauna kan d'aya daga cikin kujerun teburi ta na jiran shi, ai kam bai jima sosai ba ya shigo falon da alama wanka zai yi, kamar bai ganta ba haka ya wuce uwar d'akin shi ya fara cire kaya, ita ma bayan shi ta bi hannu ta kai da nufin kama mi shi ya yi saurin ja baya sosai yace "Nagode."

Ko wando bai cire ba ya wuce ban d'akin, ta na nan zaune har ya fito ya shirya duk ta na kallon shi ta rasa ma abinyi, juyowa ya yi zai fita yace "Idan kin gama kallon nawa na fita ni, zanyi kallo daga yanzu zuwa lokacin da zan kwanta ba na son takura."

Da sauri har da gudu ta k'arasa gaban shi ta rik'o hannun shi, za ta yi magana sai kuma ta kasa saboda yanda ya raba hannun ta da na shi, shi kam ta na rik'e hannun shi ya ji kamar ta zuba mi shi ruwan zafi a jiki, ba ta yi magana ba ya fice ya bar ta, falon ta biyo shi cikin rawar murya tace "A...a..abincin..ka..."

Da k'arfi ya mik'e daga zaman da ya yi kamar zai had'e ta cikin d'aga murya iya k'arfin shi yace "Ba na ci, nagode, dallah ki fitar min daga d'aki, zuciya ta tafasa take idan ina kallon ki, sam muryar ki babu dad'in ji kuma duk kin bi kin takura ni da zance kamar wata sabuwar rediyo (redio)."

Wani dogon tsaki ya ja yace "Haba, ni na rasa gane wannan jarabar." Kai tsaye d'akin Haseenah ya nufa ya na ci gaba da mita, ragwaf Khadija ta fad'a kan kujera ta fashe da kuka, har za ta d'aga sauti sai kuma ta kame bakin ta ta tashi ta koma na ta d'akin, har ta dasa wani sabon kukan sai kuma ta tuna maganar lahaifiyar ta da take fad'a mu su "Duk abin da ya yi zafi laganin shi Allah, ku rik'e Allah a cikin lamarin ku, ba shakka zai taimake ku dan ya na tare da ku."

Wannan maganar ce ta sa ta d'auro alwala ta shinfid'a sallaya ta d'auki Qur'ani ta fara karatu, saida ta raba dare kafin ta kabbara sallah a kowace sujuda ta na kaiwa ubangiji koken ta.

Usman kuma na shiga ko da ya sauke idon shi akan amaryar shi sai wani irin farin ciki da shauk'i ya rufe shi, sam ya manta da komai a kan shi haka ya so hayake ma haseenah, ita kam sam tsoro ya kamata dan haka ta k'i amince mi shi, da k'yar da sud'in goshi ta lallab'a shi ya koma d'akin shi, amma a ganin shi da ya ga Khadija gwara ya zauna shi kad'ai, haka ya sha baccin shi har kiran sallah asuba.

*Allah ka azurta mu da abokan zama na gari*
08/02/2020 à 23:04 - 💋😘💋: 💑💑💑💑💑💑💑💑💑💑
*KALLON KITSE*
_(Ake wa rogo)_
💑💑💑💑💑💑💑💑💑💑

_SAMIRA HAROUNA_

*Litattafan marubuciyar*

*1* _KAUSSAR_
*2* _D'AUKAR FANSA_
*3* _BA SO BANE_
*4* _AUREN HAD'I_
*5* _SANIN MASOYI_
*6* _JIHADI_
*7* _K'ANGIN RAYUWA_
*8* _ITACE K'ADDARARMU_
*9* _KAWU NA NE_
*10* _MAATA_
*11* _KALLON KITSE..._

*SADAUKARWA GA*

_MATAN FARKO_ 🧕🏼 *(UWAYEN GIDA)*

🇸🇦 *ZAMAN AMANA WRITER'S*
_(Gidan zaman lafiya da amana insha Allah)_🤜🤛

```Fatan alkairi masoya```

1. Mom teema Hakima
2. Yar baba ( Fatima Zara )
3. Momyn Dady
4. Chappa *Auntyn Khadi*
5. BILKISU Z. YA'U
6. Raheenah m Abbacar
7. Aishan Umma
8. Maman Labyb
9. Aunty Hawwer
10. Hawwer Jidda
11. Alawiyya
12. Amina
13. Yagana Mousa
14.Rukayya
15. Maman souhailat
16. Ummu sultan
17. Ouma saadou
18. Rahilat
19. Azima *momyn Imane*
20. Mme Jamil
21. Ummi 1
22. Ummi 2
23. Nazeefa
24. Jamila
25. Maijiddah
26. Sadia magaji
27. Phartee shehu
28. Ummu halima
29. Halima Muhammad
30. Maman Tasleem
31. Jawahir Gombe
32. Fareedah Boube
33. Lubabatu Shehu shayi
34. Zeinab mai kano
35. Maman Ahmad
36. Firdaussi Shehu
37. Binta Umar
38. Preettyy Aeeshartyy
39. Rukayya Usman
40. Maryam Abdul Mumin
41. Salma Ibrahim
42. Hussy luv
43. Hafsat A.A
44. Jamila Musa
45. Choukriyya
46. Khadija Isa
47. Matar manya
48. Mamar Soja
49. Momyn Rasil
50. Meeynert
51. Mandiya😁
52. Habiba Bala

_Duk wanda ya ga sunan shi to ya na zuciyar *Samira* ne, sai dai wanda na manta kawai a matsayi na na yar adam ajiza._

_Bismillahir rahamanir rahim_

*21*

Abincin jiya ta fara d'aukewa kafin ta d'ora na karin kummalo, ba ta wani d'auki lokaci ba ta k'arasa shirya komai, saida ta shirya ta tashi Bilal shima ta taimaka ma sa ya shirya da sauri, karin kuma ta had'a mi shi ya ci ya k'oshi kafin ya nufi d'akin mahaifin shi, abun mamaki shine a al'adar Usman ba ya komawa bacci bayan sallah asuba, amma sai gashi yanzu rauni da sauyin da aka samu ya sa kasala ta rufe shi ya gagara abin da ya dace, haka ya koma ya kwanta baccin shi, doguwar riga kawai ya zura suka tafi ya kai shi, ko da ya dawo ya samu Khadija zaune a falon shi, da sauri ta mik'e ta kalle shi tace "Ina kwana."

"Lafiya." Ya fad'a ya na shirin wucewa, da ido ta bishi har ya wuce d'akin amarsu, tashin ta ya yi a bacci suka shiga wanka tare su ka fito, sun jima kafin su gama shiryawa su fito tare, Khadija na zaune in da ya barta tun farko, zaune su ka yi akan kujera ita kam sai ta kafe shi da ido da tsananin mamaki, jinkirin ne ya sa yasa Usman kallon ta ganin ba ta da niyyar zuba abincin ya sa yace "Abincin na ki ko na siyarwa ne? Sai ki mana baya ni ai."

Murmushi ta masa ta mik'e ta fara zubawa, shi ta fara zuba ma ta aje a gaban shi sannan ta zubawa Haseenah da ke ta kakkaryewa ta aje mata, ta na shirin zuba ma kan ta Haseenah ta ture faranti gefe ta mik'e tsaye ta kalle shi tace "Baby, zan koma d'aki na na kwanta, ba na jin sha'awar cin abincin nan kwata-kwata."

Kamar mazari haka ya fara tambayar ta "To me za ki ci idan ba ki ci abinci ba? Fad'a min me ki ke so ki ci to? Ai ba kya zauna da yunwa ba ki cutar da kan ki."

Cike da yatsina fuska tace "Umm, da ace zan samu indomie da na ji dad'i."

Kallon Khadija ya yi ya kula kallon ta yace "Abu mai sauk'i, bara yanzu a dafa mi ki, kije ki kwanta to." Kallon Khadija ya yi da ke tsaye yace "Am dan Allah na ce ba, ki taimaka mata ki d'ora mata, ina ganin kamar ba ta da lafiya ne fa, dan gaba d'aya yanayin ta ya canza."
Chapter 39 · 0% Book details