Sashe 81
Kallon Kitse Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Shafa kumatun shi ta yi ta d'aga shi zata koma d'aki dan ta bashi damar yin tunani, sumbatar kumatunshi ta yi ta rad'a mi shi a kunne cewa "Kar ka manta Khadija na matuk'ar son ka sosai, kai ne rayuwa ta babban mutum."
Da murmushi kawai ya bita da kallo harta shige d'aki, ya jima nan zaune ya na tunanin abin da ta fad'a mi shi, har ga Allah babu ko k'aunar Haseenah a zuciyar shi bare soyayyarta, amma zai dawo da uta saboda farin cikin Khadija kawai, amma kuma ba yanzu sai ta shiga watan haihuwar ta kad'ai zai dawo da ita, kamar yanda ta sa Khadija zama a gidan su ita ma saita d'and'ana zaman gidan sosai ya ratsata kafin, tashi ya yi ya shiga d'aki saida su ka yi shirin kwanciya kafin ya fad'awa Khadija ya ji zai dawo da ita amma da sharad'i, da sauri tace "Sharad'in me?"
"Zan dawo da ita amma ba yanzu ba, idan hakan ya mi ki to, in kuma bai mi ki ba to abar maganar, sannan zan dawo da ita ne ba dan ina buk'atar zamanta a gida na ba sai dan kin matsa."
Kallonta ya yi yace "Kin yarda?" Da sauri tace "Na yarda Abban Bilal, duk da haka na san ba zaka tauye hakk'in ta ba."
Daga ranar ya samu zaman lafiya Khadija ta daina mi shi magana, haka aka kwashe wasu watannin a lokacin cikin Haseenah ya shiga watan haihuwa, taje asibiti aka bata sati biyu idan bata haihu ba ta koma, a lokacin Khadija da Hajia da Usman da malam suka je gidan su Haseenah biko, abun ya bawa Haseenah kunya sosai ta yanda ta dinga kuka ta na neman gafarar Usman da Khadija, nan iyayen ta ma suka basu hak'uri kafin aka k'ara mata fad'a da nasiha, Khadija da kanta ta tayata had'a kaya dan da tace ma su bari har gobe Khadija tace a'a, tsaf suka had'a kayan suka fito tare da ciki kowace ta na turawa, kayan Usman ya karb'a ya kai mota kafin suka tafi, gida ma saida malam ya sake mu su jan kunne tare da tunatarwa akan zaman aure ibada ne kafin Usman ya mayar da su gida, suna fita Haseenah ta sake fashewa da kuka ta rik'e k'afar Khadija tace "Aunty Khadija ki yi hak'uri ki yafe min dan Allah, wallahi na yi nadamar abin da na aikata."
Kamata Khadija ta yi tace "Haseenah na fad'a mi ki ba komai wallahi, na hak'ura har abada kuma, Allah dai ya k'ara had'a kan mu."
Bilal ne ya fito daga d'aki da riga a hannu ya mik'owa Khadija yace "Mummy taimaka saka min rigar nan, wuyanta matse ni yake."
Da sauri Haseenah ta tara mi shi hannu tace "Kawo na saka ma ka yarima." Bata ya yi ya na kallon mummyn shi a d'ard'ar ya matsa kusa da ita, saida ta saka mi shi ta kalle shi tace "Yarima ka yi hak'uri ka yafewa auntynka kaji, na yi nadamar abin da na yi."
Kallon mummyn shi ya sake yi ta sakar mi shi murmushi hakan ya sa ya rumgume Haseenah yace "Aunty amarya, uwa fa ba ta neman yafiyar 'ya'yan ta."
Kallon shi ta yi tace "To in dai uwa ce ni ai ba aunty ya kamata ka kira ni ba."
Murmushi ya yi sosai ya kalle ta da kunya yace "Mummy." Har zuciya Haseenah taji muryar Bilal ya kira ta da sunan uwa, rumgume shi ta yi take taji wata soyayyar shi ta d'arsu a zuciyar ta, sun jima nan har Usman ya shigo kafin kowa ya nufi na shi d'akin, wani irin sanyi Haseenah taji sai take ji ashe zaman lafiya da wanda Allah ya had'a ka zama da shi dad'i ne da shi, sai taji kamar yau ne aka fara kawota gidan tare da k'udurawa a ranta zata wa Khadija biyayya ko da kuwa za ta zama baiwarta ne hakan ba zai dame ta ba, har ta yi shirin kwanciya Usman ya shigo da doguwar riga yace ta same shi falon Khadija, da to ta amsa mi shi ya fice ko kallon ta baiyi ba, haka ta fito jiki a sanyaye dan tasan yanzu ba mutumcin ta Usman zai gani ba, kuma kamar yanda ya fad'a a gidansu cewa ya fa zo ne saboda Khadija ce ta matsa, to tabbas tasan dawowar nan da ta yi zaman Khadija ne za ta yi, sun samu Khadija zaune da alama su take jira, zaune ya yi kusan Khadija Haseenah kuma cike da kunya ta zauna k'asa, Khadija ce tace ta zauna sama amma tace a'a tafi jin dad'in nan, Usman ne ya gyara murya ya fara magana kamar haka.
"...
15/03/2020 à 23:06 - 💋😘💋: 💑💑💑💑💑💑💑💑💑💑
*KALLON KITSE*
_(Ake wa rogo)_
💑💑💑💑💑💑💑💑💑💑
_SAMIRA HAROUNA_
*Litattafan marubuciyar*
*1* _KAUSSAR_
*2* _D'AUKAR FANSA_
*3* _BA SO BANE_
*4* _AUREN HAD'I_
*5* _SANIN MASOYI_
*6* _JIHADI_
*7* _K'ANGIN RAYUWA_
*8* _ITACE K'ADDARARMU_
*9* _KAWU NA NE_
*10* _MAATA_
*11* _KALLON KITSE..._
*SADAUKARWA GA*
_MATAN FARKO_ 🧕🏼 *(UWAYEN GIDA)*
🇸🇦 *ZAMAN AMANA WRITER'S*
_(Gidan zaman lafiya da amana insha Allah)_🤜🤛
🔚🔚🔚🔚🔚🔚🔚
```Fatan alkairi masoya```
*ALHAMDULILLAH ALA NI'IMATUL ISLAM*
_Bismillahir rahamanir rahim_
*40*
"Haseenah, Allah ya nufa dai akwai sauran zama tsakani na dake, ina fatan abubuwan da suka faru a baya sun koya mi ki wa'azi, Haseenah zan fad'a mi ki wata magana wacce a baya na ke fargaba da shakkun fad'a mi ki, ki yi hak'uri ko da hakan zai b'ata mi ki rai, kinga Khadija da ki ke gani?" Ya fad'a ya na nuna Khadija dake gefen shi, Haseenah dai ta baza kunne ta na saurare, d'orawa da "Ba iya matata ba ce kad'ai, rayuwa ta ce, kuma kin dawo gidan nan ne a dalilin ta, ita ta dage har saida ta ga kin dawo gidan nan, ke na tak'aice mi ki ma har saida ta kai munyi fad'a da ita ko magana ba ma yi saboda ke kawai, Haseenah dan Allah ki tsarkake zuciyarki ku zauna lafiya, Allah kuma ya bani ikon yin adalci a tsakanin ku."
Khadija ce tace "Ameen mijin mu, Abban Bilal da kuma k'annan shi ma su zuwa, mun yarda ka ci gaba da jagorancin mu har zuwa gidan aljanna, mu na da yak'inin ba za mu tab'a yin nadama saboda kai *adalin miji* ne da mu ka yi sa'ar samun shi a wannan zamanin."
Fuskar nan ta Usman kamar gonar audiga haka yake mata murmushi, saida ta kai aya yace "Allah yasa matata, Allah kuma ya sa ba zigani ki ke yi ba dan naga ki na neman fasa min kai."
Dariya ta yi sosai ta mi shi fari da ido tace "A haba dai alaji, ai kasan ba ma haka da kai, duk abin da zai fito daga baki na akan ka gaskiya ne, saima saya wani abun da na ke saboda tsaro."
Kashe mata ido ya yi ita ma kuma haka, Haseenah ta saki baki ta na kallon su, wani zafi taji ya na taso mata a zuciya tare da jin mugun kishi, amma a take ta lumshe ido ta furta a ranta "Inna lillahi wa'inna ilaihi raju'un, Allah kasa na fi k'arfin zuciya ta."
Ta na bud'a ido ta kalle su sai taji sanyi tare da jin sauk'in abin da ke ran ta, murmushi ta yi ta na ci gaba da kallon su ta ayyana a ranta in har ta na son zama da Usman dole ta girmama matar shi, sannan ya zama dole ta iya zama da su ta durmiya cikin rayuwar da suke, da k'yar ta mik'e tsaye saboda nauyin da ta yi tace "To sarakan soyayya, ni zan shiga na kwanta, kunsa fa na yi kewar gado na."
Ba Khadija ba har Usman saida ya dara kafin yace "Kenan rayuwar gida babu dad'i ko?"
Turo baki ta d'anyi tace "Babu kam." Jingina ya yi a kujera yace "Dan haka sai kowace ta kama kanta ta, in ba haka ba zan dinga yanka mu ku kati ne ku na tafiya gida ku na hutu."
Kallon shi Khadija ta yi ta kalli Haseenah tace "Idan mutum ya shirya siyan abinci da kwanan kad'aici to ai ko yanzu a shirye muke, dan idan zamu shekara gida ma kaga lafiya lau mu ke kum hankali kwance."
Haseenah ce ta juy tace "Saida safen ku aunty." Da murmushi tace "Allah tashe mu lafiya."
Mik'ewa Usman ya yi yace "Bara na raka ki mai ciki, kar ki je ki zame." Hannun ta ya kama har suk isa falon ta, suna shiga ya saki hannunta har ta shiga uwar d'aka ta kwanta, juyawa ya yi zai fita yace "Ina zuwa."
D'akin Khadija ya je ya mata saida safe kafin ya koma d'akin Haseenah, sam bai wani sakar mata fuska ba har bacci ya d'auke su, dan har ga Allah har yanzu ya na jin haushin ta idan ya tuna baya, kawai babu yanda zaiyi ne Khadija ta tilasta mata ya dawo da ita, kuma tunda ya dawo da ita dole ya sauke hakk'ok'in ta ko kuma ya had'u da fushin ubangiji, Haseenah kuma sam ba ta yi bacci ba saboda sabon ciwon bayan da ya taso mata, tun tana shiru ta na addu'a har ta daddab'a Usman ya farka, nan fa ya rikice saboda ba'a tab'a nak'uda a gaban shi ba, haihuwar Bilal ma baya garin, Khadija ya taso daga bacci ta taimaka mi shi, kayan haihuwar Haseenah na gida ba'a d'auko ba sai Khadija ce ta d'auko nata su ka tafi asibiti da su, saida aka karb'e ta an shiga d'akin haihuwa kad'ai Usman ya kira Hajia ya fad'a mu su, kafin Hajia ta iso Khadija ma ta fara jin bayan ta na d'aurewa tare da rik'ewar mara, a hankali taja baya ta zauna kan bancin da ke wajen, da sauri Usman ya sunkuya ya na kallon ta yace "Ya dai Nana, ko dai kema jikin ne?"
Wani iska ta furzar ta girgiza kai tace "Um um." Sake kafeta ya yi da ido yace "Kin tab'a ba komai?"
"Babu." Ta fad'a ta na huci, kallon tuhuma ya mata yace "Khadija ko dai kema a shigar da ke ciki ne?"
"Ka bar shi kawai, ba buk'ata." Ta fad'a a wahalce, "Kin tabbata?"
Da murmushi kawai ya bita da kallo harta shige d'aki, ya jima nan zaune ya na tunanin abin da ta fad'a mi shi, har ga Allah babu ko k'aunar Haseenah a zuciyar shi bare soyayyarta, amma zai dawo da uta saboda farin cikin Khadija kawai, amma kuma ba yanzu sai ta shiga watan haihuwar ta kad'ai zai dawo da ita, kamar yanda ta sa Khadija zama a gidan su ita ma saita d'and'ana zaman gidan sosai ya ratsata kafin, tashi ya yi ya shiga d'aki saida su ka yi shirin kwanciya kafin ya fad'awa Khadija ya ji zai dawo da ita amma da sharad'i, da sauri tace "Sharad'in me?"
"Zan dawo da ita amma ba yanzu ba, idan hakan ya mi ki to, in kuma bai mi ki ba to abar maganar, sannan zan dawo da ita ne ba dan ina buk'atar zamanta a gida na ba sai dan kin matsa."
Kallonta ya yi yace "Kin yarda?" Da sauri tace "Na yarda Abban Bilal, duk da haka na san ba zaka tauye hakk'in ta ba."
Daga ranar ya samu zaman lafiya Khadija ta daina mi shi magana, haka aka kwashe wasu watannin a lokacin cikin Haseenah ya shiga watan haihuwa, taje asibiti aka bata sati biyu idan bata haihu ba ta koma, a lokacin Khadija da Hajia da Usman da malam suka je gidan su Haseenah biko, abun ya bawa Haseenah kunya sosai ta yanda ta dinga kuka ta na neman gafarar Usman da Khadija, nan iyayen ta ma suka basu hak'uri kafin aka k'ara mata fad'a da nasiha, Khadija da kanta ta tayata had'a kaya dan da tace ma su bari har gobe Khadija tace a'a, tsaf suka had'a kayan suka fito tare da ciki kowace ta na turawa, kayan Usman ya karb'a ya kai mota kafin suka tafi, gida ma saida malam ya sake mu su jan kunne tare da tunatarwa akan zaman aure ibada ne kafin Usman ya mayar da su gida, suna fita Haseenah ta sake fashewa da kuka ta rik'e k'afar Khadija tace "Aunty Khadija ki yi hak'uri ki yafe min dan Allah, wallahi na yi nadamar abin da na aikata."
Kamata Khadija ta yi tace "Haseenah na fad'a mi ki ba komai wallahi, na hak'ura har abada kuma, Allah dai ya k'ara had'a kan mu."
Bilal ne ya fito daga d'aki da riga a hannu ya mik'owa Khadija yace "Mummy taimaka saka min rigar nan, wuyanta matse ni yake."
Da sauri Haseenah ta tara mi shi hannu tace "Kawo na saka ma ka yarima." Bata ya yi ya na kallon mummyn shi a d'ard'ar ya matsa kusa da ita, saida ta saka mi shi ta kalle shi tace "Yarima ka yi hak'uri ka yafewa auntynka kaji, na yi nadamar abin da na yi."
Kallon mummyn shi ya sake yi ta sakar mi shi murmushi hakan ya sa ya rumgume Haseenah yace "Aunty amarya, uwa fa ba ta neman yafiyar 'ya'yan ta."
Kallon shi ta yi tace "To in dai uwa ce ni ai ba aunty ya kamata ka kira ni ba."
Murmushi ya yi sosai ya kalle ta da kunya yace "Mummy." Har zuciya Haseenah taji muryar Bilal ya kira ta da sunan uwa, rumgume shi ta yi take taji wata soyayyar shi ta d'arsu a zuciyar ta, sun jima nan har Usman ya shigo kafin kowa ya nufi na shi d'akin, wani irin sanyi Haseenah taji sai take ji ashe zaman lafiya da wanda Allah ya had'a ka zama da shi dad'i ne da shi, sai taji kamar yau ne aka fara kawota gidan tare da k'udurawa a ranta zata wa Khadija biyayya ko da kuwa za ta zama baiwarta ne hakan ba zai dame ta ba, har ta yi shirin kwanciya Usman ya shigo da doguwar riga yace ta same shi falon Khadija, da to ta amsa mi shi ya fice ko kallon ta baiyi ba, haka ta fito jiki a sanyaye dan tasan yanzu ba mutumcin ta Usman zai gani ba, kuma kamar yanda ya fad'a a gidansu cewa ya fa zo ne saboda Khadija ce ta matsa, to tabbas tasan dawowar nan da ta yi zaman Khadija ne za ta yi, sun samu Khadija zaune da alama su take jira, zaune ya yi kusan Khadija Haseenah kuma cike da kunya ta zauna k'asa, Khadija ce tace ta zauna sama amma tace a'a tafi jin dad'in nan, Usman ne ya gyara murya ya fara magana kamar haka.
"...
15/03/2020 à 23:06 - 💋😘💋: 💑💑💑💑💑💑💑💑💑💑
*KALLON KITSE*
_(Ake wa rogo)_
💑💑💑💑💑💑💑💑💑💑
_SAMIRA HAROUNA_
*Litattafan marubuciyar*
*1* _KAUSSAR_
*2* _D'AUKAR FANSA_
*3* _BA SO BANE_
*4* _AUREN HAD'I_
*5* _SANIN MASOYI_
*6* _JIHADI_
*7* _K'ANGIN RAYUWA_
*8* _ITACE K'ADDARARMU_
*9* _KAWU NA NE_
*10* _MAATA_
*11* _KALLON KITSE..._
*SADAUKARWA GA*
_MATAN FARKO_ 🧕🏼 *(UWAYEN GIDA)*
🇸🇦 *ZAMAN AMANA WRITER'S*
_(Gidan zaman lafiya da amana insha Allah)_🤜🤛
🔚🔚🔚🔚🔚🔚🔚
```Fatan alkairi masoya```
*ALHAMDULILLAH ALA NI'IMATUL ISLAM*
_Bismillahir rahamanir rahim_
*40*
"Haseenah, Allah ya nufa dai akwai sauran zama tsakani na dake, ina fatan abubuwan da suka faru a baya sun koya mi ki wa'azi, Haseenah zan fad'a mi ki wata magana wacce a baya na ke fargaba da shakkun fad'a mi ki, ki yi hak'uri ko da hakan zai b'ata mi ki rai, kinga Khadija da ki ke gani?" Ya fad'a ya na nuna Khadija dake gefen shi, Haseenah dai ta baza kunne ta na saurare, d'orawa da "Ba iya matata ba ce kad'ai, rayuwa ta ce, kuma kin dawo gidan nan ne a dalilin ta, ita ta dage har saida ta ga kin dawo gidan nan, ke na tak'aice mi ki ma har saida ta kai munyi fad'a da ita ko magana ba ma yi saboda ke kawai, Haseenah dan Allah ki tsarkake zuciyarki ku zauna lafiya, Allah kuma ya bani ikon yin adalci a tsakanin ku."
Khadija ce tace "Ameen mijin mu, Abban Bilal da kuma k'annan shi ma su zuwa, mun yarda ka ci gaba da jagorancin mu har zuwa gidan aljanna, mu na da yak'inin ba za mu tab'a yin nadama saboda kai *adalin miji* ne da mu ka yi sa'ar samun shi a wannan zamanin."
Fuskar nan ta Usman kamar gonar audiga haka yake mata murmushi, saida ta kai aya yace "Allah yasa matata, Allah kuma ya sa ba zigani ki ke yi ba dan naga ki na neman fasa min kai."
Dariya ta yi sosai ta mi shi fari da ido tace "A haba dai alaji, ai kasan ba ma haka da kai, duk abin da zai fito daga baki na akan ka gaskiya ne, saima saya wani abun da na ke saboda tsaro."
Kashe mata ido ya yi ita ma kuma haka, Haseenah ta saki baki ta na kallon su, wani zafi taji ya na taso mata a zuciya tare da jin mugun kishi, amma a take ta lumshe ido ta furta a ranta "Inna lillahi wa'inna ilaihi raju'un, Allah kasa na fi k'arfin zuciya ta."
Ta na bud'a ido ta kalle su sai taji sanyi tare da jin sauk'in abin da ke ran ta, murmushi ta yi ta na ci gaba da kallon su ta ayyana a ranta in har ta na son zama da Usman dole ta girmama matar shi, sannan ya zama dole ta iya zama da su ta durmiya cikin rayuwar da suke, da k'yar ta mik'e tsaye saboda nauyin da ta yi tace "To sarakan soyayya, ni zan shiga na kwanta, kunsa fa na yi kewar gado na."
Ba Khadija ba har Usman saida ya dara kafin yace "Kenan rayuwar gida babu dad'i ko?"
Turo baki ta d'anyi tace "Babu kam." Jingina ya yi a kujera yace "Dan haka sai kowace ta kama kanta ta, in ba haka ba zan dinga yanka mu ku kati ne ku na tafiya gida ku na hutu."
Kallon shi Khadija ta yi ta kalli Haseenah tace "Idan mutum ya shirya siyan abinci da kwanan kad'aici to ai ko yanzu a shirye muke, dan idan zamu shekara gida ma kaga lafiya lau mu ke kum hankali kwance."
Haseenah ce ta juy tace "Saida safen ku aunty." Da murmushi tace "Allah tashe mu lafiya."
Mik'ewa Usman ya yi yace "Bara na raka ki mai ciki, kar ki je ki zame." Hannun ta ya kama har suk isa falon ta, suna shiga ya saki hannunta har ta shiga uwar d'aka ta kwanta, juyawa ya yi zai fita yace "Ina zuwa."
D'akin Khadija ya je ya mata saida safe kafin ya koma d'akin Haseenah, sam bai wani sakar mata fuska ba har bacci ya d'auke su, dan har ga Allah har yanzu ya na jin haushin ta idan ya tuna baya, kawai babu yanda zaiyi ne Khadija ta tilasta mata ya dawo da ita, kuma tunda ya dawo da ita dole ya sauke hakk'ok'in ta ko kuma ya had'u da fushin ubangiji, Haseenah kuma sam ba ta yi bacci ba saboda sabon ciwon bayan da ya taso mata, tun tana shiru ta na addu'a har ta daddab'a Usman ya farka, nan fa ya rikice saboda ba'a tab'a nak'uda a gaban shi ba, haihuwar Bilal ma baya garin, Khadija ya taso daga bacci ta taimaka mi shi, kayan haihuwar Haseenah na gida ba'a d'auko ba sai Khadija ce ta d'auko nata su ka tafi asibiti da su, saida aka karb'e ta an shiga d'akin haihuwa kad'ai Usman ya kira Hajia ya fad'a mu su, kafin Hajia ta iso Khadija ma ta fara jin bayan ta na d'aurewa tare da rik'ewar mara, a hankali taja baya ta zauna kan bancin da ke wajen, da sauri Usman ya sunkuya ya na kallon ta yace "Ya dai Nana, ko dai kema jikin ne?"
Wani iska ta furzar ta girgiza kai tace "Um um." Sake kafeta ya yi da ido yace "Kin tab'a ba komai?"
"Babu." Ta fad'a ta na huci, kallon tuhuma ya mata yace "Khadija ko dai kema a shigar da ke ciki ne?"
"Ka bar shi kawai, ba buk'ata." Ta fad'a a wahalce, "Kin tabbata?"