← Book details Kallon Kitse Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 46 OF 86

Sashe 46

Kallon Kitse Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

*1* _KAUSSAR_
*2* _D'AUKAR FANSA_
*3* _BA SO BANE_
*4* _AUREN HAD'I_
*5* _SANIN MASOYI_
*6* _JIHADI_
*7* _K'ANGIN RAYUWA_
*8* _ITACE K'ADDARARMU_
*9* _KAWU NA NE_
*10* _MAATA_
*11* _KALLON KITSE..._

*SADAUKARWA GA*

_MATAN FARKO_ 🧕🏼 *(UWAYEN GIDA)*

🇸🇦 *ZAMAN AMANA WRITER'S*
_(Gidan zaman lafiya da amana insha Allah)_🤜🤛

```Fatan alkairi masoya```

_Bismillahir rahamanir rahim_

*24*

Tunda Haseenah ta ga Hajia Turai gaban ta ya fad'i, hak'ik'a ta tsorata sosai dan Hajia Turai irin mutanen nan ne da kana ganinsu kaga zubin rashin mutumci da masifa a tare da su, riga da siket ne jikin ta na atamfa sun kamata sosai, sai siririn gyalen da ta d'ora a kafad'a d'aya ta k'araso wajen su Bilal d'in, ido waje ta kalle ta tace "Ke yanzu akan wannan banzan farantin ne har za ki tsaya ki na zagin shi, miye wannan d'in? Ke yanzu in ba halin tsiya ba me akayi akayi wannan banzan farantin da ake siyarwa dala tamanin, shine da ba ki da mutumci har za ki tsaya ki na wani zagin shi, ke kinsan waye wannan yaron kuwa? To Bilal da ki ke gani kamar d'an ciki na haka na d'auke shi, domin kuwa uwar shi ta min abin da ba zan tab'a mantawa ba har abada, kar ki ce za ki saka k'afar wando d'aya da Khadija, dan wallahi ki na sakawa fatar jikin ki ce zata yaye ta bar ki da kunya, Bilal kuma ya zama dole ki zauna da shi dan gidan uban shine nan d'in, yarima ne a fadar mahaifin shi dan haka ya zama dole mai son ya zauna da sarki ya so yarima."

Gyara tsayuwa ta yi har da wani jijjiga ta nuna ta da yatsa tace "Wallahi tun ranar da na ganki nasan sai an samu munafurci a k'ugun ki, bansan irin zaman da ku ke ba dan har yanzu ba mu zauna da Khadija ba, amma dai tabbas nasan akwai matsala a gidan nan, to ki shirya da kyau yarinya dan zuwa na na gaba gidan nan ba lallai ya mi ki kyau ba, wallahi tallahi kinci sa'a akwai in da zanje yanzu cikin gaggawa, ba dan haka ba da sai na kwab'e rigata na yi zigidir kafin in ci ubanki, dan na lura ke 'yar marasa mutumci ce."

Kallon Bilal ta yi ta fito da chocolat daga jakar ta ta hannu da murmushi ta mik'a mi shi tace "Saboda kai kawai na zo gidan nan, ga wannan nasan ka na son ta sosai."

Karb'a ya yi da hannu biyu yace "Nagode aunty."

Shafa kan shi ta yi tace "Ba komai d'an auntyn shi." D'orawa ta yi da "Maman ka na ciki ne?"

Saida ya kalli Haseenah da ta juya ta shiga madafa yace "Bata nan, tun jiya ta tafi gida, ni ma ina so naje wajen ta."

Shiru ta yi ta na nazartar wani abu kafin ta sake shafa kan shi tace "Ka yi hak'uri kaji yarima, yanzu ni ina sauri zanje wani wuri ne duba wasu kaya, kuma kaga banda ikon da zai fitar da kai daga gidan nan dan bansan me ya faru ba, amma ka yi hak'uri kji ko."

Kai kawai ya d'aga mata, murmushi ta sake mi shi tace "Yawwa, to yanzu ka shiga ciki ka zauna kaji ko, ni na tafi sai anjima."

"To aunty." Ya fad'a ya na shiga ta falon mahaifin shi dan sada shi da falon maman shi dan k'ofar waje rufe take, Turai na ganin haka ta lek'a madafar ta ga Haseenah ta yi tsaye jugum ta na jiran Turai ta tafi ko ta samu ta koma falon ta, wani murmushi ta mata tace "Amarya ni zan wuce." Hannu ta sa aljihu ta fito da 'yer jaka goma ko karyawa babu ta cilla mata tace "Wannan zai isheki ki siyi sabbin farantai har dozin dozin, amma ki sani yarima da iyayen shi ba matsiyata bane irin ki."

Har ta juya zata fita ta kuma sake tsayawa ta juyo tace "Idan Usee d'in ya zo ki fad'a ma sa Hajia Turai Dubaï ta zo, sannan ki ce ya fad'a mi ki wacece ni, za ki ji baya ni daga bakin shi."

Juyawa ta yi ta fice ta bar Haseenah duk ta yi gumi saboda tsoro, dan har ga Allah har zuciyar ta tsoron matar ya d'arsu a zuciyarta, dan kana ganin kasan ta take Khadija ta shanye wajen masifa da ma k'arfi, amma da ta samu nutsuwa ta dawo jikinta saita shirya sake wani makircin da tugu, d'aukar kud'in ta yi ta saka a cikin rigar nonon ta, kiran Usman ta yi a waya ya na d'auka ta fashe da kuka tace "Abban Bilal dan Allah duk in da ka ke ka zo gidan nan ka sake ni, wallahi na gaji da abin da ake min kullum ace na yi hak'uri, na gaji Abban Bilal."

Usman da tuni ya zabura ya tashi tsaye cikin tashin hankali yace "Haseenah! lafiya? Me ya faru ki ke kuka?"

"Ni dai kawai ka zo ka bani takardata, ba na so saina tafi gidan mu ka sake tafiya ka dawo da ni, Allah na gaji da zaman gidan ka."

Usman kamar zai fashe da kuka sai kuwa cewa ya yi "Haba Haseenah, ya za ki fad'i haka? Kinsan ke ce rayuwa ta fa, idan ki kace na rabu da ke to ni ina zan saka kai na? Kinsan fa ke ce fitilar gidan nan, ke ce sukuni da walwala na gidan nan, ke ce farin ciki da kwanciyar hankali na, idan ki ka ce za ki bar gidan ya ki ke so na yi to? Dan Allah ki fad'a min miye ya faru ni kuma na mi ki alk'awarin d'aukar mataki da gaggawa."

Tunda Murtala ya lura ya kuma ji abin da yake fad'a kan shi ya d'aure, shi dai a sanin shi har ya auri Haseenah ba wani zazzafan so yake mata ba, hasalima kullum cewa yake auren su Allah ne ya k'addara shi kawai, amma da zai iya hanawa da ya hana dan ya zauna da matar shi, ci gaba ya yi da kallon shi yayin da Haseenah tace "Haka kawai dan ka kori matar ka shine k'awar ta za ta zo har gidan nan ta ci mutumci na ta uwa ta uba, ba irin zagin da baiwar Allahr nan bata min ba, ta kira ni da matsiyaciya yar matsiyata, talaka yar talakawa, duk saboda ka kori matar ka, saboda Allah Abban ni ina da hannu cikin korar matar ka da ka yi? Ba kai ne ka yanke hukuncin ba? Amma shine za ta turo min 'yer iska gida har tana neman duka na, to ba zan iya ba wallahi, dan kalaman da ta fad'a ni sun tsorata ni sosai, dan ko ban bar gidanka ba yau to zan barshi gobe, tunda sun ci alhwashin ba za su barni ba nima na rayu da kai, kawai ni ka zo ka sake ni ko na samu naje gidan mu lafiya."

Cikin wani irin yanayi yace "Wacece ita? Fad'a min sunan ta kawai."

Kamar mai nazari tace "Wata wai ko Hajia Turai, har da cewa na tambaye ka wai kai za ka fad'a min wacece ita."

Daga in da Usman ya ke ya nufi wajen motar shi zai shiga ya na fad'in "Kar ki damu ba sai kince komai ba, ba dai haka tace ba? To barni da ita, nasan sosai, marar mutumci ce ta gidan gaba, amma zan wa tubkar hanci."

Ya na fad'a ya kashe wayar, ita kam har da tsalle duk da bata san me zaiyi ba tasan dai ta sake gogawa Khadija bak'in panti, zai shiga mota Murtala ya rik'o hannun shi ya na kallon k'wayar idon shi yace "Wannan kamar ba Usman d'ina ba, ya naga ka canza haka, me ya faru ne?"

K'ara had'e rai ya yi yace "Ka bari dan Allah ina zuwa yanzu, akwai abin da ya faru ne da gaggawa a gida."

Ya na fad'a ya janye hannun shi ya rufe motar ya wuce zuciya sai tafasa take an tab'a mi shi Haseenah, *Abu azimun inji wata k'awata*, aifa abu ya girmama fiye da yanda ma su karatu suke tunani, dan Usman baiyi k'asa a gwiwa ba wajen zuwa ofishin 'yan sanda akai k'arar Hajia Turai akan taje gidan shi ta ci mutumcin matar shi har da mata barazana, zai iya d'aukar mataki amma dan kar ace ya d'auki doka a hannun shine ya sa ya garzayo nan, amma a mata kashedi ba ita ba gidan shi ko da kuwa me ya ke faruwa a gidan.

Nan fa aka kaiwa Hajia Turai takardar sammaci har gida, lokacin zuwan ta kenan tare da wasu samari da suka d'auko mata kaya sai ga motar 'yan sanda, ana bata takardar ta shiga motar ta fara bala'i tun daga cikin motar, fad'in take "Ai Usman k'aramin d'an hau ne, baisan ni d'in nan babu gidan kason (magark'ama) da ban kwana ba, wani jami'i ne da ya kwana ya tashi a garin nan bai sanni ba, ko ya d'auka duk bala'in nawa iya baki ne, to muje na nuna mi shi yanda ake rawar...kalmar data fad'a ba dad'in ji, amma dai kamar wannan abar ce ta anbata mai kama da ayaba."😎

Su na isa kad'an ne ya rage ofishin ya kama da wuta saboda yanda Hajia Turai ta d'aga murya take masifa, haka Usman bawan Allah ya zama kamar mahaukaci saboda shegiyar Haseenah shima ya biye mata, mutumin da ko da matanshi ba ya son hayaniya amma sai gashi ya zage damste a waje tare da k'awar matar shi suna musayar yawu, ita tana fad'in ita zai ci wa mutumci saboda yar iskar matar shi, shi kuma ya na fad'in akan me za ta je gidan shi ta yiwa matar shi wulak'anci, cikin masifa take fad'in "Kai in banda ma sususu ne kai, wannan tsomalalliyar yarinyar har yaushe ta zo gidan, yaushe ka fara cin gindin ta da har ka mance kalar gindin Khadija 😎, kenan ita wajen bokaye ta kai ka, banza kawai lusari marar kunya, kai har ka isa ka manta hallacin da Khadija ta ma ka, tun ba ka da komai take tare da kai, kusan ma ita ce silar arzik'in ka, amma shine yanzu ka samu sabon..."
Chapter 46 · 0% Book details