Sashe 8
Kallon Kitse Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Da sauri ya rik'o hannun ta ya mayar da ita gaban madubi ya bud'a ya d'auko wani k'aramin akwatin gilashi yace "Ki saka wannan ya na miki kyau."
Da kan shi ya saka mata kafin suka wuce, Haseenah kuma kamar zuciyar ta za ta harba saboda bak'in kishi na banza da wofi, haka su ka zauna tare da Bilal a faranti d'aya su ka saka hannu dukan su, sai dai Khadija da Haseenah ba sosai su ke cin abincin ba, dan kowa da abin da ke ran shi, haka dai su ka gama ango ya shirya ya fita, amarya ta koma b'angaren ta.
*Yau* ma dai sosai aka gwangwaje walimar damu, mutane sun sha anko gwanin ban sha'awa, haka aka yi abin da ya tara mutane sai dai sisin kwabo ko k'wayar gero Usman bai karb'a ba a hannun iyayen Haseenah, daga k'arshe dai tsofaffi da iyaye sun sake had'a kan Khadija da Haseenah sun mu su nasiha da jan kunne tare da gargad'i, a k'arshe kuma su ka bisu da addu'ar fatan zaman lafiya da kuma zuri'a mai albarka, haka yau ma taro ya watse in da kowa ya koma gefe dan a kalli kalar na su zaman, da dare ma Usman ya shigo tare da manyan aminan shi Alhaji *Murtala* da Alhaji *Adamu* mijin Salamatu, suma dai nasihar su ka sake mu su tare da fatan alkairi daga bisani su ka tafi.
*Allah ya bada hak'urin zama da juna.*
05/01/2020 à 22:11 - 💋😘💋: 💑💑💑💑💑💑💑💑💑💑
*KALLON KITSE*
_(Ake wa rogo)_
💑💑💑💑💑💑💑💑💑💑
_SAMIRA HAROUNA_
*Littatafan marubuciyar*
*1* _KAUSSAR_
*2* _D'AUKAR FANSA_
*3* _BA SO BANE_
*4* _AUREN HAD'I_
*5* _SANIN MASOYI_
*6* _JIHADI_
*7* _K'ANGIN RAYUWA_
*8* _ITACE K'ADDARARMU_
*9* _KAWU NA NE_
*10* _MAATA_
*11* _KALLON KITSE..._
*SADAUKARWA GA*
_MATAN FARKO_🧕🏼 *(UWAYEN GIDA)*
🇸🇦 *ZAMAN AMANA WRITER'S*
_(Gidan zaman lafiya da amana insha Allah)_🤜🤛
```Fatan alkairi masoya```
_Bismillahir rahamanir rahim_
*7*
Kasancewar Bilal zai koma makaranta yau ya sa Khadija ta shi da wuri ta nufi madafa dan shirya abin kari, (albarkacin kaza k'adangare kan sha ruwan kasko), tun da ta tunkari k'ofar ta gan ta bud'e ta ke mamakin yanda k'ofar ke bud'e, da wannan mamaki ta k'arasa shiga, turus ta ja ta tsaya ganin oga malam yallab'ai kuma alhaji Usman ya d'auki k'atuwar tasa daga kan gas ya na juye tafasashen ruwan da ya dafa a k'aramin bokiti, da sauri ta k'arasa ta na fad'in "Abban Bilal, me ka ke yi haka?"
Wani abu ya ji tare da kunya dan baiso ya ganta ba ko ita ta gan shi, d'agowa ya yi bayan ya juye ruwan ya na d'an had'e fuska yace "Um, wallahi, wai wanna ce, ina jin dai, kamar dai ba ta cika wanka da ruwan sanyi bane da safe, to shine na..."
Katse shi ta yi da cewa "Uhum! Na gane ma, ka kai mata to kafin su huce."
D'auka ya yi cike da kunya ya fice, sai da ya b'ace ma ganin ta taji hawaye sun cika idon ta, cire gilashin ta ta yi ta share k'wallan, ji ta yi ma ba za ta iya komai ba dan haka ta juyo ta fito, ta na zuwa falon ta taga abin mamaki, da sauri ta saki murmushi tace "Wa na ke gani kamar Uwani?"
Da dariya matashiyar yarinyar tace "Ni da kai na Maman Bilal."
"Uwani yaushe ki ka dawo? Sai kawai na gan ki haka kamar aljana."
Dariya Uwani ke yi har tace "Jiya na shigo da magriba, shi ya sa ma ban zo tun jiya ba."
"Kai, amma ko na ji dad'in zuwan nan na ki, dan yanzu haka da ki ka ganni wallahi na gaji ne, har na shiga madafar kuma na fito da d'aki ne zan koma ba kwanta kuma sai gaki."
Da karsashi Uwani ta mik'e tace "Maman Bilal ba ki da matsala tun da na dawo, yanzu fad'i me za'a dafa sai na shiga da kai na."
"A'a ba za ayi haka ba, ai ganin ki karsashi ya k'ara min, kawai muje tare sai mu d'ora, kinga ma daga nan sai ki bani labarin abinda ya tsayar da ke."
Dariya ta yi su ka nufi madafar, aiki suke su na hira ta na fad'a mata abin da ya tsayar da ita, da haka su ka kusan kammalawa Khadija ta sakar mata aikin ta tafi d'aki dan yin wanka.
Da taimakon Usman Haseenah ta shirya kan ta sai shefiyar shagwab'a take zuba mi shi, shi kam yau ya na jin ya samu sabuwar hanya sai wani biye mata ya ke, ba dan yaji abin da ya saba ji ba, sai dan kawai yau sabuwar hanya ce ya bud'e da kan shi, a k'arshe ma daga d'akin ta zuwa falon shi sai da ya d'auko ta ya fito da ita, ya na zaunar da ita yace "Bara na je na samo mi ki abin da za ki ci ko, na san yanzu ki na jin yunwa."
Cike da kissa da salon iskanci tace "Um, amma gaskiya ba komai zan iya ci ba."
Sai da ya sumbaci hannun ta yace "Ranar ki ce yau amarya, ki fad'i duk abin da ki ke son ci, za'a kawo mi ki shi gaban ki."
Cike da yauk'i tace "Da fari dai ruwan bunu na ke son na fara korawa a ciki na, bayan nan kuma sai na samu tuwon shinkafa."
Wani kallo ya mata da murmushi yace "Eyeee, amarsu, ko dai a dare d'aya har na yi nasarar aika sak'on ke kuma kin karb'a hannu bibbiyu."
K'asa ta yi da kai ta na murmushi, janyo ta ya yi ya rumgume yace "Allah ya sa haka Haseenah, zan fi kowa farin ciki da faruwar hakan, a karo na biyu Allah ya sake nuna min jini na a duniya."
Jin haka ai sai ta shagwab'e tace "Yunwa fa na ke ji sosai rabin rai."
Zunbur ya mik'e yace "Shikenan to, yanzu zan dawo, bara na shiga na ga auntyn ki sai na wuce."
Kwab'e fuska ta yi alamar za ta yi kuka, da sauri ya dawo ya zauna yace "Me ye kuma na kuka? Ciwo ki ke ji har yanzu?"
Kai ta girgiza tace "Ina tausayawa kai na ne dai kawai."
"Da me ya faru?"
Cikin goge ido tace "Ka ce sai ka fara zuwa wajen aunty na, kuma na san kai da aunty na kamar Roméo da Juliette ne, ban san yaushe za ka fito ba."
Murmushi ya yi yace "Yanzu fad'a min ya ki ke so ayi to?"
Cikin turo baki tace "Idan ka dawo ai sai ka je ku gaisa, kai kuma cinye kan ku ni dai ina daga nan ina cin abinci na."
Dariya ya yi yace "Kenan ba ki damu da ni ba ko?"
Hannun shi ta rik'o tana kallon idon shi tace "Da kafin daren jiya ka fad'i haka sai na iya yarda abisa wasu dalilai, amma banda safiyar da ta tabbatar min mun zama d'aya ni da kai."
Murmushin jin dad'i ya yi ya sumbaci kumatun ta ya mik'e yace "Sai na dawo, za ki sha zallar ruwan madarar soyayya."
Kashe mi shi ido ta yi tare da d'ora k'afa d'aya kan d'aya, Khadija ta fito cikin wata arniyar doguwar rigar shadda, kwanukan abincin ne hannun ta tare da Uwani a bayan ta, abin mamakin da ba ta tab'a ganinshi ba wai Usman ya fita ba tare da ya lek'a in da take ba, Haseenah da ta ga shigowar su ko kallo babu wanda ta ma, sai da ta aje kwanukan daga in da take tace "Amarya sannu da hutawa."
"Sannu." Ta fad'a ta na wani yamutsa fuska, Uwani ce tace "Ina kwana aunty amarya."
Kallon ta ta yi cikin rashin sanin wacece ita, Khadija ce tace "Sunan Uwani, mai aiki na ce, amma yanzu ta zama mai aikin mu gaba d'aya."
K'ala babu wanda ta tanka ma sai ma d'auke kai da ta yi, d'an cije leb'e Khadija ta yi alamar muje zuwa d'in nan, fita su ka yi su ka d'auko sauran kayan abin karin, ta na cikin jera su Bilal ya fito cikin shirin makarantar shi, da fara'a ta kalle shi tace "Yarima har ka shirya?"
Sai da ya je gaban ta ya sumbaci kumatun ta yace "Ina kwana sarauniya."
Dariya ta yi tace "Ka tashi lafiya?"
"Lafiya lau." Ya fad'a ya na jan kujera zai zauna, ido ta zaro mi shi tace "Kai, ba ka ga auntyn ka bane? Ka je ka gaishe ta mana."
Tsaye ya mik'e yace "Ki yi hak'uri Ammie, ban lura da ita ba."
Wucewa ya yi ya je har in da take, hannun shi ya d'ora a wuyan ta ya kai bakin shi zai sumbaci kumatun ta, ba zato ba tsammani ta ji abun, dan haka ta yi saurin zabura tare da ture shi da k'arfi har ya fad'i k'asa, tsaye ta mik'e tace "Me ye haka? Wannan wane irin iskanci ne? Wannan wani salon tuggun ku ne ko? To ka kiyaye ni wallahi, ni nan da ka ke gani na turmin tsakar gida ce."
Hararan shi ta yi ta koma ta zauna cikin tsawa tace "B'ace min da gani malam."
Tashi ya yi ya gyara jikin shi yace "Ki yi hak'uri aunty, dama zan gaishe ki ne kamar yanda na ke gaishe da Ammie na."
Tsaki ta yi ta harare shi sama da k'asa ta d'auke kai, wucewa ya yi ya koma wajen maman shi ya zauna kujerar da ita ce kujerar zaman shi dama, ta fara zuba mi shi a faranti kuma Usman ya shigo, daga in da Khadija ke tsaye ta sakar masa murmushi, shi ma mayar mata ya yi tare da nufa wajen su, Haseenah da kallon mamaki ta bishi, aje ledar hannun shi ya yi akan teburin ya sumbaci kumatun Dije yace "Sarauniya ta tashi lafiya?"
Karo na farko da Dije ta ji kunyar abin da ya yi gaban mutane, cike da kunya tace "Ina kwana babban mutum."
Kallon kwanukan ya yi yace "Ashe kin mana abin kari?"
Murmushi ta yi tace "Jiya ma ai gajiya ce ta hana."
Juyowa ya yi ya kalli Haseenah da ta daina kallon su dan bak'in ciki yace "Haseenah."
Ba tare da ta juyo ba tace "Na'am."
"Ki zo ga tuwan ki."
Da kan shi ya saka mata kafin suka wuce, Haseenah kuma kamar zuciyar ta za ta harba saboda bak'in kishi na banza da wofi, haka su ka zauna tare da Bilal a faranti d'aya su ka saka hannu dukan su, sai dai Khadija da Haseenah ba sosai su ke cin abincin ba, dan kowa da abin da ke ran shi, haka dai su ka gama ango ya shirya ya fita, amarya ta koma b'angaren ta.
*Yau* ma dai sosai aka gwangwaje walimar damu, mutane sun sha anko gwanin ban sha'awa, haka aka yi abin da ya tara mutane sai dai sisin kwabo ko k'wayar gero Usman bai karb'a ba a hannun iyayen Haseenah, daga k'arshe dai tsofaffi da iyaye sun sake had'a kan Khadija da Haseenah sun mu su nasiha da jan kunne tare da gargad'i, a k'arshe kuma su ka bisu da addu'ar fatan zaman lafiya da kuma zuri'a mai albarka, haka yau ma taro ya watse in da kowa ya koma gefe dan a kalli kalar na su zaman, da dare ma Usman ya shigo tare da manyan aminan shi Alhaji *Murtala* da Alhaji *Adamu* mijin Salamatu, suma dai nasihar su ka sake mu su tare da fatan alkairi daga bisani su ka tafi.
*Allah ya bada hak'urin zama da juna.*
05/01/2020 à 22:11 - 💋😘💋: 💑💑💑💑💑💑💑💑💑💑
*KALLON KITSE*
_(Ake wa rogo)_
💑💑💑💑💑💑💑💑💑💑
_SAMIRA HAROUNA_
*Littatafan marubuciyar*
*1* _KAUSSAR_
*2* _D'AUKAR FANSA_
*3* _BA SO BANE_
*4* _AUREN HAD'I_
*5* _SANIN MASOYI_
*6* _JIHADI_
*7* _K'ANGIN RAYUWA_
*8* _ITACE K'ADDARARMU_
*9* _KAWU NA NE_
*10* _MAATA_
*11* _KALLON KITSE..._
*SADAUKARWA GA*
_MATAN FARKO_🧕🏼 *(UWAYEN GIDA)*
🇸🇦 *ZAMAN AMANA WRITER'S*
_(Gidan zaman lafiya da amana insha Allah)_🤜🤛
```Fatan alkairi masoya```
_Bismillahir rahamanir rahim_
*7*
Kasancewar Bilal zai koma makaranta yau ya sa Khadija ta shi da wuri ta nufi madafa dan shirya abin kari, (albarkacin kaza k'adangare kan sha ruwan kasko), tun da ta tunkari k'ofar ta gan ta bud'e ta ke mamakin yanda k'ofar ke bud'e, da wannan mamaki ta k'arasa shiga, turus ta ja ta tsaya ganin oga malam yallab'ai kuma alhaji Usman ya d'auki k'atuwar tasa daga kan gas ya na juye tafasashen ruwan da ya dafa a k'aramin bokiti, da sauri ta k'arasa ta na fad'in "Abban Bilal, me ka ke yi haka?"
Wani abu ya ji tare da kunya dan baiso ya ganta ba ko ita ta gan shi, d'agowa ya yi bayan ya juye ruwan ya na d'an had'e fuska yace "Um, wallahi, wai wanna ce, ina jin dai, kamar dai ba ta cika wanka da ruwan sanyi bane da safe, to shine na..."
Katse shi ta yi da cewa "Uhum! Na gane ma, ka kai mata to kafin su huce."
D'auka ya yi cike da kunya ya fice, sai da ya b'ace ma ganin ta taji hawaye sun cika idon ta, cire gilashin ta ta yi ta share k'wallan, ji ta yi ma ba za ta iya komai ba dan haka ta juyo ta fito, ta na zuwa falon ta taga abin mamaki, da sauri ta saki murmushi tace "Wa na ke gani kamar Uwani?"
Da dariya matashiyar yarinyar tace "Ni da kai na Maman Bilal."
"Uwani yaushe ki ka dawo? Sai kawai na gan ki haka kamar aljana."
Dariya Uwani ke yi har tace "Jiya na shigo da magriba, shi ya sa ma ban zo tun jiya ba."
"Kai, amma ko na ji dad'in zuwan nan na ki, dan yanzu haka da ki ka ganni wallahi na gaji ne, har na shiga madafar kuma na fito da d'aki ne zan koma ba kwanta kuma sai gaki."
Da karsashi Uwani ta mik'e tace "Maman Bilal ba ki da matsala tun da na dawo, yanzu fad'i me za'a dafa sai na shiga da kai na."
"A'a ba za ayi haka ba, ai ganin ki karsashi ya k'ara min, kawai muje tare sai mu d'ora, kinga ma daga nan sai ki bani labarin abinda ya tsayar da ke."
Dariya ta yi su ka nufi madafar, aiki suke su na hira ta na fad'a mata abin da ya tsayar da ita, da haka su ka kusan kammalawa Khadija ta sakar mata aikin ta tafi d'aki dan yin wanka.
Da taimakon Usman Haseenah ta shirya kan ta sai shefiyar shagwab'a take zuba mi shi, shi kam yau ya na jin ya samu sabuwar hanya sai wani biye mata ya ke, ba dan yaji abin da ya saba ji ba, sai dan kawai yau sabuwar hanya ce ya bud'e da kan shi, a k'arshe ma daga d'akin ta zuwa falon shi sai da ya d'auko ta ya fito da ita, ya na zaunar da ita yace "Bara na je na samo mi ki abin da za ki ci ko, na san yanzu ki na jin yunwa."
Cike da kissa da salon iskanci tace "Um, amma gaskiya ba komai zan iya ci ba."
Sai da ya sumbaci hannun ta yace "Ranar ki ce yau amarya, ki fad'i duk abin da ki ke son ci, za'a kawo mi ki shi gaban ki."
Cike da yauk'i tace "Da fari dai ruwan bunu na ke son na fara korawa a ciki na, bayan nan kuma sai na samu tuwon shinkafa."
Wani kallo ya mata da murmushi yace "Eyeee, amarsu, ko dai a dare d'aya har na yi nasarar aika sak'on ke kuma kin karb'a hannu bibbiyu."
K'asa ta yi da kai ta na murmushi, janyo ta ya yi ya rumgume yace "Allah ya sa haka Haseenah, zan fi kowa farin ciki da faruwar hakan, a karo na biyu Allah ya sake nuna min jini na a duniya."
Jin haka ai sai ta shagwab'e tace "Yunwa fa na ke ji sosai rabin rai."
Zunbur ya mik'e yace "Shikenan to, yanzu zan dawo, bara na shiga na ga auntyn ki sai na wuce."
Kwab'e fuska ta yi alamar za ta yi kuka, da sauri ya dawo ya zauna yace "Me ye kuma na kuka? Ciwo ki ke ji har yanzu?"
Kai ta girgiza tace "Ina tausayawa kai na ne dai kawai."
"Da me ya faru?"
Cikin goge ido tace "Ka ce sai ka fara zuwa wajen aunty na, kuma na san kai da aunty na kamar Roméo da Juliette ne, ban san yaushe za ka fito ba."
Murmushi ya yi yace "Yanzu fad'a min ya ki ke so ayi to?"
Cikin turo baki tace "Idan ka dawo ai sai ka je ku gaisa, kai kuma cinye kan ku ni dai ina daga nan ina cin abinci na."
Dariya ya yi yace "Kenan ba ki damu da ni ba ko?"
Hannun shi ta rik'o tana kallon idon shi tace "Da kafin daren jiya ka fad'i haka sai na iya yarda abisa wasu dalilai, amma banda safiyar da ta tabbatar min mun zama d'aya ni da kai."
Murmushin jin dad'i ya yi ya sumbaci kumatun ta ya mik'e yace "Sai na dawo, za ki sha zallar ruwan madarar soyayya."
Kashe mi shi ido ta yi tare da d'ora k'afa d'aya kan d'aya, Khadija ta fito cikin wata arniyar doguwar rigar shadda, kwanukan abincin ne hannun ta tare da Uwani a bayan ta, abin mamakin da ba ta tab'a ganinshi ba wai Usman ya fita ba tare da ya lek'a in da take ba, Haseenah da ta ga shigowar su ko kallo babu wanda ta ma, sai da ta aje kwanukan daga in da take tace "Amarya sannu da hutawa."
"Sannu." Ta fad'a ta na wani yamutsa fuska, Uwani ce tace "Ina kwana aunty amarya."
Kallon ta ta yi cikin rashin sanin wacece ita, Khadija ce tace "Sunan Uwani, mai aiki na ce, amma yanzu ta zama mai aikin mu gaba d'aya."
K'ala babu wanda ta tanka ma sai ma d'auke kai da ta yi, d'an cije leb'e Khadija ta yi alamar muje zuwa d'in nan, fita su ka yi su ka d'auko sauran kayan abin karin, ta na cikin jera su Bilal ya fito cikin shirin makarantar shi, da fara'a ta kalle shi tace "Yarima har ka shirya?"
Sai da ya je gaban ta ya sumbaci kumatun ta yace "Ina kwana sarauniya."
Dariya ta yi tace "Ka tashi lafiya?"
"Lafiya lau." Ya fad'a ya na jan kujera zai zauna, ido ta zaro mi shi tace "Kai, ba ka ga auntyn ka bane? Ka je ka gaishe ta mana."
Tsaye ya mik'e yace "Ki yi hak'uri Ammie, ban lura da ita ba."
Wucewa ya yi ya je har in da take, hannun shi ya d'ora a wuyan ta ya kai bakin shi zai sumbaci kumatun ta, ba zato ba tsammani ta ji abun, dan haka ta yi saurin zabura tare da ture shi da k'arfi har ya fad'i k'asa, tsaye ta mik'e tace "Me ye haka? Wannan wane irin iskanci ne? Wannan wani salon tuggun ku ne ko? To ka kiyaye ni wallahi, ni nan da ka ke gani na turmin tsakar gida ce."
Hararan shi ta yi ta koma ta zauna cikin tsawa tace "B'ace min da gani malam."
Tashi ya yi ya gyara jikin shi yace "Ki yi hak'uri aunty, dama zan gaishe ki ne kamar yanda na ke gaishe da Ammie na."
Tsaki ta yi ta harare shi sama da k'asa ta d'auke kai, wucewa ya yi ya koma wajen maman shi ya zauna kujerar da ita ce kujerar zaman shi dama, ta fara zuba mi shi a faranti kuma Usman ya shigo, daga in da Khadija ke tsaye ta sakar masa murmushi, shi ma mayar mata ya yi tare da nufa wajen su, Haseenah da kallon mamaki ta bishi, aje ledar hannun shi ya yi akan teburin ya sumbaci kumatun Dije yace "Sarauniya ta tashi lafiya?"
Karo na farko da Dije ta ji kunyar abin da ya yi gaban mutane, cike da kunya tace "Ina kwana babban mutum."
Kallon kwanukan ya yi yace "Ashe kin mana abin kari?"
Murmushi ta yi tace "Jiya ma ai gajiya ce ta hana."
Juyowa ya yi ya kalli Haseenah da ta daina kallon su dan bak'in ciki yace "Haseenah."
Ba tare da ta juyo ba tace "Na'am."
"Ki zo ga tuwan ki."