Sashe 55
Kallon Kitse Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Wani irin mamaki ne ya bayyana a fuskar Khadija ta sunkuya ta aje Bilal ta kalle ta da kyau tace "Hajia, ya jikin shi fa ki ke tambaya? Hakan na nufin dama kinsan ba ya da lafiya amma shine bai samu kimar da za ku zo ku duba shi ba tunda ku ka shigo gidan nan, tunda rana fa na ke iya jiyo hayaniyar ku a gidan nan, amma sai yanzu za ku zo ku tambaye ni lafiyar shi, hum, to ba ni ku ka wa ba, kan ku kuka wa."
Juyowa ta yi ta d'auki Bilal za ta wuce d'aki Aziza tace "Aunty Khadija ga kayan shi in ji Haseenah."
Juyowa ta yi fuska a had'e tace "Bilal na da kayan da a shekara baya saka su, ku mayar mata ta mayarwa da bokan nata tace ba ma so."
"Khadija, wai baki da hankali ne? Ke kad'ai ki ka fi kowa baki anan da za ki zaunar da mu ki na fad'a mana magana, so ko ke kice dole ke ce akawa laifi kenan bayan duk abin da ki ka aikata, me ki ka d'auke ni ne da har za ki tsaya ki na fad'awa 'yan uwa na magana kuma daga ciki har da mahaifiya ta, ko kinsan da hushin ki na dawo garin nan? Amma shine za ki nuna ke ce ma akawa laifi, to ya isheki haka, maza wuce ciki zan zo na same ki."
Yanda ya ke maganar ne ya sa ta yi dariya tace "To ka had'iye ni mana kaga shikenan sai ka huta."
Ta na fad'a ba ta tsaya sauraren shi ba ta shige ciki da Bilal a hannu, tana shigewa Hajia tace "Haka kuma abin nata ya zama? Lallai mutum bashi da kama, yanzu waye zai iya cewa Khadija za ta yi abin da ta yi."
Rabi'a ce tace "Hum, dama ai sai anyi yunwa halin kowa ke fitowa."
"Gaskiya ne, yau na tabbatar da hakan." Cewar Hajia, Usman ne ya kalle su yace "Hajia ku yi hak'uri dan Allah, kar ku damu da abin da ya faru."
"Ya kar a damu, ba ka ji maganganun da ta fad'a mana bane, nan gaba mu ka san me za ta fad'a ko ta yi mana, za ta iya cewa ma Bilal d'an ta ne ita kad'ai."
Mik'ewa su ka yi su na fad'in "Sai anjiman ku."
Tafiya su ka yi Aziza ta koma wajen Haseenah, shi kuma d'akin Khadija ya koma, ya na zuwa ta kwantar da Bilal yace "Ya kamata kisan ina d'aga mi ki k'afa ne saboda abubuwa dayawa, amma naga sam kin kasa fahimta sai ma son wuce gona da iri, Khadija wannan fa mahaifiya ta da ki ka tsaya ki ka fad'a mata magana son ran ki, me ki ke ji da shi? Rashin kunya ko fitsara?"
Tsaye ta mik'e tace "Kalle ni da kyau kaga da me ya kamata ka kira ni."
Da yatsa ya nuna ta yace "Na zo ne dan na fad'a mi ki wani abu, wannan ya zama na k'arshe da hannun ki zai sake tab'a jikin Haseenah, in kuma ba haka ba wallahi zan d'auki matakin da ba lallai ya mi ki dad'i ba, kinji na fad'a mi ki."
"Haseenah? Haseenah fa ka ce? To in har kaga hannu na bai tab'a jikin ta ba ka tabbatar ba ta min rashin kunya ba, wallahi ko yanzu tace za ta min abinda ba zan d'auka ba ni kuma can ci uwar ta a gidan nan kuma a gaban ka."
Daf da ita ya matso cikin d'aga murya yace "Saboda ki nuna min kin rainani? Ban isa na fad'a mi ki kiji ba kenan?"
Kafin ta yi magana ya sake k'ure ta da fad'in "Bak'in ciki ki ke da ta samu ciki za ta haifa min wasu yaran? Shi ya sa ki ka yi k'ok'arin zubar mata da ciki, wallahi Allah ne ya ceceki cikin nan bai zube ba, da sai na sa kinyi aman duk wani abu da ke cikin ki kema."
Rasa abin fad'a ta yi saboda kukan da ke son taho mata, rab'awa ta yi da nufin shiga ban d'aki ya rik'o hannun ta ya nufi k'ofar fita da ita yace "Muke ki bata hak'uri, 'yan uwan ta ma na nan suna tsammanin jin hukunci daga gare ni, ba zan barki haka ba, amma da farko ki ba su hak'uri."
Jin wani sabon rainin hankali ya sa Khadija fizgo hannun ta da k'arfi tace "In kuma ka ga haka ta faru to tabbas ba ta hanyar aure aka haife ni ba."
Juyowa ya yi ya na kallon ta ita kuma ta gyara tsayuwa tace "Wallahi na rantse da sarkin daya busa min numafshi ko za ka kashe ni ba zan bawa uban kowa hak'uri ba, Usman." Ta kira sunan shi cikin d'aga murya ta d'ora da "Karfa ka yi tunanin sanin da ka min da, wallahi yanzu walkice ni daidai na ke da k'ugun ko wace shegiyyy..."
Marin da ya zabga mata ne ya sa ta fad'i gefe har gilashin ta na fita daga idon ta, dafe kunci ta yi ta d'ago kai ta kalle shi, cikin fitar hayyaci ya shak'o wuyan rigar ta ya mik'ar da ita tsaye yace "Wuce muje na ce."
Ba tate da tayi yunk'urin k'watar kan ta ba tace "Ba zan je ba wallahi, banga laifin da na yi ba da zan bawa wani hak'uri."
Wani marin ya sake kifa mata da k'arfi da ya sa Bilal zabura ya tashi zaune, sake dafe kunci ta yi ta na kallon shi dishi-dishi, da hannu ya nuna mata k'ofa yace "Wuce muje."
"Ba zan je ba." Ta fad'a ta na k'ok'arin tashi tsaye, a karo na uku ya sake gwab'a mata wani marin ya na fad'in "Ai kuwa za ki mutu kamar yanda ki ka ce, tunda taurin kai ne da ke."
*Lovely sister kin tuna ko? Ki ci gaba da hak'uri komai zai wuce da ikon mai kowa mai komai.*
Bilal na ganin haka ya sauko daga kan gado ya rik'e hannun mahaifin shi ya na hawaye yace "Abba dan Allah ka daina, ka bar dukan ta."
Ture shi ya yi gefe d'aya ya na fad'in "Kai bar ni na nuna mata na fita taurin kai, zuciya ai ba ki fini ba." Ya k'arashe da kifa mata wani marin, a tak'aice saida Usman ya mata lafiyayyun mari har guda takwas a kumatu kamar ya samu jaka, da ta kasa tashi ne gashi ba ta iya jin komai ba ta ganin komai ya sa take zaune har yanzu k'asa, cikin hargagi ya ke fad'in "Wai ba za ki tashi ba?" Ya fad'a ya na zura k'afa ya na kai mata hanb'ara, Bilal ne ya rik'e shi ta baya ya na kuka sosai ya na fad'in ya k'yale mi shi Mummyn shi, Usman kam ido sun rufe rai ya b'ace bai ma san me yake yi ba sai harbinta ya ke da k'afa ya na had'awa da hannu ya na nausarta, da sauri Bilal ya zo ya rumgume ta ya juyo da kan shi ya kalli Usman yace "Abba na tsane ka, ba na son ka, ka fita ka ba mu wuri, Allah saiya sakawa Mummy na."
Cak ya tsaya da hannun shi sama daga d'agawar da ya yi zai dake ta, duk da ya ji kalmar tsanar har k'asan zuciyar shi amma saiya basar ya nuna ta da yatsa yace "Yanzu hankalin ki ya kwanta da ki ka ji d'ana ya na fad'in ya tsane ni? To ki zuba ruwa k'asa kisha dan farin ciki, ni ma kuma Allah ne zai saka min da har ki ka yi sanadiyar da d'ana ya furta min kalmar tsana, munafuka kawai shed'aniya, kuma ki sani wallahi in har ki ka ce wannan halin za ki ci gaba da nunawa a gidan nan kenan, to ki na tare da wahala wallahi."
Juyawa ya yi ya fita, d'auko gilashinta Bilal ya yi ya saka mata, mik'ewa ta yi ta shige ban d'aki ba dan tasan in da take saka k'afar ta ba, zaune ta yi bakin bahon wanka ta kunna ruwa suna zuba ta fashe da kuka, tabbas yau tabbatar da Usman baya hayyacin shi tunda har zai iya mata wannan dukan a gaban d'an su, mutumin da magana marar dad'i ba ta tab'a shiga tsakaninsu ba amma yau har da kiran ta munafuka, ta jima zaune ta ci kukan ta kafin ta mik'e ta wanke idon ta ta kashe ruwan ta fito, lokacin fuskar ta har ta kumbura kamar an hura balam-balam, jakunkunanta ta d'auko ta d'ura duk wani abun buk'atar ta a ciki Bilal na kallo, hijabi ta saka ta kalli Bilal tace "Bilal."
Cikin muryar kuka yaron ya amsa da "Na'am Mummy."
Cikin muryar da tasha kuka tace "Tafiya zanyi Bilal, ka zauna gidan mahaifin ka dan ba na jin zan iya dawowa gidan nan, amma ka sani ina tare da kai kaji ko."
Da sauri ya taso yace "A'a Mummy, ni dai dan Allah ki tafi da ni, wallahi ba zan zauna nan ba, yanzu Abba ba ya so na, aunty amarya ma ba so na take yi ba, ni dai wallahi binki zanyi."
"Bilal ba zan iya tafiya da kai ba, ba wai dan ba na so na tafi da kai d'in ba, sai dai nasan mahaifin ka ba zai bari ba, ka tuna ranar ma da zan tafi shi ya hana na tafi da kai? To ka yi hak'uri ka zauna kaji, idan ba ka jin dad'in zaman nan sai ka ce ya kai ka gidan su Hajia."
Cikin kula yace "Ni dai ba na so Mummy, idan kuma ki ka tafi ki ka bar ni wallahi guduwa zanyi daga gidan nan."
Cikin sanyin jiki tace "Shikenan je ka had'o kayan ka."
Ya na fita ta zauna bakin gado ta zuba tagumi ta na fitar da wasu hawaye masu zafin gaske, ba wani jimawa Bilal ya dawo da k'atuwar jakar shi shima ya sanyo duk wani abun buk'atar shi, kallon shi ta yi tace "Ka d'auko kayan makarantar ka?"
Juyowa ta yi ta d'auki Bilal za ta wuce d'aki Aziza tace "Aunty Khadija ga kayan shi in ji Haseenah."
Juyowa ta yi fuska a had'e tace "Bilal na da kayan da a shekara baya saka su, ku mayar mata ta mayarwa da bokan nata tace ba ma so."
"Khadija, wai baki da hankali ne? Ke kad'ai ki ka fi kowa baki anan da za ki zaunar da mu ki na fad'a mana magana, so ko ke kice dole ke ce akawa laifi kenan bayan duk abin da ki ka aikata, me ki ka d'auke ni ne da har za ki tsaya ki na fad'awa 'yan uwa na magana kuma daga ciki har da mahaifiya ta, ko kinsan da hushin ki na dawo garin nan? Amma shine za ki nuna ke ce ma akawa laifi, to ya isheki haka, maza wuce ciki zan zo na same ki."
Yanda ya ke maganar ne ya sa ta yi dariya tace "To ka had'iye ni mana kaga shikenan sai ka huta."
Ta na fad'a ba ta tsaya sauraren shi ba ta shige ciki da Bilal a hannu, tana shigewa Hajia tace "Haka kuma abin nata ya zama? Lallai mutum bashi da kama, yanzu waye zai iya cewa Khadija za ta yi abin da ta yi."
Rabi'a ce tace "Hum, dama ai sai anyi yunwa halin kowa ke fitowa."
"Gaskiya ne, yau na tabbatar da hakan." Cewar Hajia, Usman ne ya kalle su yace "Hajia ku yi hak'uri dan Allah, kar ku damu da abin da ya faru."
"Ya kar a damu, ba ka ji maganganun da ta fad'a mana bane, nan gaba mu ka san me za ta fad'a ko ta yi mana, za ta iya cewa ma Bilal d'an ta ne ita kad'ai."
Mik'ewa su ka yi su na fad'in "Sai anjiman ku."
Tafiya su ka yi Aziza ta koma wajen Haseenah, shi kuma d'akin Khadija ya koma, ya na zuwa ta kwantar da Bilal yace "Ya kamata kisan ina d'aga mi ki k'afa ne saboda abubuwa dayawa, amma naga sam kin kasa fahimta sai ma son wuce gona da iri, Khadija wannan fa mahaifiya ta da ki ka tsaya ki ka fad'a mata magana son ran ki, me ki ke ji da shi? Rashin kunya ko fitsara?"
Tsaye ta mik'e tace "Kalle ni da kyau kaga da me ya kamata ka kira ni."
Da yatsa ya nuna ta yace "Na zo ne dan na fad'a mi ki wani abu, wannan ya zama na k'arshe da hannun ki zai sake tab'a jikin Haseenah, in kuma ba haka ba wallahi zan d'auki matakin da ba lallai ya mi ki dad'i ba, kinji na fad'a mi ki."
"Haseenah? Haseenah fa ka ce? To in har kaga hannu na bai tab'a jikin ta ba ka tabbatar ba ta min rashin kunya ba, wallahi ko yanzu tace za ta min abinda ba zan d'auka ba ni kuma can ci uwar ta a gidan nan kuma a gaban ka."
Daf da ita ya matso cikin d'aga murya yace "Saboda ki nuna min kin rainani? Ban isa na fad'a mi ki kiji ba kenan?"
Kafin ta yi magana ya sake k'ure ta da fad'in "Bak'in ciki ki ke da ta samu ciki za ta haifa min wasu yaran? Shi ya sa ki ka yi k'ok'arin zubar mata da ciki, wallahi Allah ne ya ceceki cikin nan bai zube ba, da sai na sa kinyi aman duk wani abu da ke cikin ki kema."
Rasa abin fad'a ta yi saboda kukan da ke son taho mata, rab'awa ta yi da nufin shiga ban d'aki ya rik'o hannun ta ya nufi k'ofar fita da ita yace "Muke ki bata hak'uri, 'yan uwan ta ma na nan suna tsammanin jin hukunci daga gare ni, ba zan barki haka ba, amma da farko ki ba su hak'uri."
Jin wani sabon rainin hankali ya sa Khadija fizgo hannun ta da k'arfi tace "In kuma ka ga haka ta faru to tabbas ba ta hanyar aure aka haife ni ba."
Juyowa ya yi ya na kallon ta ita kuma ta gyara tsayuwa tace "Wallahi na rantse da sarkin daya busa min numafshi ko za ka kashe ni ba zan bawa uban kowa hak'uri ba, Usman." Ta kira sunan shi cikin d'aga murya ta d'ora da "Karfa ka yi tunanin sanin da ka min da, wallahi yanzu walkice ni daidai na ke da k'ugun ko wace shegiyyy..."
Marin da ya zabga mata ne ya sa ta fad'i gefe har gilashin ta na fita daga idon ta, dafe kunci ta yi ta d'ago kai ta kalle shi, cikin fitar hayyaci ya shak'o wuyan rigar ta ya mik'ar da ita tsaye yace "Wuce muje na ce."
Ba tate da tayi yunk'urin k'watar kan ta ba tace "Ba zan je ba wallahi, banga laifin da na yi ba da zan bawa wani hak'uri."
Wani marin ya sake kifa mata da k'arfi da ya sa Bilal zabura ya tashi zaune, sake dafe kunci ta yi ta na kallon shi dishi-dishi, da hannu ya nuna mata k'ofa yace "Wuce muje."
"Ba zan je ba." Ta fad'a ta na k'ok'arin tashi tsaye, a karo na uku ya sake gwab'a mata wani marin ya na fad'in "Ai kuwa za ki mutu kamar yanda ki ka ce, tunda taurin kai ne da ke."
*Lovely sister kin tuna ko? Ki ci gaba da hak'uri komai zai wuce da ikon mai kowa mai komai.*
Bilal na ganin haka ya sauko daga kan gado ya rik'e hannun mahaifin shi ya na hawaye yace "Abba dan Allah ka daina, ka bar dukan ta."
Ture shi ya yi gefe d'aya ya na fad'in "Kai bar ni na nuna mata na fita taurin kai, zuciya ai ba ki fini ba." Ya k'arashe da kifa mata wani marin, a tak'aice saida Usman ya mata lafiyayyun mari har guda takwas a kumatu kamar ya samu jaka, da ta kasa tashi ne gashi ba ta iya jin komai ba ta ganin komai ya sa take zaune har yanzu k'asa, cikin hargagi ya ke fad'in "Wai ba za ki tashi ba?" Ya fad'a ya na zura k'afa ya na kai mata hanb'ara, Bilal ne ya rik'e shi ta baya ya na kuka sosai ya na fad'in ya k'yale mi shi Mummyn shi, Usman kam ido sun rufe rai ya b'ace bai ma san me yake yi ba sai harbinta ya ke da k'afa ya na had'awa da hannu ya na nausarta, da sauri Bilal ya zo ya rumgume ta ya juyo da kan shi ya kalli Usman yace "Abba na tsane ka, ba na son ka, ka fita ka ba mu wuri, Allah saiya sakawa Mummy na."
Cak ya tsaya da hannun shi sama daga d'agawar da ya yi zai dake ta, duk da ya ji kalmar tsanar har k'asan zuciyar shi amma saiya basar ya nuna ta da yatsa yace "Yanzu hankalin ki ya kwanta da ki ka ji d'ana ya na fad'in ya tsane ni? To ki zuba ruwa k'asa kisha dan farin ciki, ni ma kuma Allah ne zai saka min da har ki ka yi sanadiyar da d'ana ya furta min kalmar tsana, munafuka kawai shed'aniya, kuma ki sani wallahi in har ki ka ce wannan halin za ki ci gaba da nunawa a gidan nan kenan, to ki na tare da wahala wallahi."
Juyawa ya yi ya fita, d'auko gilashinta Bilal ya yi ya saka mata, mik'ewa ta yi ta shige ban d'aki ba dan tasan in da take saka k'afar ta ba, zaune ta yi bakin bahon wanka ta kunna ruwa suna zuba ta fashe da kuka, tabbas yau tabbatar da Usman baya hayyacin shi tunda har zai iya mata wannan dukan a gaban d'an su, mutumin da magana marar dad'i ba ta tab'a shiga tsakaninsu ba amma yau har da kiran ta munafuka, ta jima zaune ta ci kukan ta kafin ta mik'e ta wanke idon ta ta kashe ruwan ta fito, lokacin fuskar ta har ta kumbura kamar an hura balam-balam, jakunkunanta ta d'auko ta d'ura duk wani abun buk'atar ta a ciki Bilal na kallo, hijabi ta saka ta kalli Bilal tace "Bilal."
Cikin muryar kuka yaron ya amsa da "Na'am Mummy."
Cikin muryar da tasha kuka tace "Tafiya zanyi Bilal, ka zauna gidan mahaifin ka dan ba na jin zan iya dawowa gidan nan, amma ka sani ina tare da kai kaji ko."
Da sauri ya taso yace "A'a Mummy, ni dai dan Allah ki tafi da ni, wallahi ba zan zauna nan ba, yanzu Abba ba ya so na, aunty amarya ma ba so na take yi ba, ni dai wallahi binki zanyi."
"Bilal ba zan iya tafiya da kai ba, ba wai dan ba na so na tafi da kai d'in ba, sai dai nasan mahaifin ka ba zai bari ba, ka tuna ranar ma da zan tafi shi ya hana na tafi da kai? To ka yi hak'uri ka zauna kaji, idan ba ka jin dad'in zaman nan sai ka ce ya kai ka gidan su Hajia."
Cikin kula yace "Ni dai ba na so Mummy, idan kuma ki ka tafi ki ka bar ni wallahi guduwa zanyi daga gidan nan."
Cikin sanyin jiki tace "Shikenan je ka had'o kayan ka."
Ya na fita ta zauna bakin gado ta zuba tagumi ta na fitar da wasu hawaye masu zafin gaske, ba wani jimawa Bilal ya dawo da k'atuwar jakar shi shima ya sanyo duk wani abun buk'atar shi, kallon shi ta yi tace "Ka d'auko kayan makarantar ka?"