Sashe 75
Kallon Kitse Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Wannan addu'a fa bana bari ta wuce ba ni kai na, dan haka na amsa da *ameen*, Bilal ya je gidan su Abdallah da babu nisa sosai da nan d'in, sunyi farin cikin ganin juna dan sun jima basu had'u ba, amm bai yarda ya jima ba ya mu su sallama ya juyo ya dawo, *tsautsayi fa ance idan ya wuni baya kwana*, rabon ayi Bilal su ka had'e shi da wani mai mota a lokacin da zai shigo kwana, mutanen dake wajen ne da su ka ankara wasu kuma akayi gaban idon su ya sa suka rabka salati tare da sallalami, tuni aka rufe wajen ana jimami tare da taimakawa Bilal da tuni baisan in da kan shi yake ba, a daidai lokacin motar Usman ta shigo layin, dan gaba d'aya hankalin shi ya kasa kwanciya, yanzun ma ya taho ne da nufi ya d'auke shi ya tafi da shi duk in da ya saka k'afar shi, ganin wannan taro yasan had'ari ne dan haka ya tsaya tunda dai a unguwar su ne abun ya faru, tashin hankali da ba'a saka mi shi rana, sai ga Usman ya ga Bilal hannun mutumin da ya bige shi jina-jina kamar babu rai a tare da shi, kallon shi ya kai kan moton shi daya wargaje abinka da dama roba tafi yawa a jiki, wani irin duka ne gaban shi ya fara yi yayin da zuciyar shi kamar za ta fito, a hankali ya ke kutsowa cikin mutanen wanda ke ta hayaniya kowa da abin da yake fad'a, wasu na fad'in sun san shi za su je su fad'a a gidan su, in da wasu suka dakatar da su da cewa kar aje babu namiji a gidan mata ba lallai su rik'e kan su ba idan su ka ji irin wannan labarin, hannu Usman ya zura ya karb'o Bilal daga hannun mutumin da ke kallon shi da mamaki, yana amsar shi wayar Bilal ta fad'o daga aljihun shi ta fad'i k'asa, d'aya daga cikin mutanen wurin ne yace "Mahaifin shi ne."
Motar shi mutumin ya bud'e da nufin a saka Bilal ciki amma sai Usman ya nufi tashi motar da shi, amma daga ganin yanda ya ke takawa jikin shi sai b'ari yake haka ma hannayen shi, dan yanda ya ke kallon Bilal baya jin zaiyi rai, sosai jikin shi ke rawa har ya na neman fad'uwa da Bilal d'in, da sauri wani mutum da shi ma anan unguwar yake ya karb'e shi a hannun shi ya na fad'in "Ayi hak'uri Alhaji, ayi hak'uri, insha Allahu zai tashi."
Zagayawa mutumin ya yi ya kwantar da Bilal sai Usman da ya shiga ya tayar da mota, wanda ya bige shi ne ya bi bayan shi har suka isa asibitin da tafi kusa da su, amma ganin halin da Bilal ke ciki ya sa suka tura su babban gida (Hôpital), nan aka karb'e shi da taimakon ubangiji aka bashi taimakon daya dace.
Usman na zaune akan wani banci amma da simitin aka yi shi ya na tunani, shin dama Haseenah na da burin kashe ma sa d'an sa ne kome? Yanzu taya zan fara fad'awa Khadija maganar nan? Sai ta ga kamar da ni aka had'a baki ma aka cutar da shi, wata zuciyar ce tace mi shi, haba dai, ba ma za ta yi tunanin haka ba, nauyayyar ajiyar zuciyar da ya sauke ce ta sa wanda ya bankr Bilal d'in kallon shi, dafa kafad'ar shi ya yi yace "Dan Allah ka yi hak'uri, abun ya faru ne a bazata, bansan..."
Kallon shi ya yi yace "Ba komai malam, tsautsayi ne da baya wuce ranar shi, nima ina da abin hawan nan, kuma hakan na faruwa sosai."
Jinjina kai ya yi yace "Allah ya tashi kafad'un shi."
Da k'yar Usman ya iya cewa "Ameen." Likita ne ya fito daga d'akin ya na cire abin da ke rufe a hanci shi, hannu ya ba Usman da ya mik'e yace "Mu gode Allah, ya na samun lafiya in Allah ya yarda, ya na bacci yanzu."
Sanyayyar ajiyar zuciya ya sauke yace "Alhamdulillah, nagode sosai likita, Allah ya saka da alkairi."
"Ba komai." Cewar likitan ya na shirin shiga ofishinshi, Usman d'in ne yace "Likita za mu iya ganin shi kuwa?"
Juyowa ya yi yace "Eh, za ku iya." Da sauri Usman ya nufi d'akin, Bilal ne kad'ai a ciki kwance jiki duk bandeji, k'arasawa su ka yi kusan shi suna kallon yanda Allah ya canza hallitar shi cikin k'ank'anin lokaci, mutumin ne ya mi shi sallama tare da cewa saiya dawo, ya na tafiya ya kira malam ya fad'a mi shi, zuwa bayan sallah azahar d'akin da Bilal ke ciki ya cika da yan uwa, sai dai wajen su Khadija har yanzu ba su san me ke faruwa ba, duk suna zaune jugum har yanzu Bilal bai farka ba wayar Usman ta shiga kururuwa, cikin sanyin jiki ya fito da ita ya duba, take gaban shi ya tsinke ya fad'i saboda ganin sunan *uwar yarima*, kallon Hajia ya yi da ke fuskantar shi, har wayar ta tsinke bai d'aga ba saida tace "Ka d'auka mana, wa ya ke kira ne?"
Cike da damuwa yace "Khadija ce." Malam ne yace "Ka d'auka mana sai ka fad'a mata wani abun, inyaso sai kaje gidan ka fad'a musu a nutse."
Khadija da ke tare da k'anwar Mama da kuma Kaltume zaune kasa hak'ura ta yi ta sake aika wani kiran, dan gabanta ne taji ya tsananta fad'uwa haka kawai, ta kira Bilal kuma ba ta samu ba shi ya sa ta kira Abban shi, d'auka ya yi cike da son b'oye halin da ake ciki yace "Uwar yarima ya ake ciki? Har kinyi kewata ko?"
Hajia dake kallon shi mik'ewa ta yi ta fita saboda kunya, inda Khadija ta amsa da "Na yi kewar ka mana, kai fa?"
"Kema kinsan na yu kewar ai, yanzu fad'a min kin shirya ne na zo na d'auke ki?"
Dariya ta yi tace "Haba dai, da rana haka patsal-patsal, ai ko zan shigo saida dare."
"Kamar wata marar gaskiya, to me ya sa?"
"Saboda lokacin da za'a kaini gidan ma da daddare aka kai ni, dan haka yanzu ma sai da dare zan koma."
Murmushi ya yi yace "To da da d'in da yanzu d'aya ne? A lokacin fa kina sabuwa ne fil a leda, yanzu kuma na bi ta ciki na fito, sannan Bilal ya fito ta nan ga kuma k'annan shi ma na shirin fitowa."
Duk da ya sassauta murya saida Hassana taji me ya fad'a, kallon shi ta yi ta kuma sunne kanta k'asa ta rufe baki cike da kunya, Khadija kam cewa ta yi "Matsala ta da kai fa kenan, yanzu dai ba wannan ba, ina yaro na yake? Ina kiran shi amma ba a samu."
Wani tsam yaji a jikin shi kafin ya daure yace "Bilal ya d'an fita tare da Murtala, mu na shago ne, watak'ila cajin wayar ne ya k'are, amma zan..." Kasa k'arasawa ya yi saboda rawar da muryar shi ke yi, da k'yar yace "Zan kira ki saina baki shi."
Ba tare da damuwa ba tace "Shikenan sai na jika, sai anjima."
Cike da zolaya yace "Au! dama muryar d'an ki kawai ki ka kira kiji? To ya yi kyau."
Dariya ta yi tace "To meye a muryar ta ka da za ta dame ni? Bayan anjima kad'an za mu kasance tare da kai."
Da haka sukayi sallama bai nuna mata komai ba, sai lokacin ne malam yace ya kamata su san halin da ake ciki, fita ya yi da niyyar zaije ya samu Ashir ya fad'a masa, hakan kuwa akayi dan ba jimawa ya isa in da Ashir ke harkokinshi, bayan sun gaisa ne ya fad'a masa abin da ke faruwa, ya jinjina al'amarin tare da tashin hankali, amma sai Usman yace "Idan dai har kai za ka d'aga hankalin ka to ya mahaifiyar shi kenan? Na zab'i na fad'a ma ka saboda ka san ta hanyr d za ka kwantar mata da hankali."
Shiru Ashir yayi kafin daga bisani yace "Hakane Usee, insha Allahu zan fad'a mata yanda za ta fahimta, kar ka damu."
Hannu ya bashi su ka yi sallama yace zai wuce gida ne, shi ma Ashir d'in gidan ya nufa daga nan dan fad'a musu, Mama ya fara fad'a ma tasan halin da ake ciki, ita kanta Mama da k'yar ta iya fad'awa Khadija, cikin tashin hankali tace Ashir ya kaita asibitin taga d'an ta, a hanya ma kuka take ta na fad'in kawai laifinta ne da ta yarda ta bashi yaron, Mama ce ta dinga tausarta da kalamai masu kwantar da hankali da k'arfafa gwiwa, suna isa asibitin aka nuna musu d'akin, da sallama su ka shiga amma Khadija na ganin Bilal kamar ba shi ba sai ta yi shiru, da k'yar ta isa ga gadon ta zauna ta na shafa fuskar shi, hawayen da suka taho mata ne ya sa malam cewa "A'a Khadija dan Allah, kar ki masa kuka mana, k'addara ce da kuma tsautsayi, ki masa addu'a Allah ya tashi kafad'un shi."
Hassana ce ta yi tsaye kanta tana shafa bayan ta tana bata hak'uri ita ma, sun jima a haka kafin ta kalli Nura tace "Har yanzu bai farka ba?"
Cikin sanyin jiki yace "Bai farka ba har yanzu, amma dai likitan yace an masa allura ne."
Cikin zubo da wasu hawayen tace "Ko dai ya mutu ne? Dan Allah ku fad'a min idan ya mutu, wallahi zan d'auki dangana."
Hajia ce tace "Haba Khadija, idan ya mutu za mu saka shi gaba ne haka, da ran shi mana gashi ma ya na numfashi."
Haka suka zauna jugum sai wasu dake tafiya wasu na zuwa, sai yamma kad'ai Bilal ya farka idon shi har sun kumbura, bud'ar bakin shi da "Mummy, Mummy." Ya fara, dama ta na kusa kam ta rik'o hannun shi tace "Gani nan Bilal, bud'a idon ka."
Bud'a ido ya yi ya kalle ta sosai, hawaye ne suka taho mi shi yace "Mummy ina Abba na?"
Saida ta mayar da na ta hawayen tace "Ya tafi gida yanzu zai dawo."
Motar shi mutumin ya bud'e da nufin a saka Bilal ciki amma sai Usman ya nufi tashi motar da shi, amma daga ganin yanda ya ke takawa jikin shi sai b'ari yake haka ma hannayen shi, dan yanda ya ke kallon Bilal baya jin zaiyi rai, sosai jikin shi ke rawa har ya na neman fad'uwa da Bilal d'in, da sauri wani mutum da shi ma anan unguwar yake ya karb'e shi a hannun shi ya na fad'in "Ayi hak'uri Alhaji, ayi hak'uri, insha Allahu zai tashi."
Zagayawa mutumin ya yi ya kwantar da Bilal sai Usman da ya shiga ya tayar da mota, wanda ya bige shi ne ya bi bayan shi har suka isa asibitin da tafi kusa da su, amma ganin halin da Bilal ke ciki ya sa suka tura su babban gida (Hôpital), nan aka karb'e shi da taimakon ubangiji aka bashi taimakon daya dace.
Usman na zaune akan wani banci amma da simitin aka yi shi ya na tunani, shin dama Haseenah na da burin kashe ma sa d'an sa ne kome? Yanzu taya zan fara fad'awa Khadija maganar nan? Sai ta ga kamar da ni aka had'a baki ma aka cutar da shi, wata zuciyar ce tace mi shi, haba dai, ba ma za ta yi tunanin haka ba, nauyayyar ajiyar zuciyar da ya sauke ce ta sa wanda ya bankr Bilal d'in kallon shi, dafa kafad'ar shi ya yi yace "Dan Allah ka yi hak'uri, abun ya faru ne a bazata, bansan..."
Kallon shi ya yi yace "Ba komai malam, tsautsayi ne da baya wuce ranar shi, nima ina da abin hawan nan, kuma hakan na faruwa sosai."
Jinjina kai ya yi yace "Allah ya tashi kafad'un shi."
Da k'yar Usman ya iya cewa "Ameen." Likita ne ya fito daga d'akin ya na cire abin da ke rufe a hanci shi, hannu ya ba Usman da ya mik'e yace "Mu gode Allah, ya na samun lafiya in Allah ya yarda, ya na bacci yanzu."
Sanyayyar ajiyar zuciya ya sauke yace "Alhamdulillah, nagode sosai likita, Allah ya saka da alkairi."
"Ba komai." Cewar likitan ya na shirin shiga ofishinshi, Usman d'in ne yace "Likita za mu iya ganin shi kuwa?"
Juyowa ya yi yace "Eh, za ku iya." Da sauri Usman ya nufi d'akin, Bilal ne kad'ai a ciki kwance jiki duk bandeji, k'arasawa su ka yi kusan shi suna kallon yanda Allah ya canza hallitar shi cikin k'ank'anin lokaci, mutumin ne ya mi shi sallama tare da cewa saiya dawo, ya na tafiya ya kira malam ya fad'a mi shi, zuwa bayan sallah azahar d'akin da Bilal ke ciki ya cika da yan uwa, sai dai wajen su Khadija har yanzu ba su san me ke faruwa ba, duk suna zaune jugum har yanzu Bilal bai farka ba wayar Usman ta shiga kururuwa, cikin sanyin jiki ya fito da ita ya duba, take gaban shi ya tsinke ya fad'i saboda ganin sunan *uwar yarima*, kallon Hajia ya yi da ke fuskantar shi, har wayar ta tsinke bai d'aga ba saida tace "Ka d'auka mana, wa ya ke kira ne?"
Cike da damuwa yace "Khadija ce." Malam ne yace "Ka d'auka mana sai ka fad'a mata wani abun, inyaso sai kaje gidan ka fad'a musu a nutse."
Khadija da ke tare da k'anwar Mama da kuma Kaltume zaune kasa hak'ura ta yi ta sake aika wani kiran, dan gabanta ne taji ya tsananta fad'uwa haka kawai, ta kira Bilal kuma ba ta samu ba shi ya sa ta kira Abban shi, d'auka ya yi cike da son b'oye halin da ake ciki yace "Uwar yarima ya ake ciki? Har kinyi kewata ko?"
Hajia dake kallon shi mik'ewa ta yi ta fita saboda kunya, inda Khadija ta amsa da "Na yi kewar ka mana, kai fa?"
"Kema kinsan na yu kewar ai, yanzu fad'a min kin shirya ne na zo na d'auke ki?"
Dariya ta yi tace "Haba dai, da rana haka patsal-patsal, ai ko zan shigo saida dare."
"Kamar wata marar gaskiya, to me ya sa?"
"Saboda lokacin da za'a kaini gidan ma da daddare aka kai ni, dan haka yanzu ma sai da dare zan koma."
Murmushi ya yi yace "To da da d'in da yanzu d'aya ne? A lokacin fa kina sabuwa ne fil a leda, yanzu kuma na bi ta ciki na fito, sannan Bilal ya fito ta nan ga kuma k'annan shi ma na shirin fitowa."
Duk da ya sassauta murya saida Hassana taji me ya fad'a, kallon shi ta yi ta kuma sunne kanta k'asa ta rufe baki cike da kunya, Khadija kam cewa ta yi "Matsala ta da kai fa kenan, yanzu dai ba wannan ba, ina yaro na yake? Ina kiran shi amma ba a samu."
Wani tsam yaji a jikin shi kafin ya daure yace "Bilal ya d'an fita tare da Murtala, mu na shago ne, watak'ila cajin wayar ne ya k'are, amma zan..." Kasa k'arasawa ya yi saboda rawar da muryar shi ke yi, da k'yar yace "Zan kira ki saina baki shi."
Ba tare da damuwa ba tace "Shikenan sai na jika, sai anjima."
Cike da zolaya yace "Au! dama muryar d'an ki kawai ki ka kira kiji? To ya yi kyau."
Dariya ta yi tace "To meye a muryar ta ka da za ta dame ni? Bayan anjima kad'an za mu kasance tare da kai."
Da haka sukayi sallama bai nuna mata komai ba, sai lokacin ne malam yace ya kamata su san halin da ake ciki, fita ya yi da niyyar zaije ya samu Ashir ya fad'a masa, hakan kuwa akayi dan ba jimawa ya isa in da Ashir ke harkokinshi, bayan sun gaisa ne ya fad'a masa abin da ke faruwa, ya jinjina al'amarin tare da tashin hankali, amma sai Usman yace "Idan dai har kai za ka d'aga hankalin ka to ya mahaifiyar shi kenan? Na zab'i na fad'a ma ka saboda ka san ta hanyr d za ka kwantar mata da hankali."
Shiru Ashir yayi kafin daga bisani yace "Hakane Usee, insha Allahu zan fad'a mata yanda za ta fahimta, kar ka damu."
Hannu ya bashi su ka yi sallama yace zai wuce gida ne, shi ma Ashir d'in gidan ya nufa daga nan dan fad'a musu, Mama ya fara fad'a ma tasan halin da ake ciki, ita kanta Mama da k'yar ta iya fad'awa Khadija, cikin tashin hankali tace Ashir ya kaita asibitin taga d'an ta, a hanya ma kuka take ta na fad'in kawai laifinta ne da ta yarda ta bashi yaron, Mama ce ta dinga tausarta da kalamai masu kwantar da hankali da k'arfafa gwiwa, suna isa asibitin aka nuna musu d'akin, da sallama su ka shiga amma Khadija na ganin Bilal kamar ba shi ba sai ta yi shiru, da k'yar ta isa ga gadon ta zauna ta na shafa fuskar shi, hawayen da suka taho mata ne ya sa malam cewa "A'a Khadija dan Allah, kar ki masa kuka mana, k'addara ce da kuma tsautsayi, ki masa addu'a Allah ya tashi kafad'un shi."
Hassana ce ta yi tsaye kanta tana shafa bayan ta tana bata hak'uri ita ma, sun jima a haka kafin ta kalli Nura tace "Har yanzu bai farka ba?"
Cikin sanyin jiki yace "Bai farka ba har yanzu, amma dai likitan yace an masa allura ne."
Cikin zubo da wasu hawayen tace "Ko dai ya mutu ne? Dan Allah ku fad'a min idan ya mutu, wallahi zan d'auki dangana."
Hajia ce tace "Haba Khadija, idan ya mutu za mu saka shi gaba ne haka, da ran shi mana gashi ma ya na numfashi."
Haka suka zauna jugum sai wasu dake tafiya wasu na zuwa, sai yamma kad'ai Bilal ya farka idon shi har sun kumbura, bud'ar bakin shi da "Mummy, Mummy." Ya fara, dama ta na kusa kam ta rik'o hannun shi tace "Gani nan Bilal, bud'a idon ka."
Bud'a ido ya yi ya kalle ta sosai, hawaye ne suka taho mi shi yace "Mummy ina Abba na?"
Saida ta mayar da na ta hawayen tace "Ya tafi gida yanzu zai dawo."