← Book details Kallon Kitse Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 74 OF 86

Sashe 74

Kallon Kitse Part 1 Complete Hausa Novel · about 7 min read

Juyowa ya yi ya kalle ta da mamaki yace "Da Bilal d'in za ki yi kishi? D'ana ne fa shi, kinsan mahimmancin shi a gare ni kuwa? To shi d'in kamar rayuwa ta ne, ina k'aunar sa fiye da komai, ki iya bakin ki in dai akan iyali na ne, ba na juran b'acin ran su ko kad'an."

Idon ta cike da ruwa tace "Usman ba ka adalci wallahi, kullum nunawa ka ke Khadija da d'an ta sune rayuwar ka, kullum sune ma su mahimmanci a wajen ka amma ni ko oho, to kasan ba ka so na me ya sa ka aure ni?"

Girgiza kai ya yi yace "Ni bance ba na son ki ba, sai dai abin da na sani kawai shine ina son iyali na, idan ki na son zama da ni ki so su kema, kuma kar ki d'auka Khadija kishiyar ki ce ki yi kishi da ita, maganar gaskiya ta wuce nan a wuri na, Bilal d'ana ne da ya fito daga jiki na tsatsona, amma ina wa mahaifiyar shi son da bana ma sa, kinsan me ya sa?"

*Ita rayuwa dama haka take, da kin zauna da su lafiya da wannan ranar ba ta zo ba, kuskuren da mu mata keyi wani lokaci shine, ba ma fahimtar abin da mazajenmu suke so, idan har ki ka fahimci mijinki na bala'in son mahaifiyarsa ko yan uwansa ko yayansa, sai ke ma ki bishi ki nuna musu so na gaskiya, ba dan komai ba dan kawai ki faranta mi shi, hakan zaisa ya dinga kallonki da daraja da kima, saboda kina son abin da yake so, amma kishi da hauka da wauta sai ta saka mu rufe idonmu mu nuna k'iyayya da kishi kan abinda suke so, yanzu dai gashi kalaman da a baya bai iya fad'a mata yanzu gashi ya na kallonta ya fad'a mata, kenan ta jima ba ta mutu ba, Allah kasa mufi k'arfin zuciyarmu.*

D'orawa ya yi da "Saboda da ita na fara had'uwa, ita Allah ya fara bani kafin ya bani Bilal, ita ce wacce Bilal d'in ya fito daga jikin ta, shi ya sa na ke mata k'aunar da ko shi Bilal ba na masa, zanji zafi matuk'a idan aka ce yau na rasa Bilal, amma kuma zanyi farin ciki idan na waiga naga Khadija a gefe na, ba dan komai ba saidan nasan za ta sake bani wani Bilal d'in."

Ya na gama fad'a ya juya ya bar d'akin ya koma na shi ya kwanta ya rumgume Bilal kamar zai had'e shi, ya na shafa shi har bacci ya d'auke shi shima, Haseenah kam kuka ta fashe da shi mai tsanani, wai abin da a baya yake ma sayawa baya fad'a yau gashi ya fad'a, kai lallai abin nan bana lafiya bane, tunaninta ne ya bata duk wani shiri da tayi a kan shi ya wargaje, dan haka dole ta sake sabo, da haka ita ma ta yi bacci da tunanin kiran Mariya idan gari ya waye.

*Luv u all.*😘
09/03/2020 à 15:01 - 💋😘💋: 💑💑💑💑💑💑💑💑💑💑
*KALLON KITSE*
_(Ake wa rogo)_
💑💑💑💑💑💑💑💑💑💑

_SAMIRA HAROUNA_

*Litattafan marubuciyar*

*1* _KAUSSAR_
*2* _D'AUKAR FANSA_
*3* _BA SO BANE_
*4* _AUREN HAD'I_
*5* _SANIN MASOYI_
*6* _JIHADI_
*7* _K'ANGIN RAYUWA_
*8* _ITACE K'ADDARARMU_
*9* _KAWU NA NE_
*10* _MAATA_
*11* _KALLON KITSE..._

*SADAUKARWA GA*

_MATAN FARKO_ 🧕🏼 *(UWAYEN GIDA)*

🇸🇦 *ZAMAN AMANA WRITER'S*
_(Gidan zaman lafiya da amana insha Allah)_🤜🤛

```Fatan alkairi masoya```

_💕 Masoya wannan littafi wannan kyautar ku ce, nagode da soyayyar da kuke nuna min ni da kaya na😚, Allah ya barmu tare._💞

_Bismillahir rahamanir rahim_

*37*

Ko da gari ya waye Bilal ya shirya cikin k'ananan kaya dan yau alhamis ce ba karatu, Usman ma kamar kullum cikin shadda ruwan madara ya shirya, tare suka fito falon Haseenah sun same ta zaune tana waya da Mariya, bayan ta fad'a mata akwai matsala ne Mariya tace ta sake fito da kud'i kawai a mata aiki, kafin ta yi magana ta ji fitowar su hakan ya tilasta mata aje wayar, juyowa ta yi ta na kallon su, duk da cikin hushi take amma tabbas tasan an samo Bilal ne daga Usman, dan zubin hallitarsu ma iri d'aya ce, duk da ba ta zauna da yaron sosai ba amma ta fahimci ya na da miskilanci fiye da ubansa, kai tsaye teburin cin abinci su ka nufa dan ba su ma lura da ita a zaune ba, saida ta ga sun zauna ta taso ta nufo su dan zuba mu su abinci, sai dai ta na mamaki yanda yau Usman zai ci abincin ta tunda ya jima baici ba, shi kuma zai ci ne kawai saboda Bilal na gidan yau, amma sam baya sha'awar cin abincin ta tunda ya lura kullum abinci kala d'aya ta iya sarrafawa, tun kafin ta tsaya wajen Bilal yace "Aunty ina kwana?"

Cike da makirci ta shafo kan shi tace "Yarima, ashe gidan mu ka kwana jiya, lokacin da ku ka shigo har na yi bacci, ya ka ke?"

Shi kam yaron fuskar shi ba fara'a yace "Lafiya lau."

Kallon Usman ta yi wanda ke kallon cikin ta shi ma tace "Ina kwana babban mutum?"

Ba walwala a tare da shi yace "Lafiya lau, ya jikin na ki?"

Da murmushi ta amsa da "Da sauk'i sosai." Shayi ta fara had'awa Bilal ta aje ma sa kafin Usman d'in, tare su ka karya dukan su bayan sun gama Usman ya mik'e zai fita, hannun Bilal ya kamo yace "Muje ko yarima, yau da kai za mu fita."

Da zumud'i ya mik'e tsaye dan bin mahaifin shi amma sai Haseenah tace "Haba dai babban mutum, wannan ma ai son kai ne wallahi, yaushe rabon da na ga Bilal, yau ya zo kuma shine za ka fice da shi, gaskiya ni dai ban yarda ba."

Kallon ta ya yi yace "To ya ki ke so ayi?" Kallon Bilal ta yi tace "Ka bar min shi mana, anjima idan ka dawo sai ku fita tare."

Duk da ya samu labarin dalilin da yanzun mahaifiyar shi ke gida, amma kuma ba ya jin akwai wani abu da za ta iya yi wa Bilal tunda ya na gari, ajiyar zuciya ya sauke ya kalli Bilal yace "Yarima, ka zauna tare da auntyn ka kaji, zan fita amma ba zan jima ba zan dawo, idan kuma ka gaji da zaman gidan ka na iya fita k'ofar gida wajen Rabe sai kuyi hira."

Saida Bilal ya kalli Haseenah kafin ya kalli Usman yace "To Abba, amma fa kar ka jima sosai."

Dafa kan shi ya yi yace "Ba zan jima ba insha Allahu."

Saida ya sumbace shi kafin ya kalli Haseenah yace "Ba wani abin da ki ke buk'ata?"

Sosa kai ta yi irin na kunyar nan ta kasa magana, hannu kawai ya sa aljihu ya fito da kud'i ya bata, karb'a ta yi ta mi shi godiya kafin tabi bayan shi har ya shiga mota, Rabe da ke zaune da littafin karatu (dan tunda aka ce za'a maidashi makaranta abun ya sake shiga ran shi) ya taso suka gaisa kafin ya bud'e mi shi k'ofa ya fice ya na binshi da addu'a, rufewa ya yi har ya zauna Haseenah ta k'wala mi shi kira ya zo, tsaye ya ke kamar yanda take su na kallon juna tace "Wannan pliwoyin ka basu ruwa mana, ya ka ke abu kamar ba ka san aikin ba ne."

Wani kallon raini ya mata dan babu abin da bai wani ba game da ita kafin yace "Tofa, to na ji zan ba su ruwan, shikenan?" Ya na fad'a ya juya ya bar mata wajen, ciki ta koma ba ta damu da shi ba dan a cewar ta k'aramin arne ne shi ba ta shi take ba, yau dai ba wata matsala tsakanin ta da Bilal, ya na zaune gefe ta na zaune ita ma sai dai su kalli juna, dan dama ba tace ya bar shi bane saboda ta na da wani nufi akan hakan, kawai ta fahimci ta b'ata mi shi rai ne jiya saboda abin da ta fad'a, ana hakane ta shiga madafa d'ora girkin rana, ba jimawa da fara aikin Bilal ya shigo da sallama, amsawa ta yi tace "Ya dai?"

Cikin ladabi yace "Aunty dama zanje gidan aboki na *Abdallah* yanzu zan dawo."

"To shikenan sai ka dawo, amma kar ka jima kuma uban ka ya dawo ya min tijara." Ta fad'a ta na ci gaba da aikin ta, da sauri ya fita ko amsa ta biyi ba, ashe Bilal moton shi ya d'auka ya fita da shi Haseenah ba ta ma sani ba, Rabe kuma tunda bai san ba'a barin shi fita da shi ba shima bai hana shi ba sai ma bin moton da kallo da ya yi har ya daina ganin Bilal kafin yace "Kai, Allah ka bamu kud'i mu ma muji dad'in rayuwa."
Chapter 74 · 0% Book details