Sashe 44
Kallon Kitse Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Da safe ma haka Haseenah ta gama shirya abin kari sai dai a k'urarren lokaci, hakan ne ya janyo ta manta ba ta zuba komai a abincin ba, ba dan ta ji abinda ya fad'a ba sai dan ta manta, ta gama shiri za ta fito ya shigo d'akin cikin tsadaddiyar shadda bla (bleue) sai k'amshi ya ke, rumgume ta ya yi ya sumbace ta kafin ya d'ago ta daga jikin shi, hannu ya sa aljihu ya kamo hannun ta ya d'ora mata wani matashin akwati na sark'a, da mamaki ta ke kallon abun har ta bud'a, da kan shi ya d'auki sark'ar ya mak'ala mata a wuya, sannan ya cire mata yan kunnan da ta saka ya saka mata na sark'ar, hannu ta sa ta shafa tace "Kai, amma na ji dad'i sosai da kyautar nan, nagode." Ta fad'a ta na kallon shi, murmushi ya yi yace "Ba komai bane wannan, irin faranta min da ki ke ai kin wuce karb'ar sark'ar zinare."
Zaro ido ta yi dan sai yanzu tasan sark'ar dake wuyanta, murna fa ba'a magana wajen Haseenah ta dangwala sark'ar zinare a wuya, haka su ka fito ta na karairaya kamar ta karye, da kan ta ta zuba mu su abincin dan tuni Bilal ya na islamiyya, Khadija da ta fahimci takunta kamar dariya ma ta bata, dan ga dukkan alama yau ta fara saka sark'a mai tsada, tab'e baki ta yi a ran ta tace "Da alama ba ki san sark'a mai tsada ba ko a ido, dan da kin sani da yanzu kin kashe kan ki da ganin kusan kullum sune a wuya na."
Lafiya lau suka ci abinci su ka kammala, saida ya mik'e zai fita ya kalli Khadija yace "Nagode da alfarmar da ki ka min, sannan ki min message d'in abubuwan da ku ke buk'ata, anjima zan turo Bilyamin ya kawo mu ku."
Ita kam dariya ma ya bata dan haka ta mi shi wani murmushi mai shiga rai tace "Angama ranka shi dad'e."
Ya na fita ta mik'e zata koma d'akin ta, kallon Haseenah ta yi ta na murmushi tace "Sai kuma gashi yau gishiri bai shiga abincinki ba, ko ya akayi haka ta faru oho?"
Kafin ta yi magana ta shige ta barta nan, ta na shiga falon ta ta tura mi shi sak'on abubuwan da suka kusan k'arewa da wanda ma suka k'are, lokacin har Haseenah ta shiga girkin rana aka kawo kayan, Usman ma gida ya dawo cin abinci dan har ga Allah ba ya so ana kai mi shi abinci waje in dai girkin Haseenah, dan ya gama fahimta tafi k'warewa wajen iya dafa shinkafa da jar miya, yamma na yi kuma Khadija ta karb'i girki, ita ma saida ta gama girkin ta lafiyayye sai kawai ta d'auki sukari (sugar) ta zuba a ciki, tsaf ta kawo shi ta jera kamar abun k'warai, sai dai yau a shirye take duk wacce za ayi ayi a gidan, dan ta lura Haseenah ba zaman lafiya take nema da ita ba.
Zaune suke wajen cin abinci Khadija na zuba ma kowa abincin, k'amshin abincin ne ya sa Usman had'iyar yawu har ya riga kowa kaiwa a baki, rufe ido ya yi ya tauna ya kuma had'e, bud'e ido ya yi ya sauke akan Khadija da ke shirin kai loma a bakin ta, shiru ya yi ya na kallon kowa har suka kai bakin su suma, kasa had'ewa su ka yi suka furzar dan haka Khadija ta d'ago ta kalli Haseenah, murmushi ta mata cike da makirci tace "Ramawa ki ka yi kenan?"
Zazzare ido Haseenah ta yi ta kalli Usman da ya kafe ta da ido ya na kallo, cikin in'i'na tace "...
*Maganin biri karen maguzawa, waya fad'a mi ki barno gabas take.*
12/02/2020 à 21:57 - 💋😘💋: 💑💑💑💑💑💑💑💑💑💑
*KALLON KITSE*
_(Ake wa rogo)_
💑💑💑💑💑💑💑💑💑💑
_SAMIRA HAROUNA_
*Litattafan marubuciyar*
*1* _KAUSSAR_
*2* _D'AUKAR FANSA_
*3* _BA SO BANE_
*4* _AUREN HAD'I_
*5* _SANIN MASOYI_
*6* _JIHADI_
*7* _K'ANGIN RAYUWA_
*8* _ITACE K'ADDARARMU_
*9* _KAWU NA NE_
*10* _MAATA_
*11* _KALLON KITSE..._
*SADAUKARWA GA*
_MATAN FARKO_ 🧕🏼 *(UWAYEN GIDA)*
🇸🇦 *ZAMAN AMANA WRITER'S*
_(Gidan zaman lafiya da amana insha Allah)_🤜🤛
```Fatan alkairi masoya```
_Bismillahir rahamanir rahim_
*23*
"Wallahi ba ni bace, babu abin da na saka a abincin nan."
Had'e fuska Khadija ta yi tace "Kinga Haseenah, ni da ke yanzu duk d'aya ne, tunda kin rama to komai ya wuce, kin fahimta."
Cikin b'acin rai Usman yace "Yanzu miye haka? Me ku ke son mayar da ni to? Ke koma miye ai laifin ki ne tunda ke ki ka fara, ki na babba amma ko tsaya d'aukar raini ga k'aramar k'anwar ki, mtssss."
Tsaye ta mik'e ta na kallon shi tace "Dakata Abban Bilal, ni nafi k'arfin na tsaya jawa kai na raini wajen wannan mutsitsiyar yarinyar, gata ka tambaye ta tsakani da Allah uban waye ya fara zuba gishiri ko sugar a abinci? Ita ce da kan ta, har ni za ta wa makirci, saboda ta baka ka kurb'a shine za ta dinga ja min magana a wajen ka ta hanyar lalata abincin da ta girka, me ta ke nufi da hakan? Tasan dole ni za'a zarga dama ba ita ba, shine ni ma na nuna mata mace ce ni kuma gaba na ke da ita ko a haihuwa."
Zata fice ya mik'e tsaye yace "Dawo nan."
Dawowa ta yi ta tsaya sai Haseenah da ta mik'e ta kalle shi tace "Wallahi k'arya ta ke min babu abin da na saka, kawai sharri ne ta ke so ta ja min, taya ma zan lalata abin da na girka da hannu na?"
Kusanta Khadija ta matso cikin b'acin rai ta nuna ta da hannu tace "Wallahi ki ka sake cewa ina mi ki k'arya sai na fitar mi ki da jini a baki, marar kunya kawai fitsararriya, ke har ni za ki kalla ki ce ina mi ki k'arya? Wace ce ke dan Allah da zan mi ki k'arya?"
Usman ma matsowa ya yi yace "Ta fad'a d'in k'arya ne, ko k'aryar ta mi ki ne ba ki aikata ba? To gata nan ki fitar mata jinin dan Allah, wallahi da na gaggauta d'aukar mataki a kan ki, kiji mace kai ki yi laifi kuma ki ce ba za'a mi ki magana ba, ke wace ce?"
Cikin tafasar zuci ta kalle shi tace "Ni ce ma macen? To ta mace maka k'ofar d'aki, kuma na fad'a wallahi ta sake cewa na mata k'arya sai na kife ta da mari kuma a gaban ka."
Ai fa abu ya yi k'amari, sai kawai Usman ya jawo Haseenah da k'arfi ya dawo da ita gaban Khadija yace "Ke fad'a mata ta yi k'arya na ga me za ta yi, kiji iskanci kai ki yi laifi kuma ki ce ba za'a mi ki magana ba, wacece ke da ki ka fi k'arfin a mi ki magana?"
Idon ta ne suka rufe ta kalli Haseenah tace "Ki fad'a idan ke yar halak ce."
Haseenah ta tabbatar babu abin da zai hana Khadija ta dake ta, dan haka ta koma gefen Usman ta na fad'in "Abban Bilal kaga, ni fa ba na son matsala, laifi ne ta aika ta kuma na yafe, dan haka kawai abar..."
Ba ta k'arasa maganar ba Khadija ta kife ta da mari, cikin hargagi ta shak'o wuyan ta tana fad'in "Wa ki ka yafewa? Ni wai ki ke cewa kin yafe wa? To bari ki gani idan na ci uban ki gobe ko kud'i aka baki ba za ki sake shiga harka ta ba."
Tuni Khadija ta yi fatali da ita a k'asa warwas, sosai ta shak'e wuyanta ta na jijjigata ta na fad'in "Za ki sake shiga harka ta, daga yau za ki sake rai na ni?"
Duk abin nan da ake Usman na ta k'ok'arin raba su amma Khadija ta rik'e ta sosai, saida ya sa k'arfi sosai ya rumgumo Khadija ya d'aga ta daga jikin Haseenah, jefar da ita ya yi gefe in da ya kaiwa Haseenah d'auki ya kamota ta tashi, kallonta ya ke duk ta fita hayyacinta ido sunyi waje saboda wahala, ganin haka ne ya sa Usman juyowa cikin b'acin rai ya kashe Khadija da mari, gilashin ta ne ya k'arasa fita ya fad'i, dafe kunci ta yi ta d'ago ta kalle shi, cikin tsananin hushi ya nuna ta da hannu yace "Wallahi yau sai kin tafi gidan ku, ba zan d'auki wannan iskancin ba, haka kawai saboda kifi yarinya k'arfi sai ki dinga mata cin kashin da ki ka ga dama, to ba zai yiwu ba, kawai kije gida sai na nemi ki."
Za ta yi magana Bilal ya sakaya hannun shi ta k'ugun ta ya na kallon Usman da ke rarrashin Haseenah ya nufi d'akin shi da ita, Bilal kam hannun ta ya kama yace "Mummy ki zo mu tafi, mu tafi gidan su Hajia kawai."
Sunkuyawa ya yi ya d'auko mata gilashin ta ya d'aga hannayen shi da nufin saka mata, b'acin rai ne ya saka ta fizgar gilashin ta karya shi gida biyu ta jefar, hanya ta kama da nufin komawa d'akin ta amma sai ta yi karo da kujera, hannun ta Bilal ya kama bai saki ba har saida ya kai ta d'akin ta, su na Bilal ya sake d'auko mata wani gilashin ya saka mata kafin yace "Mummy, meya sa Abba ya daina son ki yanzu?"
Kallon shi kawai ta yi ta mik'e ta d'auko akwatin ta ta zuba kaya, d'akin Bilal ta koma can ma ta had'o mi shi kayan shi kafin ta saka mayafi ta d'auki jakunkunan suka nufi k'ofar fita, a lokacin Haseenah ma sai kuka take ita wallahi gidan su za ta tafi kafin Khadija ta kashe ta, hakan ya sa lokacin da suka iso falon shi suka hangi Khadija da Bilal za su fita, da hanzari ya fito ya tare ta yace "Bilal d'ana ne, kuma ba da shi ki ka zo gidan nan ba, dan haka ki bar min yaro na."
Fuska a had'e tace "Ni ma zan tafi da shi ne saboda ko da na zo gidan tare na same ku."
Zaro ido ta yi dan sai yanzu tasan sark'ar dake wuyanta, murna fa ba'a magana wajen Haseenah ta dangwala sark'ar zinare a wuya, haka su ka fito ta na karairaya kamar ta karye, da kan ta ta zuba mu su abincin dan tuni Bilal ya na islamiyya, Khadija da ta fahimci takunta kamar dariya ma ta bata, dan ga dukkan alama yau ta fara saka sark'a mai tsada, tab'e baki ta yi a ran ta tace "Da alama ba ki san sark'a mai tsada ba ko a ido, dan da kin sani da yanzu kin kashe kan ki da ganin kusan kullum sune a wuya na."
Lafiya lau suka ci abinci su ka kammala, saida ya mik'e zai fita ya kalli Khadija yace "Nagode da alfarmar da ki ka min, sannan ki min message d'in abubuwan da ku ke buk'ata, anjima zan turo Bilyamin ya kawo mu ku."
Ita kam dariya ma ya bata dan haka ta mi shi wani murmushi mai shiga rai tace "Angama ranka shi dad'e."
Ya na fita ta mik'e zata koma d'akin ta, kallon Haseenah ta yi ta na murmushi tace "Sai kuma gashi yau gishiri bai shiga abincinki ba, ko ya akayi haka ta faru oho?"
Kafin ta yi magana ta shige ta barta nan, ta na shiga falon ta ta tura mi shi sak'on abubuwan da suka kusan k'arewa da wanda ma suka k'are, lokacin har Haseenah ta shiga girkin rana aka kawo kayan, Usman ma gida ya dawo cin abinci dan har ga Allah ba ya so ana kai mi shi abinci waje in dai girkin Haseenah, dan ya gama fahimta tafi k'warewa wajen iya dafa shinkafa da jar miya, yamma na yi kuma Khadija ta karb'i girki, ita ma saida ta gama girkin ta lafiyayye sai kawai ta d'auki sukari (sugar) ta zuba a ciki, tsaf ta kawo shi ta jera kamar abun k'warai, sai dai yau a shirye take duk wacce za ayi ayi a gidan, dan ta lura Haseenah ba zaman lafiya take nema da ita ba.
Zaune suke wajen cin abinci Khadija na zuba ma kowa abincin, k'amshin abincin ne ya sa Usman had'iyar yawu har ya riga kowa kaiwa a baki, rufe ido ya yi ya tauna ya kuma had'e, bud'e ido ya yi ya sauke akan Khadija da ke shirin kai loma a bakin ta, shiru ya yi ya na kallon kowa har suka kai bakin su suma, kasa had'ewa su ka yi suka furzar dan haka Khadija ta d'ago ta kalli Haseenah, murmushi ta mata cike da makirci tace "Ramawa ki ka yi kenan?"
Zazzare ido Haseenah ta yi ta kalli Usman da ya kafe ta da ido ya na kallo, cikin in'i'na tace "...
*Maganin biri karen maguzawa, waya fad'a mi ki barno gabas take.*
12/02/2020 à 21:57 - 💋😘💋: 💑💑💑💑💑💑💑💑💑💑
*KALLON KITSE*
_(Ake wa rogo)_
💑💑💑💑💑💑💑💑💑💑
_SAMIRA HAROUNA_
*Litattafan marubuciyar*
*1* _KAUSSAR_
*2* _D'AUKAR FANSA_
*3* _BA SO BANE_
*4* _AUREN HAD'I_
*5* _SANIN MASOYI_
*6* _JIHADI_
*7* _K'ANGIN RAYUWA_
*8* _ITACE K'ADDARARMU_
*9* _KAWU NA NE_
*10* _MAATA_
*11* _KALLON KITSE..._
*SADAUKARWA GA*
_MATAN FARKO_ 🧕🏼 *(UWAYEN GIDA)*
🇸🇦 *ZAMAN AMANA WRITER'S*
_(Gidan zaman lafiya da amana insha Allah)_🤜🤛
```Fatan alkairi masoya```
_Bismillahir rahamanir rahim_
*23*
"Wallahi ba ni bace, babu abin da na saka a abincin nan."
Had'e fuska Khadija ta yi tace "Kinga Haseenah, ni da ke yanzu duk d'aya ne, tunda kin rama to komai ya wuce, kin fahimta."
Cikin b'acin rai Usman yace "Yanzu miye haka? Me ku ke son mayar da ni to? Ke koma miye ai laifin ki ne tunda ke ki ka fara, ki na babba amma ko tsaya d'aukar raini ga k'aramar k'anwar ki, mtssss."
Tsaye ta mik'e ta na kallon shi tace "Dakata Abban Bilal, ni nafi k'arfin na tsaya jawa kai na raini wajen wannan mutsitsiyar yarinyar, gata ka tambaye ta tsakani da Allah uban waye ya fara zuba gishiri ko sugar a abinci? Ita ce da kan ta, har ni za ta wa makirci, saboda ta baka ka kurb'a shine za ta dinga ja min magana a wajen ka ta hanyar lalata abincin da ta girka, me ta ke nufi da hakan? Tasan dole ni za'a zarga dama ba ita ba, shine ni ma na nuna mata mace ce ni kuma gaba na ke da ita ko a haihuwa."
Zata fice ya mik'e tsaye yace "Dawo nan."
Dawowa ta yi ta tsaya sai Haseenah da ta mik'e ta kalle shi tace "Wallahi k'arya ta ke min babu abin da na saka, kawai sharri ne ta ke so ta ja min, taya ma zan lalata abin da na girka da hannu na?"
Kusanta Khadija ta matso cikin b'acin rai ta nuna ta da hannu tace "Wallahi ki ka sake cewa ina mi ki k'arya sai na fitar mi ki da jini a baki, marar kunya kawai fitsararriya, ke har ni za ki kalla ki ce ina mi ki k'arya? Wace ce ke dan Allah da zan mi ki k'arya?"
Usman ma matsowa ya yi yace "Ta fad'a d'in k'arya ne, ko k'aryar ta mi ki ne ba ki aikata ba? To gata nan ki fitar mata jinin dan Allah, wallahi da na gaggauta d'aukar mataki a kan ki, kiji mace kai ki yi laifi kuma ki ce ba za'a mi ki magana ba, ke wace ce?"
Cikin tafasar zuci ta kalle shi tace "Ni ce ma macen? To ta mace maka k'ofar d'aki, kuma na fad'a wallahi ta sake cewa na mata k'arya sai na kife ta da mari kuma a gaban ka."
Ai fa abu ya yi k'amari, sai kawai Usman ya jawo Haseenah da k'arfi ya dawo da ita gaban Khadija yace "Ke fad'a mata ta yi k'arya na ga me za ta yi, kiji iskanci kai ki yi laifi kuma ki ce ba za'a mi ki magana ba, wacece ke da ki ka fi k'arfin a mi ki magana?"
Idon ta ne suka rufe ta kalli Haseenah tace "Ki fad'a idan ke yar halak ce."
Haseenah ta tabbatar babu abin da zai hana Khadija ta dake ta, dan haka ta koma gefen Usman ta na fad'in "Abban Bilal kaga, ni fa ba na son matsala, laifi ne ta aika ta kuma na yafe, dan haka kawai abar..."
Ba ta k'arasa maganar ba Khadija ta kife ta da mari, cikin hargagi ta shak'o wuyan ta tana fad'in "Wa ki ka yafewa? Ni wai ki ke cewa kin yafe wa? To bari ki gani idan na ci uban ki gobe ko kud'i aka baki ba za ki sake shiga harka ta ba."
Tuni Khadija ta yi fatali da ita a k'asa warwas, sosai ta shak'e wuyanta ta na jijjigata ta na fad'in "Za ki sake shiga harka ta, daga yau za ki sake rai na ni?"
Duk abin nan da ake Usman na ta k'ok'arin raba su amma Khadija ta rik'e ta sosai, saida ya sa k'arfi sosai ya rumgumo Khadija ya d'aga ta daga jikin Haseenah, jefar da ita ya yi gefe in da ya kaiwa Haseenah d'auki ya kamota ta tashi, kallonta ya ke duk ta fita hayyacinta ido sunyi waje saboda wahala, ganin haka ne ya sa Usman juyowa cikin b'acin rai ya kashe Khadija da mari, gilashin ta ne ya k'arasa fita ya fad'i, dafe kunci ta yi ta d'ago ta kalle shi, cikin tsananin hushi ya nuna ta da hannu yace "Wallahi yau sai kin tafi gidan ku, ba zan d'auki wannan iskancin ba, haka kawai saboda kifi yarinya k'arfi sai ki dinga mata cin kashin da ki ka ga dama, to ba zai yiwu ba, kawai kije gida sai na nemi ki."
Za ta yi magana Bilal ya sakaya hannun shi ta k'ugun ta ya na kallon Usman da ke rarrashin Haseenah ya nufi d'akin shi da ita, Bilal kam hannun ta ya kama yace "Mummy ki zo mu tafi, mu tafi gidan su Hajia kawai."
Sunkuyawa ya yi ya d'auko mata gilashin ta ya d'aga hannayen shi da nufin saka mata, b'acin rai ne ya saka ta fizgar gilashin ta karya shi gida biyu ta jefar, hanya ta kama da nufin komawa d'akin ta amma sai ta yi karo da kujera, hannun ta Bilal ya kama bai saki ba har saida ya kai ta d'akin ta, su na Bilal ya sake d'auko mata wani gilashin ya saka mata kafin yace "Mummy, meya sa Abba ya daina son ki yanzu?"
Kallon shi kawai ta yi ta mik'e ta d'auko akwatin ta ta zuba kaya, d'akin Bilal ta koma can ma ta had'o mi shi kayan shi kafin ta saka mayafi ta d'auki jakunkunan suka nufi k'ofar fita, a lokacin Haseenah ma sai kuka take ita wallahi gidan su za ta tafi kafin Khadija ta kashe ta, hakan ya sa lokacin da suka iso falon shi suka hangi Khadija da Bilal za su fita, da hanzari ya fito ya tare ta yace "Bilal d'ana ne, kuma ba da shi ki ka zo gidan nan ba, dan haka ki bar min yaro na."
Fuska a had'e tace "Ni ma zan tafi da shi ne saboda ko da na zo gidan tare na same ku."