← Book details Kallon Kitse Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 72 OF 86

Sashe 72

Kallon Kitse Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

A kwana biyu zuwa lokacin da aka kammala sabgar bikin Nura Usman ya shiga taitayin shi, dan ko wayar shi Khadija ba ta d'auka bare ta saurare shi idan ya zo, hakan ya tab'a shi sosai dan ya damu, haka ma Haseenah ta fara damuwa sosai akan lamarin na shi, dan har yanzu ba su kwana d'aki d'aya ba, gari na wayewa kuma zai buga sammako yaje gida ya na lallab'ar malam ya je ya dawo da Khadija, sam ba ya da lokacin wata Haseenah yanzun, abinci ma idan ta dafa sai dai ta ci ita kad'ai amma ban da shi, ba ya son zuwa gidan saboda ba ya son ganin Haseenah da idon shi, ya na iya k'ok'arin shi sosai wajen b'oye k'iyayyar da yake mata, ya rasa dalilin da ya sa ya ke sake jin tsanar ta a kullum idan ya ganta, ba ya son jin muryar ta ko ganin giftawarta a gidan, duk da ba ya da kokwanto akan cikin da ke jikin ta cewa na shi ne amma dai ba ya jin ya na k'aunar abin da ke cikin ta kamar yanda ya ke k'aunar wanda ke cikin Khadija, a haka har aka kwashe *sati biyu* babu abin da ya sauya.

A sati biyun nan ne Usman ya yi tattaki har k'auyen su Baba Garba mai gadi ya je ya bashi hak'uri akan abin da ya farusannan ya nemi da ya dawo bakin aikin shi, ya hak'ura ya kuma nuna masa komai ya wuce shi dama bai rik'e ba saboda ya san ba laifin shi bane, amma dai ba zai iya komawa aiki ba saboda jiki da jini, amma idan ya amince akwai d'an shi da ke neman kangarewa zai iya had'a shi da shi saiya zauna a mazaunin shi, ya amince ya taho da yaron mai sunan *Rabe*, tabbas ya fara aiki yanda ya kamata sai dai burin Usman akan yaron ba wai ya zama mai kula da pliwoyin (flawers) gidan shi bane da k'ofa, ya na so a gama wannan zagon na karatu sannan ya d'ora shi ya ci gaba da karatun shi tunda ya na yi ya dakatar saboda shirme, duk da haka kuma Usman bai daina bibiyar Khadija ba, yanzu haka har ya gaji da sawa Bilal na rok'on ta akan ta dawo, Hajia da malam dama sun ce ba ruwan su, a k'arshe ya samu da k'yar ya lallab'a Murtala ya je ya mata magana, nuna masa ta yi ba komai za ta koma, amma ya na barin gidan tace ba yanzu sai ya sake shiga hankalin sa, jin shiru shiru ya sa saida ta kai ga Usman ya turo Nura da Kabir da kuma Mannir su ka je bata hak'uri, sai lokacin Mama tasan da irin tsiyar da Khadija ke tsulawa, dan sam babu wanda ya tab'a ce mata ya zo bata hak'uri dan ta koma, Usman kuma idan ya zo ta kan basu wuri ne dan su tattauna, kuma ba ta nuna mata wasu alamu na rashin jituwa, hakan ya sa ba ta san me ke faruwa ba, shi ma Usman ya so ya b'oye mata ne dan yasan za ta iya tirsasata akan ta dawo, duk da ya na matuk'ar so ta koma amma ya fi so ta koma dan ganin damar ta, kuma har yau ba ya ganin laifin ta akan hukuncin da take masa, dan kuwa babu abin da ta rage shi da shi a rayuwa amma ya mata kishiya, sannan ya rasa meya shiga kan shi da ya dinga cin mutuncin ta, dan wasu abubuwan sai yanzu ne idan ya na rarrashin ta take iya fad'a mi shi irin abin da ya mata, bugu da k'ari kuma bata gama hucewa ba ya zo ya bugar mata baki har saida ya kumbura, wanda kullum mitar hakan take masa, nan Mama tace su koma Khadija za ta dawo gidan ta ba jimawa, sun tafi da farin cikin samun nasara amma sam Khadija tace ba yanzu zata koma ba, da Mama ta fara fad'a kuma sai 'yan biyar suka tausheta suka ce tunda ba yarinya ba ce kawai a rabu da ita, hakan ya sa a ranar Usman ke ta zuba idon ganin Dije amma shiru, ko bacci baiyi ba a ranar ya na sak'awa ya na warwarewa, washe gari da dare ya je gidan da kan sa, a falo ya samu duk 'yan biyar d'in da wasu daga cikin yaransu, Mama na d'aki hakan ne ya sa ya zauna suka gaisa sosai, Naseer ne yace "Auta kam ta na ciki, amma kafin ka shiga ciki ka kawo kud'in ganin ta."

"To in dai hakane me zai hana ka fad'a min gaba d'aya farashin da zan biya, kaga sai ka d'auke ta da kan ka ka kai min ita gida na." Cewar Usman cikin raha, dariya su ka yi sai Habeeb ne yace "K'anwa ta fa tsada ne da ita, farashin ta baya fad'uwa."

Cikin zolaya yace "To kunga, duk cikin kun nan naga babu wanda zai iya taimaka min, dan haka ni zanje na yi yak'i na ni kad'ai, in har k'anwar ku bata koma gida na zuwa gobe ba to ku canza min suna."

Cike da cika baki ya mik'e zai nufi d'akin Khadija Naseer ya bushe da dariya yace "Wane sunan za mu saka ma ka to?"

Juyowa ya yi ya harare shi yace "Ka zab'a da kan ka mana."

Bashir ne ya yi saurin cewa " sai mu saka mi shi *Mani*."

Komai baice ba ya wuce d'akin, ko sallama baiyi ba yau dan al'amarin ba sauk'i, kuma cikin sa'a saiya samu Khadija tana ban d'aki, murmushi ya yi kafin ya cire hular kan shi ya aje gefe ya kwanta kan gadon ya yi d'a-id'ai, kusan minti biyu ya d'auka kafin Khadija ta fito daga ciki d'aure da k'irji, kasancewar cikin ta ya sa ya d'age sosai daga sama har ya kan iya hango cinyoyinta, ita kam gilashin ta ne take gogewa ta na k'ok'arin sakawa, ta na sawa ta ja ta tsaya da tsoro fal a idon ta, bud'ar bakin ta cewa ta yi "A'uzu billahi mina shaid'anir-rajim, innahu min Suleimana wa innahu bismillahir-rahamanir-rahim."

Ba tare da damuwa ba Usman yace "A kan ki, wato na ma zama shaid'an ko?"

Wata ajiyar zuciya ta sauke ta matso kusan shi tace "...

*Ina k'aunar ku.*
06/03/2020 à 12:54 - 💋😘💋: 💑💑💑💑💑💑💑💑💑💑
*KALLON KITSE*
_(Ake wa rogo)_
💑💑💑💑💑💑💑💑💑💑

_SAMIRA HAROUNA_

*Litattafan marubuciyar*

*1* _KAUSSAR_
*2* _D'AUKAR FANSA_
*3* _BA SO BANE_
*4* _AUREN HAD'I_
*5* _SANIN MASOYI_
*6* _JIHADI_
*7* _K'ANGIN RAYUWA_
*8* _ITACE K'ADDARARMU_
*9* _KAWU NA NE_
*10* _MAATA_
*11* _KALLON KITSE..._

*SADAUKARWA GA*

_MATAN FARKO_ 🧕🏼 *(UWAYEN GIDA)*

🇸🇦 *ZAMAN AMANA WRITER'S*
_(Gidan zaman lafiya da amana insha Allah)_🤜🤛

```Fatan alkairi masoya```

_Bismillahir rahamanir rahim_

*36*

"Malam lafiyar shigo min d'aki haka kawai, wa ma ya baka izinin shigowa nan?"

Kamar ba dashi take magana ba ma saiya share ta, ta jima tsaye ta na kallon shi ganin bai damu da tsiyar da take ba ya sa ta juya ta isa gaban madubi ta fara shafe shafe kamar yanda ta saba, lokaci lokaci takan juyo ta kalle shi amma abun mamaki shi kuma hankalin na ga waya ya na dannawa, saida ta gama ta nufi wajen kaya ta d'auko riga, ba tare da ta cire d'aurin k'irjin ba ta saka wando da rigar nono kafin ta saka doguwar rigar, juyowa ta yi ta kalle shi tace "To malam, idan ka gama da d'akin sai ka rufe min ko, ni zan fita."

Gyale ta d'auka ta fesa turare ta juya zata fice, da sauri ya duro daga kan gadon yace "Ina za ki je?"

Ta na kallon idon shi tace "Bak'o..." Sai kuma ta yi shiru saboda tuna ranar da ya kwamtse mata baki, rik'e k'ugu ta yi tace "Ka ban hanya mana zan wuce."

Rumgumo ta ya yi jikin shi ya dawo da ita ya zaunar akan gado, ture shi ta yi tace "Malam ka daina tab'a ni mana."

Sosai ya kalle ta yace "Khadija, har yanzu fa ni mijin ki ne, a labarin da ki ka bani ba ni ne na kore ki ba, amma Khadija ki na hukuntani abisa laifin da na ke tunanin ko da na aikata shi ne dadangan za ki yafe min, me ya sa haka Khadija? Kin daina so na ne yanzu? Ko kuma ba kya son ki tsufa a gida na ne yanzu kamar yanda ki ke fad'a min."

Mik'ewa ta yi tsaye tace "Ni dai kawai ka fitar min daga d'aki, so ka ke mutane su d'auka wani abun ne ke faruwa anan? Dan Allah ka tashi ka fita."

Yau fa ya yi niyyar ba zai bar gidan nan ba babu wani sakamako mai kyau, dan haka ya haye gadon ya gyara kwanciya ya kalle ta yace "Ba zan fita d'in ba, idan kuma ki na ganin za ki saka k'artin 'yan uwan ki ne su fitar da ni to bismillah."

Mamaki ne ya sa ta zaro ido tace "Abban Bilal, yan uwan nawa ne ma k'arti? To ai ko ba k'artin banza bane tunda su na ciyar da duka girman gidan nan dama wasu dake kewayen shi."

Hararan ta ya yi yace "Ni kuma na gaza ko? To ki jaraba kiran su ki gani mana idan za su iya."

Rumgume hannaye ta yi tace "Amma dai kasan tsaf zan iya saka su kefa min kai cikin kwalbatin unguwar nan ko?"

Wata irin dariya ya bushe da ita yace "To ki kira su mana, na fad'a mi ki ina tsoro ne."

Fitowa kam ta yi daga d'akin amma abun mamaki ba kowa a falon har telebijin ma an kashe, mayar da d'akin ta yi ta rufe ta dawo ta zauna kan kujerar da ke gaban madubi, kallon ta ya yi yace "Hajia ko za ki iya samo min kayan bacci a gidan nan?"

A harzuk'e ta kalle shi tace "A ina zan samo ma ka kayan bacci? Na wa zan d'auko ma ka?"

Har ta yi shiru shi kuma ya fara dariya sai kuma ta kalle shi tace "Wai ma tsaya, idan na d'auko ma ka kayan baccin me za ka yi da su?"
Chapter 72 · 0% Book details