← Book details Kallon Kitse Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 27 OF 86

Sashe 27

Kallon Kitse Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Gyara zama Kaltume ta yi tace "Da alama yarinyar da fitsara ta shigo, amma ki bita ta bayan gida, ki nuna mata na gaba ya yi gaba, na baya kuma sai tsinkaye, ki nuna ke ba wai shekaru ku ka yi tare da shi ba, ki nuna mata ke goggagiyace a fannin sanin mijinki, ki nuna mata na ku ba irin na su bane, sannan *wutsiyar rak'umi tayi nesa da k'asa*, kissa, k'awata yanzu kishi ma cikin kissa ake yin shi, kada ki kuskura ki bari yarinyar nan ta gane kina kishi da ita, bare harta fahimci kuna samun matsala da mijinki, k'awata abun ya na da wuya sosai, saboda ya na buk'atar k'arfin zuciya, amma ni nasan za ki iya, saboda kin jure fiye da wannan ma, yanzu ki fad'a min yaushe ne Usman zai dawo hannunki."

"Na yarda Hajiata, amma ai ko ban fad'a mi ki ba ai kin sani"

"Hakane kuma fa." Cewar Kaltume, matsowa ta yi ta rad'a mata abu a kunne, a tare suka bushe da dariya harda tafawa da hannu, Khadija ce tace "Banda mastala dake k'awata, nasan za ki gyara ni."

Bayan fitar Usman kam gida ya nufa, ya samu mahaifinshi ma na shirin fita, saida ya duk'a k'asa ya gaishe su kafin ya zauna kan tabarmar da Hajia ke zaune, fita malam ya yi Usman ya bishi da "A dawo lafiya."

"Allah ya sa." Ya fad'a fita, kallon Hajia ya yi yace "Su Nura har sun fita ne?"

"Sun fita tun safe." Cewar Hajia, d'orawa ya yi da "Ba wani abu da ku ke buk'ata?"

Ba tare da ta d'ago ba tace "Babu komai Fodio, Allah ya yi albarka."

"Ameen Hajia."

Shiru ne ya d'an ratsa kafin Hajia ta kalle shi da kyau tace "Jiya su Rabi'a sun zo nan su ke fad'a min wani abu da ban ji dad'in sa ba ko kad'an, sai dai kuma na yi mamaki da hakan ta faru a gidan ka, duba da tsayawarka akan iyalinka da kuma hak'urin ita Khadijar."

Ajiyar zuciya ya sauke yace "Hakane Hajia, nima abun ya ban mamaki, sai dai koma miye ni nafi ganin laifin Haseenah, tun da Khadija ai ba yau mu ke tare ba, ko tsakani na da ita bamu tab'a samun matsalar da za ta saka mu d'agawa juna murya ba."

"Toh, haka kai ka ke gani, amma yan uwanka ba haka su ke gani ba, sunfi ganin laifin Khadija."

Murmushi ya yi yace "To Hajia koma me su ke gani ai wannan matsalar su ce, tun da dai ni ga yanda nake gani kuma na sani."

"Hakane, Allah dai ya kyauta, amma dan Allah a saka ido sosai saboda gudun abin da zaije ya dawo."

"Insha Allahu Hajia."

Mik'ewa ya yi ya zura takalmin shi yace "Hajia ni zan wuce, amma anjima da dare zan dawo, dan mun kwana biyu bamu had'u da yan rigamar nawa ba (k'annan shi)."

Daroya ta yi tace "Gaskiya kam, dan tuni ma su ka fara k'orafin amarya ta b'oye ka."

"Na sani dama ayi hakan." Ya fad'a ya na dariya, har ya juya Hajia tace "Yawwa har na sha'ada ban fad'a ma ka ba."

Juyowa ya yi ya dawo ya sunkuya, d'orawa ta yi da "Jiya matar *Issoufou* (d'an k'anin baban shi) ta haihu, an samu 'ya, idan ka samu dama sai ka je, su ma kuma matan sai ka fad'a mu su."

"Ah masha Allah, insha Allah kam Hajia zanje, amma na yi mamaki da bai kira ni ba."

"Watak'ila ya manta ne."

"Ba shakka kam."

Da haka ya bar gidan kuma ya na shiga mota ya kira Issoufou, take yace mi shi su had'u gidan yanzu zai je, haka ko akayi, ka zuwan nashi alkairi ne, domin kuwa kud'i ya bashi ma su yawa ayi hidima, bayan tafiyar shi kuma sai ya ya sa aka kawo mi shi kayan abinci, daga nan kuma makaranta ya wuce d'aukar Bilal.

Suna ta hirar su cikin farin ciki sai ga Usman tare da Bilal, sannu da zuwa suka ma sa in da ya dinga tsokanar Kaltume su na wasa da dariya, da haka ya lek'a wajen Haseenah, ya samu ta na girki ba ta gama ba, dan haka ya fita yace sai ya dawo, saida ya dawo su ka yi sallama da Kaltume, sai dai mamaki ya kama shi ganin su na cin abinci har da Bilal ma, dan shigowar shi ya ga gas a waje da tukunya, sam bai kawo a ran shi abinci su ka girka ba, haka ya fita da tunani iri iri da kuma niyyar tsayar da wannan abun, dan ba zai yarda tun yanzu su raba mi shi kan gida ba ta hanyar raba abinci.

_Ah to banga laifinka ba._🤷‍♀

*Luv u guy's*
24/01/2020 à 21:19 - 💋😘💋: 💑💑💑💑💑💑💑💑💑💑
*KALLON KITSE*
_(Ake wa rogo)_
💑💑💑💑💑💑💑💑💑💑

_SAMIRA HAROUNA_

*Littatafan marubuciyar*

*1* _KAUSSAR_
*2* _D'AUKAR FANSA_
*3* _BA SO BANE_
*4* _AUREN HAD'I_
*5* _SANIN MASOYI_
*6* _JIHADI_
*7* _K'ANGIN RAYUWA_
*8* _ITACE K'ADDARARMU_
*9* _KAWU NA NE_
*10* _MAATA_
*11* _KALLON KITSE..._

*SADAUKARWA GA*

_MATAN FARKO_🧕🏼 *(UWAYEN GIDA)*

🇸🇦 *ZAMAN AMANA WRITER'S*
_(Gidan zaman lafiya da amana insha Allah)_🤜🤛

```Fatan alkairi masoya```

_Bismillahir rahamanir rahim_

_*ALLAH GATAN BAWA*_

*16*

Farar miya Haseenah ta yi da shinkafa, ba wai miyar ba ta yi bane a wajen Usman, sai dai ji ya yi cin shinkafar ta gundure shi, kuma hakan baya rasa nasaba da sabon da Khadija ta mi shi na girka abinci kala kala, musamman da tasan ba ya san shinkafa sosai, sai ta yi wata d'aya ba ta girka ta ba, yanzun ma bai wani ci mai yawa ba ya bar shi, ko da ya yi wanka ya shirya falon Khadija ya shigo, Uwani na ganin haka ta mik'e ta fita, Bilal kuma dama ya na ciki ya na shiri, Kaltume kam ta na sallah la'asar ta wuce gida, zaune ya yi kalle ta ta na fad'in "Har ka fito?"

"Um." Ya fad'a ya na sake kafe ta da ido, ita kam gyara gilashinta ta yi ta kalle shi tace "Ya dai? Da magana ne? Wannan kallon haka."

K'asa ya kalla kafin ya kalle ta yace "D'azu da na shigo sai na ga kamar girki ku ka yi ko?"

Ba tare da shakka ba tace "Eh, girki na yi, da matsala ne?"

Gyara zama ya yi kamar zai had'e ta yace "Sosai ma, Khadija kar ki ce min ba ki hango matsalar da ni na hango ba, hakan bai dace ba, kuma gaskiya ba na so, idan har zai yiwu, to cikin d'aya dole ku yi d'aya, ko dai ku had'a kanku ku dinga girki tare, ko kuma dai duk ranar girkin d'aya to d'aya ba za ta tab'a d'ora min tukunya ba da sunan girki ba, wannan hukuncin yankakke ne, kuma umarni."

Mik'ewa ya yi ya juya ya kalli d'akin Bilal ya kalli agogon hannun shi, mik'ewa ta yi ta kalle shi tace "Ban k'i ta taka ba, amma kafin ka yanke wannan hukucin ya kamata ka fara fad'awa amaryarka cewa ba'a raba abinci a gidan nan, in dai har za ta ci gaba da ware mana abinci ni da yarona, to wallahi ba zan ci ba haka ma d'ana, kuma ko kaga ai bama zauna da yunwa ba alhalin Allah ya hore abinci ta ko ina, wannan shine."

Ta gaban shi ta rab'a za ta wuce ya rik'o hannunta, kallon ta ya yi yace "Na fad'a mi ki ba na so, raba abinci kuma na yan kwanaki ne da ba su taka kara sun karya ba, idan ki ka duba tsawon lokacin da mu ka d'auka tare hakan bai tab'a faruwa ba, me ya sa yanzu za ki gagara fahimta Khadija? D'an lokaci fa kawai tace a bata ita ma ta san ta na da miji, me ya sa za ki zama mai son kan ki dayawa, me zai rage ki idan ki ka hak'ura ki ka ci abincin, nan da lokacin da kwananta zai k'are fa shikenan komai ya wuce."

Rik'e k'ugu ta yi da hannu d'aya tace "Uhum! Anzo gurin, yau kuma sai gashi ka na fad'in wai ni ce mai son kai na, ni ce mai son kai na yau? To na ji kuma nagode, amma ka sani in dai wannan ne son kai to tabbas ni mai son kai na ce, wallahi ba zai tab'a yiwuwa ba ta barbarad'a min iskanci a abinci sannan ta bani na ci, wallahi ka ji na rantse ko ba zai yiwu ba, rai a baran mai shine, lafiya kuma uwar jiki, daidai da ciwon hannu wannan idan ya same ni akwai abin da za ka iya yi min ne? Ni fa zan ji zafin kuma na yi jinyata, hasalima duk soyayyar da ka ke sauki burutsun cewa kana min wallahi babu abin da za ka iya tsinana min, haka kawai kuma sai na jefa kai na a motar da na tabbatar ba ta da birki, rai fa guda d'aya ne."

Yanda take masifa sai abun ya ba shi dariya da mamaki, a zaman shi da ita bai tab'a ganin ta na fad'a haka ba sai yau, b'ata rai ya yi yace "Wallahi ba da wasa nake ba, kar ki sake d'ora min tukunya indai har ana girki a gidan nan, kinji na fad'a mi ki."

Za ta yi magana Bilal ya fito daga d'akin, sai kawai ta yi murmushi ta sa hannu ta shafo d'an gemunshi ta kashe masa ido tace "Ban ji da kyau, d'an sake maimaita min."

Dariya ce ta so sub'uce mi shi sai ya dake ya matsa kusan ta ya rad'a mata a kunne "Wallahi karki sake na sake ganin kin aza girkin ki, in ba haka ba rai zai b'ace fa."

Bilal ne ya shiga tsakansu ya na fad'in "Idan na bi taku sai na makara islamiyya, muje Abba."
Chapter 27 · 0% Book details